Thursday, 25 January 2018

Kashe Fitila 8

*KASHE FITILA*💡8

*Batul Mamman*💖

A kwanakin da suka biyo baya Gimbi ladabi take yiwa Awaisu sosai. Tsakanisu tamkar wani abu bai faru ba. Tarewarsu a sabon gidan da ake jiran sai bayan babbar sallah idan sun dawo daga hajji kuwa tuni ta rushe. Kusan duk abin da suke bukata daga tsohon gidan sun gama kwashewa.

Gimbi ta gyara dakin da Maamu zata zauna tamkar wata amarya. Dayake komai sabo ne idan ka shiga kamar kada ka fita. Dakin Daula da taci burin gyaransa ma saboda tilon 'yarta sai da ta matsawa Awaisu aka karo wani gadon a matsayin na Rumana. Karshe ta yiwa Maamu da Rumana dinki kala biyar biyar ta kawowa Awaisu.

Shayi yake sha yana duba wasu takardu ta kawo ledoji manya biyu ta ajiye tare da durkusawa a gabansa.

"My dear ga tawa 'yar gudunmawar"

Daya daga cikin ledojin ya bude. Kaya ya gani a dinke duka super holland har biyar. Ya kalleta da alamar tambaya. Rausayar da kai tayi tana kifta idanu alamun zata yi kuka.

"Nasan babu wani abu da zanyi ya wanke wautar da nayi maka kwanakin baya. Amma don Allah ina mai sake neman afuwarka. Na tsorata ne da jin labaran zama da surukai har naso bata aurena akan labaran wasu da nake ji"

Tayar da ita yayi sannan ya matsa yadda zata iya zama kusa dashi. Ya kama hannunta ya rike.

"Bazanyi miki alkawarin cewa kullum cikin zaman lafiya zamu kasance ba idan Maamu tazo. Amma ina so ki sani ba wai don ita ta haifeni ba, Maamuna bata da rigima ko kadan. Mace ce wadda yanayin kaddarar rayuwa ta sanya mata mugun hakuri da kawaici. Ina jin ba domin Baaba ba da a sangarce ma zan tashi saboda tsabar hakuri irin nata. Tabbas banji dadin abin da kika yi ba amma na hakura. Da kinsan yadda nake mafarkin zama inuwa daya da ita nasan baza kiyi waccan maganar ba tun farko"

Sake bashi hakuri tayi tana kuka da alkawarin gyara kuskurenta ta hanyar bin Maamu sau da kafa.
*****

"Anti Bebi lokacin tafiyarmu sai kara matsowa yake fa. Ni wallahi bana son yin tafiyar da mutanen nan. Dukkaninsu babu wata alamar wayewa. Muje airport su janyo a rinka kallona"

Dariya sosai Anti Bebi tayi sannan ta soma magana da shakakkiyar muryarta wadda tsabar gayu da make murya wurin janyo hankalin maza ta koma haka

"Ki samu ya barki muje wurin da nake fada miki. Kuma kiyi a hankali kada uwarki taji labari. Kinsan dai ba shiri muke da ita ba"

Gimbi ta tsuke baki jin an zagar mata uwa. Ita kanta bata fiye shiga sabgar Antin tasu ba sai da wannan abin ya faru. Yadda Anti Bebi da Mama basa kama a fuska haka suka bambanta a hali. Yanzu haka aurenta na shida kenan. Abin mamaki masu kudi take aure suyi ta mata bauta. Sai ta tara abin da ta tara ta nemi sanadin da zasu saketa. Mama ta gaji da fada da nasihar ta tsame hannunta daga lamuran kanwar ta ta.

"Shi kuma mijin naki ki barni da shege, idan Wangesi na tsangaya ya fara aiki akansa ina fada miki sai juya alkalami yafi miki wahala akan yadda zaki rinka juya shi son ranki. Shi din banza..."

Mikewa Gimbi tayi tana rataya jaka rai a bace. Anti Bebi tace
"Me aka yi kuma zaki tafi muna magana"

"Haba Anti, zamana a nan kin zagar min uwa kin koma kan mijina. Ina sonsu bazan jure zaginsu da kike yi ba"

Dukan cinya tayi irin na matan da suka ga jiya suka ga yau.

"Karyar banza, Amina dai zan yarda kina sonta tunda ita ta haifeki. Amma indai Awaisu ne karya kike yi Gimbi. Duk matar da take son mutum take kin iyayensa ko 'ya'yansa na wani auren kallon munafuka nake yi mata. So da ya amsa sunansa shine ki rungumi duk abin da mijinki ya nuna yana so ki taya shi ririta shi"

Ganin Antin tana ya6a mata magana ta fice ko sallama babu. Dama can ba wai tana ganin mutumcinta bane. Tun suna yara sun san tayi kaurin suna a dangi saboda fitinarta. Yanzu ma dole ce ta kawota. Zata nemarwa kanta mafita.
*****

Bayan kwana biyu Awaisu yake sanar da ita cewa nan da sati uku su Maamu zasu taho Abuja domin ta nan zasu tashi. Kuma an kusa fara dibar alhazai. Sanan za'a taho da Rumana tun yanzu domin taya Laminde zama da su Haris da kuma sabawa ita ma da gidan. Da murnarta ta dauko takarda tana yi masa list na abubuwan da take so a karo musu na kayan abinci da kayan masarufi domin tarbar baki. Yadda take yi masa dole duk wani sauran zargi da bacin rai da yake ransa ya kawar dashi.

Bayan ya fita a gigice ta kira Anti Bebi har ta manta abin da ya faru tsakaninsu. Ita kuwa tana ganin kiran taki dauka. Sai da ta kira yafi sau biyar sannan ta amsa tana magana da kyar wai ita a dole anyi mata ba daidai ba.

Gimbi bata yi fushi ba ta fada mata yadda suka yi da Awaisu. Anti Bebi tace idan zata iya ta je ta sameta a gida washegari su tafi wani kauye a Nasarawa state inda Wangesi na tsangaya yake.

Da daddare kuwa ta karantawa Awaisu karya da gaskiya saboda kada ya ga bata dawo gida da wuri ba daga bankin da take aiki. Shi kuwa sanin yanayin aikinsu bai kawo komai a ransa ba sai addua da yayi mata.

Washegari tana zuwa wurin aiki tayi karyar ciwon ciki ta samu manaja ya yarje mata komawa gida. Daga nan bata zame ko ina ba sai gidan Anti Bebi. Ko zama batayi ba suka kama hanya. Dreban Anti Bebin ne ya kaisu. Tayi mamaki sosai yadda taji suna hirar malamin tsibbun tare dashi. Ashe shine ya hadasu ma.
*****

Wangesi ya bata layu da guraye da zata saka a cikin gidan wanda su Maamu suna zuwa zata ji ta tsani gidan saboda zafin da zaiyi mata. Saboda yarda da shirkarsa da yayi har alkawarin dawo mata da kudinta yayi idan Maamu ta iya kwana uku a gidan batare da ta matsa a mayar da ita Fika ba.

Gimbi murna ba'a cewa komai. Tana zuwa gida tayi duk yadda yace ayi da kayan da ya bata ta zauna jiran lokaci.

Ranar da zasu zo ta kama asabar. Tun kafin asuba ta farka ta shiga kitchen tana ta dafa kayan tarbar baki. Laminde ma a nan ta sameta. Awaisu kuwa zuciyarsa fes ganin ta sake tana nuna masa ta fishi murnar zuwansu.

Dama dreba ya tura aka dauko su. Motar na shigowa yaran suka fita a guje suna murnar ganinsu. Haris tamkar ya shige cikin Harisu don murna. Ba karamin son kawun nasa yake yi ba. Maamu ce karshen fitowa daga motar. Kafar dama ta fara saukewa cikin sanyin muryarta tace "Bismillah tawakkaltu alallah"

Wednesday, 24 January 2018

Kashe Fitila 7

*KASHE FITILA*💡7

*Batul Mamman*💖

Gani tayi kukan bazai kaita ko ina ba ta yanke shawarar washegari zata kira Mama ta fada mata. Dole ma a dauki mataki don ba bauta tazo yiwa kowa ba.

Shirin bacci tayi sannan ta koma dakin nasa. Kwance ta same shi akan abin sallah da gani sallah ya idar bacci ya dauke shi. Tausayinsa kuma taji, ya mayar da kansa tamkar agogo. Bashi da hutu kwatakwata duk domin ya farantawa su Maamu. Tsaki taja a fili tana tunanin yadda zata bullowa lamarin da ya tunkaro ta.

"Saboda zan kawo mahaifiyata gidana shine kike tsaki haka Gimbi?"

Muguwar faduwar gaba taji. Shi kuwa ya mike tsaye yana kallonta rai a bace. Bakinta yana dan rawa tace "haba my dear, kada kayi min mummunar fahimta mana. Dazu da kanka ka gani ina murna harda kukan..."

"Kukan bakinciki ba. Da farko har ga Allah nayi zaton dadi kika ji ganin yadda na damu da yanayin da mahaifiyata take ciki. Bata da wurin da zata kira gidanta. Sai da nayi wanka na biyo bayanki naji kina kuka sosai a dakinki."

Rasa bakin magana tayi shi kuwa ya cigaba da magana cikin kunar rai
"Duk duniya bayan Maamu babu wanda ya cancanci kyautatawa daga gareni kamar Yaya Harisu. Ban taba boye miki asalina ba. Amma abin mamaki kina nuna bacin ranki akan kyautatawar da zanyiwa wanda suka zama jigon rayuwata. Idan bazaki iya zama dasu ba sai na auri wadda zata iya"

Tun da ya fara magana  bata tanka shi ba sai yanzu da ya ambaci kishiya.

"Kayi kadan kace zaka auro wata ka ajiye a gidan nan. Ko ka manta cewa nawa ne. Suna na ne a jikin takardun gidan"

"Dadin abin nima ina da nawa. "

Ta turo baki cike da tsiwa. Tsiwar da a da take bashi sha'awa idan tayi
"Haka nan zaka kare rayuwarka kana yiwa wani kato bauta. Sai shegen aure da tara iyali. Kai kuma an barka da siyan shinkafa da ragon suna"

Shiru yayi har sai da ta gama maganarta tukunna sannan ya tako gabanta fuskarsa babu annuri ko kadan. Ja ta rinka yi da baya yana binta

"Yaya Harisun ne kato Gimbi?" Ya fada a hankali amma kana jin muryarsa har wani rawa take yi saboda bacin rai.

Duk da a tsorace take amma ta kule da yadda yake zare mata ido akan 'yan uwansa.

"Karya nayi ba katon bane? Ko baiyi biyunka ba"

Bata karasa magana ba taji ya gwabje mata baki. Nan take jini ya soma zuba saboda fashewar lebenta na kasa.

Cikin kuka tace "Awaisu ni ka fasawa baki?"

"Idan baki fita daga dakin nan ba sai nayi miki abin da yafi wannan."

Murya ta soma dagawa tana kuka "babu inda zani, gidana ne ba naka na. Idan kaji haushi ka fita ka koma naka"

Fitar yayi zuciyarsa tana tafasa. Wai akan iyayensa da bashi da tamkarsu shine Gimbi take yi masa abin da bai taba tunanin zata aikata ba. Lallai ba'a shaidar mutum. Yasan halinta na kyankyami da ji da kai. Shiyasa yake mamakin irin son da take masa farkon haduwarsu. Falo yaje ya samu yaransa uku sunyi bacci sai Haris da yake karasa homework. Tashinsu yayi daga su sai kayan baccin jikinsu suka fice. Motarsa ya bude suka shiga suna tambayarsa inda zasu je. Bai basu amsa ba ya rinka dannawa mai gadi horn. Yana budewa ya fita a guje.

Karar horn din ce ta fito da Gimbi. Tsoronta kada da gaske ya fita daga gidan. Sai dai abin mamaki ba shi babu yaran.

Nan fa hankalinta ya kara tashi. Mai aikinsu Laminde ta shure da kafa tana bacci itama a falon ta tambayeta ina su Daula

"Hajiya gasu nan suna hamok. Jiransu nake yi su karasa aje a kwanta."

Ta galla mata harara "ina kika gansu. Aikin banza babu abin da kika iya sai bacci"

Waje ta fita inda mai gadi ya tabbatar mata da yaran Alhajin ya fita. Haka ta rinka kiran wayarsa yaki dauka. Karshe ma kashewa yayi yana kallon yaransa suna bacci a makeken gadon dakinsa. Gidansa na Apo ya tafi dasu.
******

Da sassafe yaji ana buga gate ya leka ta taga. Maigadinsa ya gani yana ta washe baki ya budewa Gimbi gate ta shigo. Ko rufe kofar motarta batayi ba ta fito ta shiga gidan cikin sauri.

A falo ya sameta yace kada ta tasar masa yara.

"Wane irin wulakanci ne zaka daukar min yara cikin dare"

"A iya sanina lokacin da muka tare a gidan nan ke kadai kika shigo sai akwatunan kayanki. To mene ne na bacin rai don na kwashe yaran da jinin Maamu yake yawo a jikinsu"

"Wai duk saboda maganar jiya da bata taka kara ta karya ba kake min wannan cin kashin harda fasa min baki"

Ya tabe baki "ina jin baki san girman uwa bane"

Neman sulhu take yi domin tun aurensu basu taba samun sabani irin haka ba. Kwantar da murya tayi ta soma magana
"Duk laifinka ne, ta yaya zaka shirya kawo Maamu batare da neman izinina ba? Nima fa ina da hakki akan ka. Kuma abu irin wannan sai ka fara shawara dani kaji nawa view din"

"Neman izininki? Wai dama haka kike ne ko kuwa sabon salo ne kika fito dashi kawai don baki son dangina. Ba fa tun yau na san kina nuna musu kyama ba. Sharewa kawai nake yi saboda babu wanda ya taba korafi cikinsu."

"Kaga ni ba rigima nazo muyi ba. Maganar fahimta nazo da ita. Idan kana so ka ginawa Maamu sabon gida a Fika is up to you. Amma batun mu zauna tare is out of the question. Zama da suruka baya taba haifar da alkhairi"

Duk yadda yake son ta a daidai wannan lokacin yayi nadamar aurenta. Rasa bakin magana yayi yace mata kawai ta fita idan ta gama. Ganin wankin hula zai kaita dare ta ja motarta ta tafi gidansu. Tana kuka ta zayyanawa Mama abin da ya hadasu. Mama ta dubeta sosai ta girgiza kai.

"Idan kika kure Awaisu ya sakoki zaki gane kudi da gata aikin banza ne idan aka rabaka da iyalinka. Ke da ya kamata ki nuna masa kinfi kowa farinciki shine zaki bata masa rai akan mahaifiyarsa. To yayi miki adalci ma da bai hadoki da takarda ba. Shashashar kawai. Idan ma zugaki akeyi ki sani aljannarki tana karkashin kafar mijinki. Shi kuma tasa tana tare da mahaifiyarsa. Kada ki zama mace mai kashewa mijinta fitilar rayuwarsa Gimbi. Uwa haske ce, uwa rahamace. Da kika shiga matsala ai gaki a gabana."

"Mama yanzu goyon bayansa kike yi"

"Ki kiyayeni Gimbi. Kuma ki wuce yadda kika bata mishi rai ki bashi hakuri ku sasanta. Idan Alhaji yaji maganar nan ki kuka da kanki. Kinsan halinsa sarai. Bar ganin yana sonki hakan bazai hana ya saba miki ba"

Dukar da kai tayi ta gama jin fadan Mama ta tashi ta koma sabon gidan.

Amir ne ya fada mata baban nasu yana daki ta shiga da sallama. Kafin ya amsa ta durkusa gwiwoyi a kasa a gabansa tana kuka. Kamar ya basar sai dai Gimbi matsayinta daban a zuciyarsa.

Tasowa yayi yazo gabanta. Cikin kuka da nuna nadama ta rinka bashi hakuri da nuna masa ta gane kuskurenta. Kukan da tayi tana ajiyar zuciya yasa dolensa ya hakura tare da yi mata nasiha. Cikin dan kankanin lokaci ta shawo kansa suka daidaita.
*****

Zaune suke cikin daki su biyu ta dubi kanwar Mama wadda take binta bayan ta bata labari.

"Anti Bebi wannan ita ce matsalar da ta tunkaro ni. Kuma Mama ta bashi goyon baya"

"Ki bar komai a hannuna 'yata. Indai ina raye babu wanda ya isa ya takura miki. Tun da dadewa nace kizo muje a mallaka miki shi a tafin hannuki kika ki yarda ke dadi miji. Yau ga irin abin da nake ta hango miki ya faru. Ke ko babu boka babu malam yayi kadan kinji ko.  Shi din me? Mijina na uku ma duk taurin kansa sai da ya koma albashinsa ma a hannuna yake balle wani Awaisu."

Kalmar karshe ta sosawa Gimbi rai sai dai biyan bukata yafi dogon buri

Tuesday, 23 January 2018

Kashe Fitila 6

*KASHE FITILA*💡6

*Batul Mamman*💖

Tun daga wannan rana Awaisu yake wasan buya da Harisu. Duk inda yasan zasu hadu su kebe guduwa yake yi. Ranar da zai koma Abuja ma kamar ana korarsa don sauri. Haka ya tafi tasha kafin Harisu ya dawo daga shagonsa inda ya ajiye masa kayan amfani kamar su madara da ganyen shayi da yake son bashi guzurin tafiya.

Baiyi sati da komawa ba Alh Mudi ya dawo daga Kano. Wata rana da yamma ya tura karamin dansa ya kirawo Awaisu. Da ya zo ne ya tabbatar masa da Gimbi ta sanar dasu abin da ke tsakaninsu. Karshe yace yana so ya sanar da yayansa cewa su same shi a Kano shi da Saminu idan har da gaske yana sonta da aure suyi magana.

"Ban yarda da bata lokaci ana soyayya ba indai akwai halin yin auren gara ayi kowa ya huta."

Gaban Awaisu ya fadi jin Alh Mudi ya ambaci ganin yayansa da Saminu. To da wane idon zai kallesu ma. Shi dai Alh Mudi bai san me yake faruwa ba. Albarkacin Saminu yake ganin lallai Awaisu ma mutumin kirki ne kamar yadda ya kula a dan zaman da yayi dasu.

Bai sami damar komawa gida ba sai bayan sati biyar ana hutun Good Friday da Easter Monday. Haka ya tafi jiki babu kwari saboda rashin sanin yadda zai tunkari dan uwansa da maganar auren Gimbi. Gashi Alh Mudi yace su same shi a gidansa na Kano. A son ransa ayi bikin bayan sallah karama tare da na babban dansa wanda suke a Kanon tare da babarsu uwargidan Alhaji.
*****

Kwanansa biyu da dawowa ya rasa abin da ke masa dadi kuma ya kasa fadawa kowa. Maamu tayi fadan da magiya duka yaki cewa komai. Gashi yana matukar son Gimbi baya fatan rasata.

Da daddare yana kwance a dakinsa Harisu ya shigo. Ya tashi zaune amma ya kasa cewa komai.

Harisu yayi murmushi yana kallonsa. Sai da ya zauna a gefen katifar dakin ya soma magana.

"Yanzu ni kake gudu saboda ka soma aiki a Abuja kayi kudi ko. Kana ganin kafi karfinmu."

Awaisu ya zaro ido a razane "Yaya me ya kawo wannan zancen kuma? Wallahi ba haka bane. Allah Ya kiyaye. Bana fatan abin da zai kawo min tunani makamancin haka"

Harisu ya daure fuska "haka kawai za ka fara guduna ne idan ba kana tsoron a ganka tare da talaka irina ba."

Idanun Awaisu tuni suka yi ja saboda rashin jindadin kalaman yayansa. Shi da ya dauki Harisu uba yaushe ma irin wannan tunanin zai zo masa.
"Wata matsalar ce daban Yaya"
Ya fada a raunane.

Harisu yayi dariya a zuci domin ya samu Awaisu ya fada tarkon da yayi masa na son jin damuwarsa.

"Ina jinka, menene matsalar da take hanaka walwala a gidan nan?"

Babu amfani cigaba da boyewar shiyasa ya fada masa maganar da yaji sunyi da Saminu da kuma wadda suka yi da Alh Mudi.

Wani dogon numfashi Harisu ya ja. Ya jima yana tunani kafin ya soma magana cikin nutsuwa.

"Kai ba yaro bane da zan ce baka san abin da kake yi ba. Sannan ka wuce ayi maka auren dole. Duk yadda nake son ka auri Mardiya ba ni zan zauna maka da ita ba. Saboda haka nagode da ka fada min da wuri kafin ayi auren muji kunya. Zanyi kokarin fahimtar da Saminu. Kuskurena ne da ban fara maganar da kai ba na fada masa"

Ko bai fada ba yasan ransa a bace yake kawai ya danne ne "Kayi hakuri Yaya. Itama Gimbi tana da kyawawan halaye idan ka ganta ....."

Bai karasa ba Harisu ya mike batare da yace komai ba yayi hanyar fita. Tunaninsa bai wuce yadda zai fita kunyar Saminu ba. Tsayawa yayi ba tare da ya juyo ba yace
"ka shirya muje Kanon gobe kafin lokacin komawarka aiki."
*****

"Zancen banza kai, ina Awaisu ina 'yar masu kudi. Ko kuwa so yake ya janyo ace yayi auren jari? To ma a ina yake tunanin ajiyeta idan anyi auren.  Yaushe ma ya fara aikin da zai jajibo aure irin wannan"

Maamu ce take ta fada bayan Harisu ya sanar da ita da Baaba batun tafiyarsu Kano neman aure. Haka tayi ta fada yana bata hakuri da nuna mata magana kawai zasu je yi ba auren za'a daura ba.

Ranar da suka isa Kano Saminu jiki a sanyaye ya tarbesu. Wannan ya dagawa Harisu hankali ko har Alh Mudi ya sanar dashi komai. Baya son abin da zai taba alakarsu ko kadan. Shi Awaisu dama ya kasa kallonsa ma. Tunda suka zo yake sunkuyar da kai.

Bayan sun dan huta ne suka zauna tattaunawa. A nan Saminu ya dubi Harisu "Alh Mudi yazo gidan nan da kansa akan yana son na bawa dansa auren Mardiya. Sanin cewa munyi magana da kai nace na bayar da ita ga Awaisu. Shine yayi min wani bayanin daban da ban gama fahimta ba "

A kunyace Harisu ya fada masa abin da ke faruwa.
"Kayi hakuri abokina, bani da masaniya akan hakan. Da tun farko bazan bijiro da maganar hadasu ba"

Awaisu duk sai yaji babu dadi. Yanzu da Alh Mudi baizo nemawa dansa ba shikenan ya bata zumuncin abokan.

Muryar Saminu ce ta katse masa tunani "Babu komai, ai kaga yadda Allah Yake nuna ikonSa. Sai muje gidan ka fada masa ka bada auren Mardiya ga Fawaz a matsayin waliyinta tunda bani da dan uwa namiji. Shi kuma Awaisu sai na nema masa auren Gimbi"

Sai a lokacin Harisu yayi murmushi hankalinsa ya kwanta ganin Saminu bai dauki abin da zafi ba.

Washegari kuwa suka dunguma sai gidan Alh Mudi aka daidaita magana. Sallah karama da sati biyu aka sha bikin Awaisu da Gimbi. Ganin cewa bai samu muhallin kirki ba Alh Mudi ya bashi gida da sunan Gimbi a Abuja inda zasu fara zama kafin ya sami nasa. Ita kuma Mardiya suka tare a Kaduna ina Fawaz yake aiki.
*****

*Bayan shekara 12*

Cikin shekarun da suka gabata Awaisu ya sami budi sosai. Domin har gida ya gina kato a Abuja yana shirin tarewa. Inda Allah Ya kara taimakonsa shine kasuwanci da yake yi. Duk da yana aiki ga rashin lokaci haka ya sami yara biyu 'ya'yan kawunan sa da ya budewa shago suke sayarda atamfa da shadda. Abu kamar wasa sai da ya hada shaguna hudu a jere a Wuse market. Ga kwazonsa a wurin aiki yasa ya sami mukamin manaja a bankin.

Gidan Harisu kuwa yasha gyara sosai har mota ya saya masa sannan ya kara masa jari. Zamansu gwanin sha'awa. Tsakaninsu da Gimbi babu wata matsala. Dayake itama aikin bankin take yi bata da lokaci na zuwa Fika sosai. Yaransu hudu babban ciki Haris, sai Daula mai sunan babar Gimbi, Amir mai sunan Alh Mudi da kuma auta Sa'ad suna kiransa Mu'allim.
*****

A gajiye Awaisu ya shigo bayan isha yaran suna ta murnar dawowarsa daga Fika. Sai da ya gama dasu ya wuce dakinsa. Sauri yake yi idanunsa su gane masa matar da yake jin bazai taba iya hadata da kowa ba saboda irin son da yake yi mata ga kuma albishir a bakinsa.

Taci kwalliya tayi kyau sosai tazo ta tarbe shi tana murmushi
"Ashe ka shigo maimakon ka kira kafin ku karaso na hada maka ruwan wanka"

Ya shafi gefen fuskarta yana murmushi "kada ki damu, zo ki zauna kiji albishir din da nazo miki dashi har biyu. Dayan ina hanya akayi min waya aka fada min"

Kaskon turaren wutan da yake gefen gado ta dauke sannan ta dawo ta zauna kusa dashi yana rungume da ita yayi ajiyar zuciya.

"Gimbina Allah Ya yarda. Visa dinku ta fito"

Ta dago kai da sauri cikin farinciki "wace visa kuma?"

"Dama na boye miki ne sai komai ya tabbata. Na biya muku Hajji ke da Yaya Harisu, Baaba da Maamu. Sai Yaya Zakiyya tunda su Anti Baraka da Ummu mazansu sun kaisu. Kinga za ta tayaki kula dasu Baaba. Albishir na biyu kuma kuna dawowa nake so mu tare a Apo. To babban abin jindadin shine dasu Maamu zamu tare"

Shiru yaji Gimbi taki dagowa bare tayi magana. Ko da ya dago kanta hawaye  take yi sosai. Wani sonta ne yake shigarsa domin yasan kukan farinciki take yi. Rungumeta yayi yana shafa bayanta.

"Dama nasan zakiyi murna sosai Gimbina. Shiyasa ban fada miki batun tafiya Hajjin ba sai da na gama. Tunda kinga ni naje har sauu biyu kuma last year munyi umara tare dake. Shiyasa bazan bi ku ba. " ya cigaba da cewa
"Kuma fa yadda naso har da Baaba zamu tare. Sai dai lalurar idonta yasa Yaya yaki yarda. Shine na hakura ba don naso ba. Burina ya cika zan dawo da Maamu kusa in kula da ita. Itama taji dadin arzikin da Allah Ya bani. Ta dade tana jin nauyin su Baaba da Yaya Harisu. Duk da naso hadawa da Baaba hakan bai samu ba. Amma zan dauko Rumana. Gimbina da ina da yadda zanyi fa wallahi Yaya Harisu ya dena fita neman kudi. Komai ni zanyi masa"

Can kasan makoshi tace "uhmm hakane." Domin ji take yi ya cikata da surutu mara kan gado.

Mikewa yayi ya shiga bandaki domin yayi wanka ko zaiji saukin gajiya.

Yana shiga Gimbi ta fice ta tafi dakinta ta rufe kofar da mukulli. Gadonta ta hau ta saki kuka cikin tashin hankali. Ko da wasa bata taba kaunar zama da uwarmiji ko dangin miji ba. Can daga nesa dai yayi musu kyauta suna kauye ba sai sun rabesu ba.

"Tabdi, akwai matsala. Matar da ko Hausar kirki bata iya ba sai anyi magana tayi ta yankare hakora tana murmushi. Shine don kana jin ka fara kudi zaka dauko min su ka kawosu ko neman izini na bakayi ba. Da sake Awaisu....bana cikin matan da za'a hada da uwarmiji ace mu zauna lafiya gida daya"

Dankwalinta tayi jifa dashi ta rasa me yake mata dadi. Ita fa shi kadai take so ba danginsa ba. Duk halaccin da tayi masa ta aureshi talaka ko gidan zama bashi dashi. Shine yanzu arzikin nasa kuma sai sun raba tare da wadda bata nan lokacin da suke nema. Ta hana kanta sukuni tana fita aiki duk domin ta taimaka masa. Ba don kada ace tayi sharri ba ma sai tace gabadaya gidan Harisu wari yake yi mata idan taje Fika. Shiyasa bata son zama idan taje.

Monday, 22 January 2018

Gidan Mati 11

*GIDAN MATI*

©BINGYEL FULANI & RUFAIDA OMAR

BABI NA GOMA SHA DAYA

Abule ta yi k'asa-k'asa da murya.
"Makarin shine a jik'a wandon kwarto a shanye."
  Nene ta zabura tayi zaman 'yan bori wanda ya yi daidai da sullu6owar tusa ta mai k'ara. Abule ta toshe hancinta, a hankali Nene ta numfasa har da lumshe idanu don ba k'aramin sassauci ta samu a cikinta ba.
  "Na shiga uku, yanzu ina zan ga kwar... Af! Fad'uwa ta zo daidai da zama ai Abule, yo bana manta ashe muna da su a kurkusa ba? Ga Basharin Shafa?"
  Abule wacce itama shaf ta mance da batun Jik'an Lamid'on ta sauke ajiyar zuciya tana mai jin zuciyarta wasai, babban abinda ya sanyamata damuwa da lamarin ba komai bane sai na tsoron kada ya kasance Nene bata warke ba ta tonamata asiri mutan gari su zageta. Ta daki cinyarta tana mai washe rinannun hak'oranta.
  "Kai Allah mungode maka, ai ni dinma kaf tunanina bai je nan ba. Ko jiya da daddare ya haurawa Kulu Gurguwa."
  Suka saki shewa don Nene har ta hango warakarta a sauk'ak'e.
  "Kai Allah Ya k'arowa Bashari ilimin kwartanci, wannan ai gaba ta kaini. Ashe kwarto da ranarsa. (Kun ji jahilci!)"
  Dariya suka k'ara kwashewa da ita.

  A yammacin ranar Shafa na durkushe a gaban murhu tana kokarin iza wuta ta tsinkayi sallamar Nene da Abule.  Da mamaki ta dubesu kafin ta mike. Abule ta ci burki anan tana k'arewa gidan Shafar kallo domin rabonsu da shiga gidan har sun mance. Daga can gefen garu ta hangi jerin manyan duwatsu wanda ta taimakonsa ne Shafa ke k'arewa cikin gidansu kallo. Ta6e baki ta yi gami da bin sahun Nene da har ta shige rumfar Shafar ba tare da ko neman izni ba.
  Shafa za ta yi magana Abule ta hanata ta hanyar rik'o hannunta tanamata alamar ta yi shiru gami da yi mata nuni da gidansu, nan take ta fahimci ba su kaunar Fad'ime da Inna su san da zuwansu. Ta gyara zaman d'aure kirjinta suka shige ciki.
   Nene ta washe baki.
  "Shafa Shafa, Shafar Bashari, uwargida ran gida! Kin tare gaba kin tare baya, turmin tsakar gida sha lugude!"
  "Wannan haka yake." Fad'in Abule tana gyada kai kamar k'adangaruwa.
  Shafa ta yamutsa fuska tana kallonsu d'ai-d'ai.
  "Halan dai Nene acan asibitin har allurar mahaukata suka manta suka yi maki?"
  Nene ta hau daure fuska za ta kwa6omata mai zafi ganin haka yasa Abule saurin tarewa.
  "Kai Shafa, dad'ina da ke zolaya. Nene ai taki ce, banda abinki ai makwafci ance ya fi dan uwa, a baya ma rashin fahimta ne."
  Dariya Shafa tayi gami da tafa hannuwa. Nene da Abule suka dubi juna, dakyar dai suka shawo kanta ta yarda zata sauraresu.
  Nene ce ta soma magana bayan ta gyara zaman nafkin dinta.
  "Ki taimakeni Shafa ki bani aron wandon Bashari."
  Shafa ta fiddo idanu gami da dafe k'irji.
"Yau naga ta kaina! Nene me zakiyi da wandon Basharina? Anya Nene ba ki samu matsalar kwakwalwa ba? Au to na fahimta, wato dai duk matattarar kwararar gudawar da aka sanyamaki bai isheki ba sai kin had'a da wandon Basharina? To mine amfanin na Mati?"
Nene ta share zufa tana girgiza kai. Abule ta cafke zancan.
  "Kinga Shafa duk ba haka bane, wannan maganar da za mu yi sirri ce, don Allah ki rufamana asiri."
  Shafa ta dan zubamasu idanu na 'yan dak'ik'u kafin ta gyada kai don ba za ta bari gulmarnan ta wuce ta ba.
  "Ina jin ku."
  Abule ta zayyanemata duk abinda ya faru da kuma makarin asirin.
  Shafa ta saki shewa har da tafa hannuwa.
  "Yau abin namu ne! Oh ni matar na Lamid'o!"
  Saida ta basu wuya Nene harda matsar kwalla sannan ta amince da sharad'in Nenen za ta kyautarmata da tunkiyarta da take kiwo. Ba musu Nene ta aminta daganan ta mik'e ta fita zuwa d'akin kwanansu ta hau lalube.
  Jimawa kad'an sai ga ta rik'e da wani tsohon wandon Bashari da ya gada gun Lamid'o ta mik'amata.
  "Gashinan, kuma kada ya kai gobe a wajenki, ko ta katanga ki jehomin."
Nene ta hau godiya kafin kuma cikin lallami ta ce.
  "Ki taimakamin Shafa, ki bani sabon d'inki mana."
  "Cab! Ai idan kinga Bashari ya yi sabon dinki to mutuwa akayi a danginsa don haka ban bayarwa, idan ba kwa so ku k'ara gaba."
Ta k'ara he tana girgiza k'afa gami da jefamusu tafin hannunta.
  "A'a me ya yi zafi? Mu je Abule hakan ma ya wadatar" " To karki manta dai ki jefon ta katanga." Da komawarsu kuwa Abule ta tarkata lallen ta watsar Masai, shi zaman duniya dama rabo ne, idan ba ka da shi kuwa za ka zo ne a banza ka koma a wofi. Tuna hakan ya sa ta nutsuwa ta ma fita daga batun Fadi. To haka ma ga Nene sai wayar gari akai aka ganta sumul tamkar mai bugun Iska. Itama ta mai da rayuwarta shiru ta hanyar aro nutsuwar dole. Daga bisa ni ta kulla Amintaka da Shafa ba ma ta zaman gidan balle ta zubda hali.  Bayan watanni, ranar wata laraba wanda ya yi daidai da kwanan Inna guda a birni ta je hado kayan haihuwar fadi. Faɗimen ta tashi da nakuda. Gidan daga Abule sai Nene dake shirin fita.
  Ta gyara zaman yafenta tana mai sauke kabar shiga d'akinta. Ta juyo gami da duban Abule, za ta yi magana kenan suka ji nishi da salatin Fad'ime. Cikin hanzari suka dubi juna.
  "kinji abinda na ji?" Abule ta ya tsina fuska" na ji mana kila abinne ya zo."  "To ya za ai ko mu dubu yar magaji... " Abule ta ƴi saurin rufe mata baki. "Ke gafara, kinmanta yanda ta musanya miki magani? To yaune ranar ramuwa dan haka maza kwaɓe gyalen nan ki dauka surfe mu yi yanzu dan karma makota su jiyo bayan awa guda ma lekata."  Da sauri Nene ta aje gyalen ta juye hatsinta a turmi suka hau dukansa ba ka jin karan komi sai tunkwal-tunkwal.
  Fadime cikin azaba haka ta rarrafo bakin kofarta tana kiransu amman suka yi biriss da ita. Har sai da suka bar jin muryarta tukun suka zubda taɓaren suna ma su nufarta. Ganin ruwa gefenta ya sa Nene zare ido "Ke abu ai  fayar ta fashe."
Abule ta karasa itama tana lek'e-lek'e, a karshe suka kinkimi Fad'ime suka maidata ciki. Haka suka kar6i haihuwar santalelan d'anta suka yanke cibi. Nene dake rike da jaririn wanda bai bar komai na Mati ba, katon kan Fad'ime ya yo. Ta yiwa Abule ido kafin ta fice zuwa d'akinta rike da jaririn wanda ta cusawa yatsanta a bakinsa gudun kada sautin kukansa ya ankarar da gulmammun makwaftansu.
  Abule ta dubi Fad'ime wacce ba k'aramin k'aruwa ta samu ba wajen haihuwa sai murk'ususu ta ke da alamar dai akwai abinda ke damunta. A hankali ta sulale ta bi bayan Nene. Idanu ta ware a tsorace ganin Nene na kokarin sanya jaririn cikin kwali.
  "Nene! Bakya tsoron asirinmu ya tonu?"
Nene ta harareta.
"Kinsan iyakar tsawon lokacin da na dauka ina ajiyar kwalinnan? Ai bazan bari damarnan ta kufcemin ba, yau dan kwal ubannan sai kwanan daji."
  Kafin Abule ta ce wani abu suka tsinkayi sallamar Mati.
  A razane suka dubi juna har Nene batasan sadda ta cire yatsanta daga bakin jinjirin ba ai kuwa ya canyara kuka.
  "Lafiya Fad'i? Kin haihu ne?"
  Mati dake jefowa Fad'insa tambayoyi ya tsaya gami da saurin bin inda ya jiyo kukan jaririn.
  Duk kokarinsu na kada ya fahimci shirunsu saida ya gane. Nan ya hau salallami, wani wawan tsalle da ya doka sai gashinan gaban Nene, ya kwasheta da mari kafin ya fiddo jaririn daga kwali.
  "Ka gantanan, yasin ba hannuna ciki! Yanzu na shigo daga makwafta ina.." Fad'in Abule yayinda Mati ya katseta da sauri.
"Dalla can rufemin baki kema bakar munafuka! Wato kun yi shirin kashemin mata da d'a ko?"
Sautin karar Fad'ime ya kid'imashi, a guje ya fice zuwa d'akinta.
  Kan kace me Shafa da Delu sun shigo domin tun kukan jaririn na farko sun tsinkaya saidai ba su k'ara ji ba sai yanzun da Mati ke balbalin fad'a. Lek'owarsu suka san abinda ke faruwa suka bazamo cikin gidan.
Su ya bari a wajen Fad'ime yayinda ya fice nemo abin hawa don mik'a Fad'ime asibiti.
  Delu na gyara jaririn tana zubamusu habaici Shafa na tayata. Su kam kowacce na d'akinta sun k'unshe gaba daya a tsorace suke da abinda zai biyo baya.
  "Shegen, ashe d'agamin k'afa kawai ya ke." Fad'in Nene a k'asa-k'asa tana shafa kuncinta.
  Mati na dawowa aka wuce kai Fad'ime ga likita bayan ya kora Nene da Abule gidajensu da shika (saki) d'ai-d'ai.

Kashe Fitila 5

*KASHE FITILA*💡5

*Batul Mamman*💖

Abu kamar wasa sai gashi komai ya kankama dangane da samun aikinsa. Awaisu ya koma Fika sanar da mutan gidan halin da ake ciki da tafiyar da zaiyi Lagos.

Kafin ranar tafiyar Maamu ta tura shi wurin yayanta ya karbo rago biyu cikin tumakin da ake yi mata kiwo ya sayar. Da kudin wanda ko sisi bata cire a ciki ba tace yayi kudin mota da guzuri.

Kamar kullum kyakkyawar addua yayi mata tare da godiya.
"Ba godiya zakayi min ba. So nake idan kaje ka dage yayi abinda ya kaika. Lokaci yayi da ya kamata ace kana da iyali kaima sannan ka fara ragewa dan uwanka nauyi. Ga zuri'a Allah Ya bashi sosai. Kaga yanzu cikin yaran sai ka rinka biyawa wasu kudin makaranta idan ka fara daukan albashi"

"Maamu kenan, Allah Ya bani iko. Nifa babban dana ma sunansa Haris. Tun yanzu ya kamata ki fara kirana Abu Harith irin na Larabawa"

Neman abin da zata buga masa tayi saboda rashin kunyar da yake yi a gabanta. Ba shiri ya tashi ya gudu.

Bayan kwana biyu Harisu ya raka shi tasha ya wuce Lagos. Watansa daya wurin induction din sababbin ma'aikatan banki. Ana gamawa ya koma Abuja domin jiran posting. A wannan lokacin ne kuma soyayya mai karfi ta shiga tsakaninsa da Gimbi. Tun yana ja da baya har ya amince. Ji yake yafi kowa sa'a. Mace kamarta tana soyayya da talaka irinsa.

Da taimakon Alh Mudi ya samu aka barshi a Abuja maimakon Ilorin da aka tura shi da farko.

Ganin yana da kwanaki goma kafin lokacin fara aikin ya hada kayansa sai gida. Gimbi harda kuka da zai tafi saboda sonsa take da gaske. Alkawari yayi mata cewa bazai wuce sati ba zai dawo sannan suka rabu.

Yana isa gida yara suka fito ana ta murnar dawowarsa. Ya shiga ciki nan ma su Baaba sai murna aiki ya samu. Nan yake jin kwanaki hudu da suka wuce matar Harisu ta biyun ta haihu. Kai kace shi aka yiwa haihuwar ya fita neman dan uwanansa yana murna.
*****

Washegari suna zaune a bakin shagon Harisu suna hira Awaisu yace ya zabawa jaririya suna Ummu Ruman. Amma Rumana za'a kirata.

"Kai kuma a ina kaji wannan sunan" Harisu ya tambaya yana kallonsa.

"A littafin tarihi"

"Idan munje gida sai kayi mata huduba dashi" cewar Harisu

Duk da cewa ya riga yayi mata da suna Aisha amma baya son batawa kaninsa. Shima kuma Awaisun da yasan da hakan bazai taba kawo wani sunan ba.

Sai yamma suka koma gida. A bakin kofa ya tarar da dansa na biyu yana shirin fitowa.

"Sarkin yawo ina zaka da yamman nan"

"Baba kayi bako daga Kano. Shine aka ce na kirawo ka"

Harisu ya shiga ciki dakin Baaba inda suke yana tunanin waye yazo.

Abin mamaki Saminu ya gani tare da matarsa da yaransu biyar. Tsabar murna ya rungumeshi suna dariya.

"Bala dreban tifa ne ya fada min haihuwar nace to lokacin tada zumuncin mu fa yayi. Dole mu hada kan iyalinmu."

"Sosai kuwa, sannu yaya hanya"

Matar Saminu mai suna Amina da yaransa duk suka gaishe da Harisu. Ana ta barkwancin yadda zasu rinka magana tunda Hausa a gidan bata zauna sosai ba. Baaba da Awaisu sune masu Hausar sosai. Awaisun shima ya shigo suka gaisa. Fita yayi sauran kudin hannunsa yasa ya siyo lemo, kaji da kwai ya bawa Maman Antu uwargidan Harisu domin karrama baki. Yaushe zai manta Saminu a rayuwarsa.

****
Kwanansu hudu a gidan duk an saba kamar sun dade tare. Yaranma kowa da abokin sa ban da babbar wadda ta girmi duka yaran gidan.

Ana gobe zasu tafi ne Harisu da Saminu sun zauna hira da daddare Harisu ya sako zancen da yake ta son yi.

"Mardiya shekararta nawa ne yanzu?"

"Ka ganta tayi tsayi ko? Shabakwai zatayi da azumi.  Badi zata gama sakandire in sha Allah"

Harisu yayi murmushi "To Allah Yasa abin da zan zo dashi yayi maka. Nace mai zai hana mu hadata da Awaisu?"

Saminu ya kalle shi sosai "da gaske kake yi?"

"Indai ka amince. Wallahi Saminu ban taba ganin mutum irinka ba. Halayenka abin koyi ne ga wasu.  Idan na bari damar nan ta wucemu ai na cuci zuri'ar Awaisu. Mai alkhairi irinka dole a kyautatawa 'ya'yanka zato"

Saminu ya kama hannunsa kam "in dai haka ne na bawa Awaisu Mardiya halak malak inyi maka ta yara"

Dadi ya kama Harisu suna dariya "in sha Allah Awaisu bazai bamu kunya ba. Dama watan da ya wuce na gama biyan su Zakiyya kudin gidan Malam da ya fada rabonsu a gado. Gyara shi zanyi sosai kafin shekara  mai zuwa shima Awaisun ya tara abin da ya tara sai su zauna a ciki. Ba munyi maganar a Abuja zaiyi aiki ba? To muna sa rai zai sami muhalli kwanan nan. Kaga sai su koma can ya sa ta cigaba da karatu ma"

Saminu farinciki ya cika zuciyarsa. Shi yana yiwa Harisu kallon mutumin kirki. Shima Harisun kallon da yake yi masa kenan.

Sun yanke shawarar sanar da Mardiya babbar 'yar Saminu da Awaisu shawarar da suka yanke domin jin ta bakinsu da kuma basu hakkinsu don kada a zalinci kowa.

Awaisu wanda yake bayan kofa tun bayan yaji an ambaci sunansa ya fasa karasawa wurinsu. Ji yayi kamar an dora mada dutse a kansa. Shi kadai ya soma magana a hankali "yanzu wannan yarinyar da bata gama zama mace ba za'a bani? Wallahi da sake. Ko ban hadu da Gimbi ba babu inda zan kai wannan yarinyar"

Kashe Fitila 4

*KASHE FITILA*💡4

*Batul Mamman*💖


Ranar laraba da yamma Harisu da kaninsa suka isa Abuja. Da tambaya suka karasa gidan Alh Mudi Maibuta, dan kwangilan da Saminu ya nemi taimakonsa akan neman aikin Awaisu.

Gida ne babba irin na mutanen da naira ta zauna musu. Daga bakin gate din maigadi ya tambayi sunansu da abin da ya kawosu. Suna fada ya saki fuska tare da sanar dasu Alhaji ya bayar da umarnin yi musu iso da zarar sun karaso.

Wurin wata katuwar bishiya ya rakasu inda Alhajin yake zaune yana shan iska. Gefensa 'yan mata ne guda biyu sanye da kaya iri daya.

Tun tahowarsu Awaisu wurin babbar ciki ta kafe shi da ido tana murmushi. Shi kuwa hankalinsa bai ma kai gareta ba. Cike da girmamawa suka gaishe da Alh Mudi. Shima fuska a sake ya amsa musu sannan yace su shiga wani daki kusa da na maigadinsa.

Abinci yasa aka kawo musu aka yi musu tarba a mutumce. Sai da suka ci suka koshi sannan ya dawo ya karbi takardun Awaisu. Murmushin fuskarsa ya fadada
"Ikon Allah ashe kaima Bauchi kayi karatu. Kila ma ka taba haduwa da Gimbi."

A ladabce Awaisu yace "Wane ne hakan?"

Alh Mudi ya hau dariya "Yarinyar wajena ce, sune a zaune ita da kanwarta shigowarku dazu. Da yake sunan mahaifiyata gareta shine nake kiranta Gimbiya. To kuma kasan mutane, a hankali sunan ya koma Gimbi."

Harisu da Awaisu suka gyada kai suna Allah Sarki.

Alh Mudi ya cigaba da bayaninsa
"Shekararnan ta gama ATBU din amma Business admin ta karanta. Nayi magana da wani sun karbeta a banki zatayi bautar kasa. Shine kaga ina dariya da na ga kaima bangarenka kenan, to zan tura masa takardunka gobe. Kaga abin ma duk zaizo da sauki"

Godiya da addu'a suka rinka yi masa. Murmushi kawai yayi
"Saminu akwai kirki. Kaya kawai nake saya a wurinsa amma ina jinsa kamar dan uwa saboda iya mu'amalarsa da mutane"

Harisu yace hakane domin shima shaida ne.

Daga nan Alh Mudi ya yace lallai sai Awaisu ya zauna a Abujan domin idan ya bayar da takardun washegari mai yiwuwa zuwa litinin a bukaci ganinsa a bankin.  Sannan yayi alqawarin bashi makwanci har zuwa lokacin. Harisu ya rasa bakin godiya. Mutanen kirki basa karewa a duniya. Sai dai haduwa dasu dace ne. Duk kudin Alh Mudi Maibuta bashi da dagawa da girman kai.

Da safe Harisu ya koma Fika bayan yaja kunnen dan uwansa akan ya kula da kansa kuma ya kame mutumcinsa.
*****

Tun tafiyar yayansa baya fita ko'ina. Kullum yana daki sai sallah da take fitar dashi wadda Alhajin ko wani saurayi da Awaisu bai tantance matsayinsa a gidan ba suke jagoranta. Safe, rana da dare maigadi zai miko masa abinci ya karba da godiya.

Yau lahadi sun idar da sallar magariba Alh Mudi yace ya shigo falonsa su gaisa da iyalin gidan. Domin idan har ya sami aiki an barshi a nan Abujan to dole kafin ya sami wurin zama nan zai cigaba da zama tare dasu.

"Ni kuma ba mazauni bane, shiyasa na ga ya kamata kasan mutanen gidan suma su san ka"

A baya ya bishi suka shiga wani falo wanda aka kawata da duk wani abu na jindadi. Kafin su zauna wata mace ta shigo sanye da hijabi da alamun sallah ta idar. Sai 'yan matan ranar da suka zo biyu da wani yaro da suke sallah tare wanda bai wuce shekara goma ba.

Awaisu ya gaisheta ta amsa da fara'arta ta tambayi sunansa.

Kafin ya amsa babbar wadda yake tsammanin ita Alh Mudi ya kira da Gimbi tace "A.S Abali, Mama shine yayi vice president na S.U.G a makarantarmu"

Da mamaki ya dago yana kallonta. Shi dai bazai iya tuna fuskarta ba amma dai abin da ta fada gaskiya ne. Kyaunta kuwa tuni yayi tasiri a zuciyarsa.

Maman tace "Gimbi rawar kai, ai ba ke na tambaya ba. Naga yayi shiru ne shine nake son jan shi da hira ya sake damu."

Ta koma tana kallonsa "Alhaji yayi min bayanin komai game da kai. Allah Ya bamu ikon zaman gaskiya da amana"

"Amin Hajiya nagode. Allah Ya kara girma"

"Amin, sai dai Mama ake kirana ba Hajiya ba"

Daga nan sun dan taba hira wadda hankalinsa gabadaya yana kan Gimbi. Tunda ta fadi sunansa dazu zuciyarsa take kawo masa sabon tunani game da ita. Sai dai a wurin ya yakice shi. Ai ido ba mudu ba amma yasan kima. Ina shi ina 'yar babban gida irin wannan.
*****

Washegari da sassafe ya tashi ya shirya kamar yadda Alh Mudi ya umarce shi. Yana wurin maigadi suka fito tare da Gimbi. Taci kwalliya tayi kyau sosai.

A bayan mota ta zauna kusa da babanta shi kuma Awaisu yana gefen dreba. Babu inda ya gane a wurin da suke tafiya sai dai kawai yaga an rubuta Zenith Bank. A reception Alh Mudi ya barsu shi da Gimbi ya wuce wurin manaja.

Hira suke tabawa jefi jefi saboda shi dai ya kasa sakewa da ita duk kuwa da cewar ya fahimci sakon da yake boyewa a zuciyarsa itama shine a cikin ta ta zuciyar.

Ba jimawa Alh Mudi ya fito ya bukaci Awaisu ya shiga wurin Manaja. Shi kuma suka shiga wani dakin daban da Gimbi. A nan ne aka yi mata bayanin aikin da zata rinka yi.

Shi kuma Awaisu takardu ne aka bashi yayi ta cike cike. Bayan ya gama aka sanar dashi zai dawo washegari interview sannan yaje Lagos sati na sama training na wata daya daga nan ya jira posting.

Thursday, 18 January 2018

Kashe Fitila 3

*KASHE FITILA*💡 3

*Batul Mamman*💖

       

       *Tuna baya*

Da alamun gajiya ya shigo gidan yana daga kafa da kyar. Baaba ce ta fara ganinsa ta taso da sauri.
"Yaya Awaisu an dace?"

Girgiza mata kai yayi a hankali zuciyarsa a cunkushe da bakinciki.

"To kada ka damu, rabon mutum komai nisan lokaci zai zo gareshi. Ka wuce dakina abincinka yana can"

Cikin sanyin jiki ya wuce ta bishi da kallo. Sai da ta ga fitowarsa da kwanon abincin ta mayar da hankalinta ga Maamu da take zaune tsakiyar matan Harisu guda biyu tana tayasu tsinkar zogale.

Dan daure fuska tayi cikin wasa tace "Kina kallon dana ya dawo ko sannu balle ki tambayeshi yadda akayi?"

Maamu murmushi tayi "tunda kina kusa meye nawa a ciki. Da dai bakya nan sai nayi muku kara"

Baaba ta hau mita ita Maamu bata kyauta mata ba. Matan Harisu suka sa dariyar rigimar surukansu.

Da suka gama Maamu ta tashi ta shige dakinta ta dan turo kofar. Hawaye ne ya taho mata ta sanya habar zaninta ta goge. Tun dawowar Awaisu tana ganin yanayinsa zuciyarta ta karye. Daurewa kawai ta rinka yi tana yaken dole. Shekara biyu kenan yana neman aiki har yanzu shiru. Ita kam Allah Ya sani ta kure matakin jin kunyar Baaba Hure da Harisu. Wanda ya kawota gidan ya jima da rasuwa gashi nauyinsu ya dawo wuyan dansa.

Lokacin da ta auri Mal Sa'adu Abali da danta na auren fari Awaisu tazo. Shekararsa biyu mahaifinsa ya rasu. Yana da shekara hudu ta hadu da Malam har sukayi aure. Taso mayar da shi wurin dangin mahaifinsa amma sam Malam yaki yarda yace bai ga amfanin auren mace kuma a kyamaci 'ya'yanta na wani gida ba. Zaman lafiya suka yi sosai da Baaba Hure. Ita Baaba mutuniyar Katsina ce. Cirani ya kawo iyayenta garin shiyasa ta tashi da iya yarensu. Amma duk da haka tana Hausa da 'yan uwanta. Malam da Maamu wadda ainihin sunanta Safara'u duk 'yan Fika ne, yaren Bolanci sukeyi. Kuma haka duka gidan har yara da shi suke tashi sai dai suna Hausa kadan kadan saboda cudanya da Hausawan cikin gari.

Baaba Hure yaranta hudu. Baraka, Harisu, Ummukulsum da autarsu Zakiyya. Mace ce mai kyaun hali da sanin ya kamata. Sannan mai jajircewa wurin tarbiyar yara. Domin yaran sunfi tsoronta akan Maamu mai sanyi. Ita dai barta da yawan murmushi ko da ranta ya baci.

Haka suke zamansu gwanin sha'awa. Malam ya sanya Awaisu a makaranta Harisu ne yake rakashi  domin autarsu ma ta girmi Awaisu da shekara shida.

Yana aji biyu a sakandire Malam Sa'adu ya rasu. Maamu ta shiga tashin hankali saboda bata haihu ba a gidan tana gudun su bukaci ta tashi bayan an raba gado. Sanin cewa yanzu gidansu ko ta koma babu inda zata zauna saboda yayyenta duk sunyi aure da matansu a cikin gidan iyayensu yasa Baaba Hure tace ta cigaba da zama dasu tamkar gidanta. Karatun Awaisu kuma 'yar buga bugar da Harisu yake yi da nata jarin suka hada suna biya masa kudin makaranta.

A haka ya kammala ya fara shirin jami'a. Maamu ta sayar da gonarta ta biya masa kudin ya tafi Abubakar Tafawa Balewa University (ATBU) ta Bauchi inda ya karanci Banking and Finance.
Lokacin nauyi ya fara yiwa Harisu yawa ya soma tara yara.

A haka dai da karume karume suka rinka tallafawa har ya gama da sakamako mai kyau. Ga shakuwa tsakanin 'ya'yan gidan wanda bai sani ba bazai taba gane cewa Awaisu ba dan Malam bane.

A halin yanzu aiki yake nema ruwa a jallo abu ya gagara. Maamu kullum burinta ya sami abinda suma zasu gwadawa Baaba Hure da zuri'arta karamci ba don su biyasu ba. Sai don kawai ta nuna musu cewa bata taba manta alkhairinsu ba gareta.

Harisu ya kara aure iyali suna ta karuwa. Ya ciyar da dolensa ya ciyar da ita da danta. Wannan yasa take jin babu dadi.

*****
Bayan kwana biyu Harisu yaje Kano saro kaya a Kantin kwari kamar yadda ya saba duk karshen wata. Sunansa yaji an ambata ya juya yana neman mai kiran.

Murmushi ya saki tare da sassarfa wurin karasawa wurin wani mai shago suna dariya tare da rungume juna

"Harisu Abali"

"Saminun Kano"

Sake rungume juna sukayi sannan Saminu ya ja hannunsa suka shiga cikin shagon atamfofi. Lemo mai sanyi yasa aka kawo masa sannan ya bayar da kudi a siyo musu abinci.

"Ikon Allah, ashe rai kan ga rai" cewar Saminu yana kara kallon abokinsa.

"Ga zahiri dai, sama da shekara biyar sai yau Allah Yayi ikonsa"

Hira sukayi sosai ta yaushe gamo. Saminu yayi zaman Fika inda suka saba sosai da Harisu. Daga baya ya dawo garinsu Kano ya cigaba da kasuwancinsa. A hirar yake tambayarsa kaninsa ya fada masa ai har ya gama jami'a.

"Aiki fa?"

"Nan fa daya, yanzu ma tare muka zo zai fara tayani kasuwanci kawai kafin aikin ya samu. Yanzu ma yana Wambai wurin masu robobi"

Harisu da Saminu sun sha hira  sannan suka yi sallama da alkawarin haduwa washegari kafin su koma Fika.

****

Washegari kafin azahar sun isa shagon Saminu yi masa sallama. Yana ta tsokanar Awaisu an girma an dena kiran Yaya da an taba shi. Ya hada musu 'yar tsaraba daidai misali sannan ya ja Harisu gefe.

"Mutumina nayi maka karambani fa, jiya bayan rabuwarmu naje gidan wani tsohon dan kwangila da nake sayar wa shadda"

"Kana nan da shige shigen ka mutumina" Harisu ya fada yana murmushi.

"Me za'a fasa..yanzu dai mu bar wannan zance. Cikin hira nayi masa bayanin ina da kani da ya gama karatu yana neman aiki. Sai dai anyi rashin sa'a bansan me ya karanta ba. Shiyasa bayanin nawa bai cika ba"

Farinciki sosai ya bayyana a fuskar Harisu
" da gaske kake?"

Murmushi yayi ganin abokin nasa yaji dadi "yanzu dai yace sati mai zuwa zashi Abuja wurin wani kusar gwamnati. Shine yace idan zai yiwu Awaisu ya same shi a can ranar alhamis"

Kati ya dauko mai dauke da sunan mutumin da nambar wayarsa ya mika masa.

"Gashi Allah Yasa a dace. Idan yaje sai ya fada masa cewa shine kanin Saminu Zawachiki"

Harisu ya rike hannuwansa ya ma rasa kalmar godiya "idan munje zaka ce. Ai dole na rakashi. Allah Ya baka ladan zumunci."

Yafito Awaisu yayi da hannu ya matso kusa dasu ya fada masa halaccin da Saminu yayi musu. Shima godiyar yake yi kamar zasu ari baki su biyun.

Kashe Fitila 2

KASHE FITILA💡2

Batul Mamman💖

Fika LG-Yobe State

Yara ne suke ta tsalle-tsalle a tsakar gida saboda yau alhamis babu makarantar Islamiyya. Masu dan girman kuma musamman matan kowacce ta kama aikin gida tana yi.

Sallamar da suka ji ce tasa suka tashi babu babba babu yaro suka tafi tarbo mai yinta. Murnar ganin Kawunsu suke yi sai dai ganinsa rike da Rumana tana tangadin karya yasa suka yi cirko cirko. Sarkin surutun gidan ne ya ruga ciki yana sanarwa ga Rumana ta dawo.

Mahaifiyarta wadda ta kasance mata ta biyu cikin matan gidan bata san lokacin da ta janyo hijabi ta fito ba. Addu'a take yi Allah Yasa ba wani abin Rumanan tayi ba Kawunta ya kasa zama da ita.

Ko da ta fito sauran matan gidan wato uwargidan da amaryar duk sun fito suna musu maraba. Ganin yanayin Rumana yasa suka san babu lafiya. Maman Antu kamar yadda ake kiran uwargidan ita tayi saurin riko hannunta suka shiga babban dakin da yake mazaunin falo a gidan. Tuni Awaisu ya wadata musu shi da kayan kallo da kujeru masu kyau.

Bai bi bayansu ba ya wuce dakin Baaba Hure. A zaune ya sameta tana jiran shigowarsa tun bayan taji an ambaci sunansa da na Rumana. Sai da ya gaisheta cikin yarensu na Bolewan Fika sannan yayi mata bayanin dalilin zuwansu.

"Kuma ka tabbata ba aljanu bane da ita?"

"Ko daya Baaba, jiyan nan dai ta bani tsoro shiyasa nace bari na kawota ta huta kwana biyu. Makarantar tasu zanje sati mai zuwa duk da sun san bata da lafiya na sanar musu halin da ake ciki"

"To Allah Ya sauwake, ina 'yar uwata? Kwana biyu ko a waya idan nace yayanka ya kira ba ma samunta"

Dan murmushi yayi "tana nan lafiya, kinsan sai ta ajiye wayar ta manta inda take ma. Alhaji bai dawo bane?"

Kafin ta bashi amsa suka jiyo muryar Alhaji Harisu yayansa. Dakin ya karaso suka gaisa inda ya sake labarta musu dalilin zuwansu. Wannan karon harda matan gidan da Rumana a wurin.

"Zancen banza" cewar Alh Harisu
"Shine zaka biye mata ka baro aikinka ku taho"

Rumana ta tsuke baki, fatanta kada Alhaji ya bata shirin da suka kwashe sati uku suna yi ita da Yusra yace ta koma wannan kurkukun. Ita yanzu ko sunan Abuja ma bata son sake ji.

Shi dai Awaisu lallabata yace ayi kuma a tambayeta dalilin kin cin abinci. Domin ko mutan gidan suna ganinta sunyi korafin ramarta. Yarinyar da ko da tana makarantar kwana kafin komawarta Abuja da kibarta. Ita ko ramar nan ta kewar gida bata yi.

*****

Washegari da sassafe Awaisu da drebansa suka kama hanya.

Sai da Rumana taji tashin motarsu tayi wata kyakkyawar ajiyar zuciya. Za taci karenta babu babbaka, ta mike kafa taji dadin rayuwarta. Abinci kuwa tun daren jiya take yi masa cin hauka.

Bayan kwana biyu da dawowarta suna daki ita da babbar yayarsu da tazo daga gidanta. Hira suke yi Rumana tana bata labarin horon da akeyi musu a gidan Kawun nasu. Karshe ma tashi tayi tana kwatanta irin abin da tayi a clinic din makaranta. Mahaifinsu ne yazo ya tsaya yana sauraren bayaninta batare da ta sani ba. Ita kuma Maryama yayarta da ta ganshi ta kasa cewa tayi shiru sai kai da ta sunkuyar. Tana cikin nuna mata sandarewar da tayi a mota ta kula da Alhajin. Nan jiki ya fara rawa, kanta yayi yana duka ko ta ina.

"Har kinyi wayon yiwa dan uwana sharri Rumana?"

Ihu take yi tana kuka "Wallahi Baba ba karya nake ba. Ba'a bamu abinci sosai a gidan. Daga ni har Maamu bama koshi"

"Rufe min baki sakarai mara godiyar Allah. Sharrin naki harda Maamu a ciki? To zan kira Awaisun da kaina muyi magana"

A fusace ya fita ya shige dakinsa. Ko zama baiyi ba aka sanar dashi Baaba tana kiransa. Ya tashi ya fita.

"Ina gidan nan kake hukunci irin haka ko? duk kiran da nayi maka kuma baisa ka dena ba"

"Kiyi hakuri Baaba wallahi banji ba"

Abubuwan da Rumana ta fada ya maimaita mata. Gyada kai ta rinka yi har ya gama.

"Babu abin da ya dace kayi da ta fadi maganar nan sai bincike ba duka ba."

Cike da mamakin rashin gaskata zancenta yace "bincike kuma Baaba? Awaisu fa ake magana"

"Na sani, fada maka ne kawai banyi ba amma dan zaman da nayi kwanakin baya banji dadi ba. Kuma kasan Maamu da zurfin ciki"

Kallon mahaifiyarsa yayi yana mamakin maganganunta.

Fita yayi yasa aka kira masa Rumana. Ya tsareta da jan ido yace ta fada masa komai tsakani da Allah. Kamar an kunna rediyo haka ta rinka bashi labari kuwa. Tana yi tana kuka, shi kansa Alh Harisu idanunsa kamar gauta don bakinciki da bacin rai. Sallamarta yayi da gargadin kada kowa yaji maganar nan sai ya gama bincike.

Wayar kaninsa ya kira suka gaisa tare da taba barkwanci sannan yace ya hada shi da Maamu. Anyi sa'a yana gida da kansa ya kai mata wayar.

A zaune take sanyin AC yana neman illata ta amma ta kasa kashewa saboda karamin dansa Safwan ya kwashe batiran remote din ya saka a game dinsa. Da ya shiga hankalinsa bai kai kan rawar darin da takeyi ba balle ya taimaka mata. Wayar kawai ya mika mata.

Tana karawa taji muryar Harisu sai kwalla wadda tayi saurin mayarwa. Rabon da suyi magana wane wata biyu. Gaisheta yayi ta amsa muryarta tana rawa. Hakan da yaji kawai ya fahimci tana cikin matsala. Bai zurfafa tambayoyi ba yaje ya sanar da Baaba gobe zaije Abuja taho da Maamu.

Ganin ransa a bace sosai yasa ta dakatar dashi yana kokarin fita "kada ka manta Awaisu danta ne na cikinta, bata nemi taimako ba kada kayi shisshigi. Garin neman kyautata mata ka shiga hurumin da baza'ayi maraba da kai ba"

Cak ya tsaya yana auna maganar Baaba Hure.

"Yanzu sai kawai mu zuba ido idan har gaske ne tana cikin matsala a gidan?"

"Ba ido kawai zamu zuba ba kuma bazamu yi gaggawa ba. Komai na duniya a sannu ake binsa har a gano bakin zaren. Misali yanzu Rumana karya tayi mana, da wane ido zaka kalli kaninka ko Maamu idan suka ji?"
             
           Labarin Maamu

Kashe Fitila

© Fikra Writers Association

*KASHE FITILA*💡1

*Batul Mamman*💖

*FWA Girls Secondary School Abuja*

_SS 2A_

Hankalin malamin Civic Education da kusan duka daliban yana kan monita wadda aka sanya rarraba takardun test da akayi satin da ya wuce. Wannan ya bawa 'yan mata biyu cikin daliban da suke zaune a layin farko daga tsakiya damar karasa shirin abin da suke kullawa tun safe.

Daya daga cikinsu ce ta rike ciki tare da kwalla kara iya karfinta sannan ta sulale a kasa ta kwanta. Kafin malamin da sauran su ankara dayar ta durkusa a gabanta tana jijjigata a hankali  da muryar kuka take cewa "Rumana me ya sameki, tashi don Allah, wayyo...."

Murmushi ne yaso kwacewa Rumana ai kuwa taji kyakkyawan mintsini daga wurin Yusra kawarta "don ubanki idan kika tona mana asiri wallahi cewa zanyi ba dani akayi ba"

Tsabar tsoro ne yasa Yusra yin zagin. A lokacin malamin har ya iso, sauran 'yan aji duk an zagaye su ana tambayar me ya faru. Yusra harda kukanta tace haka kawai ta ga Rumanan ta fadi.

Health prefect aka kirawo daga ajinsu tare da taimakon Yusra da wata malama suka kai Rumana karamin asibitin cikin makarantar. Sannan aka nemi numbar makusancinta wanda ya kasance kawunta aka kira shi.

Bayan an saka mata allura ana yi mata karin ruwa ne kowa ya fita sai likita da Yusra. Suna jin shiru Rumana ta bude idanu tare da saukowa daga kan gadon ta durkusa a gaban likitan "doctor ka taimakeni idan Uncle dina yazo ka fada masa ulcer ta kusa cinye hanjina"

Duk da ya dauki maganar rainin wayo amma bai san lokacin da dariya ta subuce masa ba. Sai kuma yayi saurin daure fuska.
"Nayi miki kama da abokin wasanki ne ko me?"

Yusra ma durkusawar tayi "idan baka taimaketa ba wallahi yunwa zata kasheta a gidansu. Ulcer din gaske ce zata kamata"

Juyawa yayi zai fita Rumana wadda ta tabbatar idan hakkansu bai cimma ruwa ba yau kila banda yunwa jikinta sai ya gayamata a gida bata san lokacin da ta fizge hannu daga jikin allurar ta ruga ta tare kofar ba "idan baka taimaka min ba wallahi zanyi muku hauka a asibitin nan. Ka fada masa mugun ciwo ya kamani a kaini gidanmu kada na mutu a nan"

Saroro yayi yana kallonta. Bai ankara ba ya ga ta nufi gadon dakin ta daga shi da yake ba wani nauyi ne dashi ba ta kifar. Dan tebur din kusa da gadon ma hantsila shi tayi tana ihu da kuka. Yusra wadda tare sukayi shirin ciwon karyar ma sai da ta tsorata ganin da gaske Rumana tana neman yin hauka.

Suna haka likitan yana kokarin riketa taji muryar kawunta daga dan karamin reception din yana tambayar inda take. Idanunta cike da hawaye ta sake kallon likitan alamun roko da neman agaji.

Tausayi ta bashi, ita kuwa Yusra kuka take yi.

Awaisu yana shigowa dakin ya ganta biji-biji kamar anyi wasan kura da ita. Ga hawaye ya wanke mata fuska. Da saurinsa ya karasa inda take ya rikota "Rumana me ya same ki? dena kukan ki fada min abin da kike so"

Kasa magana tayi sai kukan da ta cigaba da yi. Ba a son ranta tayi wannan abin ba amma idan ba gaban iyayenta ta koma ba bata jin zata iya cigaba da hakurin zaman gidansa.

Hankali a tashe ya dubi likitan "me ya sameta?"

Hadiyar yawu yayi yana kallon yadda 'yan matan suka tsare shi da idanu "uhmm a binciken da nayi yarinyar nan tana fama da ulcer sosai har tana neman lahanta mata hanji" mamakin kansa yayi da biye musu harda aron kalamansu.

Girgiza kai yake yi alamun rashin yarda "Ulcer, ulcer ciwon yunwa? Mtsew, ba dai a gidana ba wallahi."

"Abin da bincike ya nuna kenan ranka ya dade" Tuni likita ya fara tsorata kada a daga maganar gaba.

Harzuka yayi "kasan ko ni waye zaka kira min ciwon yunwa? To ko maigadin gidana bazai kira yunwa ba balle 'yata"

Gaban likita ya fadi a zuciyarsa yace 'yarsa kuma, wace 'ya ce zata yiwa iyayenta sharri irin wannan. Harara ya jefa musu duk da ba kallonsa suke yi ba.

Awaisu ya katse masa tunani " kaga ka sallameta zan kaita babban asibiti."

Bai jira amsarsa ba ya  ya durkusa ya dauko takalmanta ya saka mata sannan ya kamata suka fita. Wani irin tausayinsa ya kamata. Sai dai ko ana muzuru ana shaho da yardar Allah sai ta koma garinsu.

Suna shiga mota taji ya umarci dreba da ya kaisu asibitin kudi da iyalan gidansa suke zuwa. To kada karyarta ta kare kawai sai ta sandare masa tana mimmikewa. Hankalinsa ya kara tashi. "Uncle babu inda zani, ka mayar dani gida na mutu gaban Mama. Kada na mutu ban sake ganinsu ba"

A take ta karyar masa da zuciya. Asibitin dai yasa suka karasa sai dai a binciken gaskiya an tabbatar masa da gaske bata da kuzari. Tana bukatar hutu da abinci mai gina jiki.

Wannan jawabi ya sanya shi cikin rudani. Duk yadda yaso su kwantar da ita fafur taki yarda ita Mama kawai take son gani.

Gida suka koma yayi ta fadan yaya akayi bata cin abinci ba'a sanar dashi ba. Maamu mahaifiyarsa ita tayi jinyar Rumana a ranar. Da gaske ta rinka sambatu tana kiran babarta ko runtsawa basuyi ba. Dole washegari yayi shiri shi da dreba zai mayar da Rumana gida. Sai dai yana tunanin me zai fadawa dan uwansa a matsayin dalilin da yasa ya dawo da ita.

Suna fita Maamu ta leko ta tagar dakinta tana kallonsu. Hawaye taji ya taho mata mai zafi tana tunanin yadda karamar yarinya ta samarwa kanta mafita. Ita kuma ta yaya zata ta bar gidan dan da ta haifa a cikinta?

Gidan Mati 10

GIDAN MATI

©BINGYEL FULANI & RUFAIDA OMAR

    BABI NA GOMA

Ihun Nene ya janyo hankalin mutan gidan, gaba daya suka fito har da Abule wacce ta gwaggwa6e a d'aka tana kwa6a lallen. Kan kace me tuni Delu ta gyara zamanta jikin garu tana lek'e, itama Shafa ba'a barta a baya ba wajen ganewa idonta. Mati a rude ya nufeta.
  "Nene, lafi..."
Kii! Ya ja burki sakamakon wari da k'arar sakin tusa da ya bugi kunnuwa da hancinsa. Inna ta sanya salati.
  "Me zan gani haka Nene? Wane irin shashanci ne haka ki wuce Makewayi mana" Nene dake ta kokarin danne mazaunanta da hannu ta daddage ta ja numfashi sama tana mai hade jikinta dan ta tsayar da gudawar, ganin kamar an kara kunnu ta ya sa ta sakin wani wawan ihun "Wallahi ba ta tsayawa, na shiga uku ruwan jikina zai k'are. Kai Mati! Kai mati zan mutu, za ta zuƙen jini" Ai sai ta zabura ta danna a guje zuwa karshen gidan abu na yoyo. Mati ya yi sauri ya bita ganin ta zube gun, "Nene, nene, jin shiru ya sa shi toshe hanci yana jijjagata, sai kuma ya dago a tsorace yana duban Inna.
  "Kamar fa ba ta numfashi Inna"  "kai kauce nan, wane irin ba ta numfashi matsa ni ka ga na ba ta fastu aidi (First Aid)shashasha ko dabarun lafiya baka iya ba dake kanka ya cika da gashin jakai."  "Um Inna yanzu dai bata ba'a ake ba ki duba ta kiga ni Aradun Allah Inna ba ta motsi"
Inna ta dan na masa harara, sai kuma ta hau karewa Nene dake yashe kallo, ganin har yanzu Abun na tuttulowa daga jikinta ya sa ta kallo Mati "Tunda dai kai ne Mijinta matso kusa daidai bakinta ka lalubo harshenta ka gantsara mata cizo, shi ne zai sa ta farfadowa yanzu" Mati ya kalli Inna da ta kauda kai gefe tana jijjiga kafa kamar ba ita ta fadi wannan zance ba, ya waiga ga Abule dake matsar kwalla, ya dora idonsa kan su Delu dake bisa katanga, ai sai ya hau girgiza kai yana mai sharce gumi "Bazan iya ba! Kwarankwatsa dubu Inna wannan zalunci ne, ya zan ciji marar lafiya. Kuma sannan wannan ai Yahudanci ne." ai sai inna ta zabga salati tana mai fashewa da kuka Mati ya ce mata Azzaluma, kafin kuma ta share hawayen tana mai watsa ma masa dakuwa "To ka tsaya jahilci Nenen ta mutu, numfashin mutum na daukewa da minti goma idan bai samu taimakon gaggawa ba yake mutuwa"
  Jin haka ya sa Mati yin wurin Nene da sauri yana lalumar bakinta. Da dai ya zakulo harshen ai sai ya gatsashi da karfi. Baya ya yi yana ganin Nene ta yi wani irin cilla kafa. Tana fadi a hankali " Na mutu Mati" cikin magagi. Abule ta ƙara sautin kukanta "Inna dan Allah mu kai ta gun kula da lafiyan da kika kai Faɗime kwanaki"  Mati ya kalle ta, sai kuma ya yi waje da sauri. Ba daɗewa sai ga shi da mai Baro. Abule ta taya shi kama Nene aka dora ta bisansa. Suka ɗunguma Asibitin ƙauye.
   Bayan dube-duben da likitan ya yi sakamako ya fita. Nene dai banda Maleria ba abinda ke damunta. Likita duk tambayoyin da ya yi sun tabbata ba abinda ta ci na ɓata ciki tunda dai abincinsu guda ne. Dan haka ya daura ma karin ruwa ya rubutawa Mati O.R.S  da Napkin na manya aje a siyo mata. Ta kuma dinga daura napkin din duk bayan sa'a biyu. Karshe ya sallemusu da cewar su je Binni a duba ta da kyau shi kam iya na sa ke nan. Da komawarsu  gida Abule ta yi wuf! Ta fada ɗakin Nene tana sakayo kaba. Kallonta take cike da tausayi ganin harta tsotse rana guda.
  "Ni Nene anya ba maganin fadi kika sha ba? Na ganta sumul fa" Nene dake ji da yoyon kashinta ta mike a hankali  jiki na rawa" Shi ne wlh a randa na tadda shi a bude na sha,  na shiga musanyamin ta yi bakar muguwa wayyo ni. Mene makarin ki taimake ni Abule" Abule ta dafe kirji ido warwaje "Lalle dara ta ci gida Nene! Makarin da wuya Nene, ba za mu iya ba, sai kuma rushe da kuka."
  Nene ta yi ruf da ciki tana numfarfashi.
"Ki fad'amin Abule, ko menene shi zan iya."
  Jin haka Abule ta fyace majina ta soma magana.

Gidan Mati 9

GIDAN MATI
 
BY BINGEL FULANI & RUFAIDA OMAR

KASHI NA TARA

"Ke dadina dake jahilci kwarankwatsa dubu, haba ai ko karamin yaro ya san ruwa za a shekama Zubo a zuba Sugar shi ke nan ya zama lemo, batun lalle kuma kin manta Inna da shegen san fadanci kamar matar Bawan Sarki? Ai kawai kururuta mata kai zakiyi har ta sake ta baki kafar ki kunsa. " Nene ta yi shiru kamar mai nazari, sai kuma ta gintse fuska ganin Fad'ime ta fito zuwa makewayi. "Shegiya kai da wata fuskarta kamar taunanniyar gyada, Allah Abule yadda naki jinin Matar nan bank'i a cemin karta fito raye daga makewayin nan, ba ni zoban ki gani duka gidan zan had'a idan ya so a na tan sai na juye maganin" Ta fad'a tana wartar ledar zobon da Abule ta riga ta siyo. "A'A hankali dai Nene d'an kad'an ya ce a zuba saboda karfinsa." Ta balla mata harara "Wallahi duka zan juye idan za a sha giya asha ta dubu Abule!" Ta fad'a tana mai ficewa daga d'akin. Kai tsaye madafi tayi ta dauko kwanon sha ta juye zobon, ta tuttulo ruwa daga tulu ta sheka bisansa ta zuba Sukari wadatacce ta juya. Nan da nan ta kasafta na kowa, na Inna ta fara dauka dauka za ta kai mata, da shigarta kuwa ta tarar ta tana gyangyadi dan haka ta aje ta juya za ta fita. " Na shige su ni Uwar Biyu, Nene me nake gani haka?" ta juyo da sauri tana kallonta kafin kuma ta saki murmushi. "Zobo ne muka samu tsaraba daga Abule, shi ne na hadamana lemo da shi na san ai kin sanshi a birni." Inna ta balla mata harara tana turo kallabi goshi." To ke ina kika taba ganin anyi zobo ba a tace tikar ba? Wannan zobo za mu sha ko roman zobo? Idan ba ku iya abu ba ku dinga tambayata mana, ni nan da kuke gani na bayan zobo durinkis (DRINKS)har mangwar durinkis (MANGO DRINKS) Na iya, dan haka ban san jahilci d'auki ki ta ce shi sai ki kawon. Sum-sum Nene ta fice jin Inna ta koma yaren 'yan sama jannati. Sake gyarawa ta yi, tukun ta dauki na Fadime ta kai mata daki, komawarta daki ke da wuya Mati ya sawo kai Gidan. Kai tsaye dakin Fadi ya yi yana doka sallama, fasa kai dan karamin kwanon shan baki ta yi ta aje tana amsa masa    da murmushi kafin kuma ta mike tana kokarin zare masa zungureriyar hular da ke kansa. Ya shaki kamshinta da yake so na Karkar dan haka ya washe baki "ALLAH Amarya son ki nake kamar na mutu" Ta yi murmushi tana rangwada kwalelen kanta "A'A Maigidana mai ya kawo mutuwa kuma, muna tare ai." "Hmm! Ba za ki gane ba ne, idan kina kusa da ni ji nake kamar numfashi... KYYYATTT...FYYTTATAT... Ya dakata yana mai kakalo kaki, kafin kuma ya dunkulo majinar yana mai furzo ta waje da ba ta dire ko'ina ba sai cikin kwananshan Fadime dake cike da zobo. Ita da shi suka zubawa kwanon ido kafin kuma ta kwabe fuska. "Haba Maigida na sha ce maka ka dainamin tofe-tofe a bangon daki ko kasa, wannan ko a kan titi ne ba abin so ba ne. Yanzu kalli yadda ka haramtamin abinda tunda na gani yawuna ke tsinkewa. " Ki hakuri na mantane, yanzu bari na karbo miki kasona sai ki sha." ya fada yana mai daukan kwanon ya fice. Bisa randa ya tadda wani kwanon rufe da Fai-Fai Dan haka ya aje wancan ya dau wannan ya tafi. Nene da ta shiga makewayi rage ciki tana fitowa tayo inda ta ajje zobanta, ganinsa bude ya sata doka ashar "Ko wane shegen ya budemin oho, to idanma diba akai an sha wuta bal-bal tunda nawa ne. Ta fada tana hararar dakin Inna, kafin kuma ta daga kwanon ta kwankwade tas! Har kakin Mati. Minti biyar da sha cikinta ya yi wani irin juyi, jin kamar ruwa da wani wari na binta ya sata lekawa abin da ta gani na binta ratata ya sata doka ihu tana dafe mazaunanta "Wayyo ni Mati! Yoyon Kashi ya kamani.

Muna zuwa.

Gidan Mati 8

*GIDAN MATI*

BY BINGEL FULANI & RUFAIDA OMAR

KASHI NA TAKWAS

Kamar wasa cikin Fad'ime ya tabbata, Inna  har Asibitin K'auyen ta mik'a ta tare da Abule da Nene wadanda suka tik'e akan sai sun bisu sun ji da kunnuwansu. Itama Innar ba ta yi gigin hanasu ba don ta fi so su ji abinda zai hana su bacci.
  Ranar kam sun riga su yin gaba, zagi da tsinuwa ba irin wanda Fad'ime da Inna basu sha ba.
   Tun daga wannan lokacin kuma sai sabon tashin hankali da makirci ya k'ara ɓallewa a gidan. Akwai ranar da Nene ta shigo da Kuliya cikin gidan, sanin cewa Faɗime ba ta so. Hakanan ta lallaɓa ta  d'ora mata ita bisa gadonta tana cikin barci. Allah ne ya tsare da kwallayenta na jere basu zubo bisanta ba, saboda yadda ta dinga razana tana bige-bige a ɗakin. Ƙarshe dai Inna ta cece ta  da fitsari ya fiddo ta, ta juyo motsi ɓarin Faɗimen. Shi kuwa Mati yana can ya saki gañɗa ɗakin Abule. Sai washegari ne  Inna  ta sanar masa, karshe dai ta yi maganin abin da cewa duk wacce ta k'ara kawo wani Abu gidan ko da Ɓera  ne, ko ta jefi Faɗime ko Mati da bak'ar magana to a bakin aurenta. Da wannan aka samu bakinsu ya rufu suka koma rara  gefe, ƙarshe dai Nene ta tattara ta tafi wani ƙauye bikin kanwar kishiyar matar babanta.

  Inna  zaune gefen Fad'ime tana lalla6ata  ta samu ta ci kwad'on Zogalen da ta had'amata, ita kuwa Abule tana tankad'e Garin Tuwo tana wak'e-wak'en habaici. Fitowar Nene daga bayan gida ya sanya suka bita da kallo. Tayi daurin k'irji da tsohon zanin da ta ci 'yanmatancinta da shi duk a huje, k'asan duk ya rarake har idan ka zura hannu a 6uli guda zai ta6o mazaunanta. Fatarnan kallo daya za ka yi mishi kasan akwai nakiyayyar d'aud'a da bai kammala fita ba, jikinta  kuwa babu alamar ya wanku. Sai kyalli takeyi da nason datti da hamami dake tashi.
  "Ke jik'ar Maduga, wai wankan da ruwan Taɓo ki ka yi shi ne?" Cewar Inna.
Juyowa ta yi ta mata murmushi, sai kuma ta yi gaba tana murzo wata naɗaɗɗiyar dauɗa a wuyanta.
"Ah'ah Nene magana fa nake miki." Fasa ɗaga labulen kabar ta ta yi ta juyo tana kallon Innar, sai kuma ta haɗe mata hannuwa biyu tana roko alamun ta kyale ta.

"Uhm! Sabon salo, wai gemu a kafaɗa, halan da kika je bikin rashin magana kika koyo? To ai gaba ta kai mu, tuntub'en me carbi" Inna ta faɗa tana riƙe hab'a.

         Ganin haka ya sa Abule  ture tankaɗen gefe, ta mike zuwa dakin Nene.
Da shigarta ta same ta tsaye tana jan Jagira a girarta me kama da ta Tunku. Ai sai ta yi turus! Da mamaki tana ƙare mata kallo daga ƙasa zuwa sama. Ta sha Atamfa koriya fatau, da dinkin rigarta irin na Lema, wani abin mamakin har kallabin irin na atamfar ne, ba wai wari da wari ba. Kwalliya dai irin wacce ko da tana Amarya ba ta taɓa yinta ba. Sai ƙamshin man kadanya ke tashi da ta mulkawa jikinta. 
"Wannan kallon fa? Ban fa san irin kakannin ki ba?" Ta faɗa tana kaɗawa Abule hannu ganin yarda ta ƙame.
"A'a mamaki kawai nake, tunanina  ko dai ƙanwar Nene aka  musaya mana.
"Uhm! Kibar mamaki, kawai nasihar da Innata tamin kan zaman duniya da ƙiyama nake ta tunanowa yau."
"Anya kuwa Nene? Ke din ce kike tuna wanda ya mutu? Abokin kuka ai ba a ɓoyemasa mutuwa. Ki faɗamin abinda ya faru dake kika saki makaman haka? Ko duk tsoron kar Innar Mati  ta kora ki gida ne?"
Ai sai ta gundumo ashar tana me ture ɗaurin kallabin da ta dade tana murd'ashi dan ya yi kyau gefe. "Ni wallahi har kin ɓatamin rai, tsohuwar banzar can zan ji tsoro? To Talle Bodara ce ta ba ni maganin Ɓari, sharuɗɗan cikar maganin shi ne ko daka Ni Uwar Miji za ta yi kar na sake  na tanka ta. Kin ganshi a bakin Masai ake barbaɗashi."
Ta karashe gami da bankad'a k'asan katifarta, wani k'ulli ta fiddo a bak'ar leda ta nunamata.
Abule ta washe baki don tsabar farinciki. Ganin babu damar ihu ya sanya ta kaiwa Nene runguma sai dai tun kan ta k'ara sa had'a jikinta da na ta ta yi baya da sauri tsabar tashin da Nene ke yi kamar mai warin k'ashi.
  "Dagaske ki ke yi?"
Nene ta ta6e bakinta.
"Ni idan na fad'i abu na fi son ki yarda, zan miki k'arya ne? Nan da ki ke ganina ba ta wasa bace ba. Bari ki gani, wuyarta dai Fad'ime ta tsugunna saman Masai, ko kwad'o ne a cikinta sai ya fad'o.
  Jin haka suka saki shewa gami da cafkewa, sai kuma da sauri suka rufe baki.
"Um kinga bari na je kafin wannan Tsohowar karuwar birnin ta ankara."
Dariya Nene ta yi.
"Ai mukam Allah Ya had'amu da suruka."
  Suka dara sannan Abule ta fice.
      
      ***
  Shiru-shiru ciki zai zube anjima, gobe, bai zube ba. Ko ciwon kai Fad'ime ba ta yi ba ballantana a kai ga ciki.
  Ganin haka Abule ta yanke gwada ta ta sa'ar ko za'a dace. Nene ta ba ta goyon baya d'ari bisa d'ari, da wannan ta shirya tafiyar kwana daya da sunan ziyartar jikar abokiyar kakarta.
  Dawowarta akayi sa'a babu kowa sai Nene a gidan da ke faman zazzaga bala'i ta katanga tare da Delu wai Akuyar Delun ta shigo ta cinyemata shanyar da ta yi ta k'anzo.
  Ganin Abule ba k'aramin dadi ta ji ba, itace har da rungumarta tana tsalle, da ace akwai mutane a gidan da sun sha mamaki.
Bayan sun k'ule a d'akin Abule ne ta hau bata labarin abinda ta samo.
  "Ba k'aramar wuya na sha ba in fad'amaki. Ban ta6a rawar 'yan bori ba amma shege la'antaccen bokannan sai da ya sanyani yi. Amma tunda kwalliya za ta biya kud'in sabulu da sauk'i. Bari ki gani."
Ta ɓalle ɓarin zaninta ta fiddo k'ullin magani har biyu ta nunawa Nene.
  "Ya ce na kwa6a lalle da garin na d'aurawa Inna a k'afa don rufe bakinta. Shi kuma wannan."
Ta nuna d'ayan,
"A had'a Lemon Zobarodo a sanyawa Fad'ime a ciki ta shanye."
  Shiru ya biyo baya kafin Nene ta jinjina kai.
"Tabd'ijam! Aiki ja! Yanzu banda abinki ina mu ina iya haka? Ni kinga banda kwaɗa zobo da kuli ba abinda na sani kansa, sai yau da na ji ana lemonsa, kema  kuma na san duk sammak'al. Inna kuwa ba ta yanda za ta amince waninmu ya d'auramata lalle. Ina mafita?"

Muna zuwa

Gidan mati 7

*GIDAN MATI*

©ƁINGYEL FULANI & RUFAIDA OMAR

KASHI NA BAKWAI

"Maigidana Randar Zuciyata, Idan ka fita kaje shagon Bakari Mai Ashana ka ce a baka Makilin da Burushi." Mati ya washe baki yana kallon kwalelen kanta da yasha zanen shuku yana ta ƙamshin Karkar.
   "Wani sabon Abinci ne muka samu  Amarya Timah?"
Ta yi far! Da ido "a'a kai dai jeka kawo za ka ga abinda zan maka da shi."
"To shi ke nan, bari na yi wanka sai na fita na siyomiki, kinsan tunda na sameki bana iya fita banyi wanka ba.
Ta yi murmushi "Yauwa kama tunamin abinda na ce zan nuna maka rannan, muje Makewayin na maka kaga sai na cuɗamaka baya ma."
Ta faɗa tana jawo hannunsa su fita. Fisgewa ya yi yana nuna mata waje da baki, sai kuma a hankali ya ce "Ki rufan asiri safiya ce fa? Kinsan su Nene sun tashi kar ya zama abinda zan kasa cin abinci yau."
"Haba Maigida Ni wallahi kanamin irin wannan sai in dinga ganinka ragon maza, ranar kwana nane fa, kuma baka shiga haƙƙin kowa ba dan ka shiga Makewayi da ni, Matarka ce ni, ba ta aro ba, ko ta titi, kuma ko su ka shiga Makewayi da su ba abinda zai dameni tunda na san aikin lada ne.
Ya zare ido yana dubanta "Da gaske aikin lada ne?"
"Kwarai kuwa, ai zaman Aure indai ba cuta lada gare shi."
"Au to muje, amman dan Allah saɗaf-saɗaf bana so Nene ko Abule su tsinkayi motsi na.
"To shi ke nan muje" Ta faɗa tana me yin gaba. Ruwa ta tuttula  daga tulu a ɗan kwatashin wankan na su, ta sunkutu ta yi Banɗakin da shi, shi kuma Mati ya hau kewaye tsakar gidan, da dai yaji kamar babu motsi ko daga ɗakunansu, ai sai ya yi wuf! Ya faɗa Makewayin.
 
    Abule ta yi miƙa ba salati ba rufe baki, ta miƙe tana mai riƙe mararta sakamakon fitsarin da ya rike mata ita. A hankali ta fito waje, ganin ba kowa ya sa ta tsugunna nan gefen kwatamin tsakar gidan ta tsiyaya abinta, ta wawwatsa ruwa ba ko cuɗawa ta miƙe, za ta koma ɗaki ta jiyo kamar kacaniya a Banɗaki, a zatonta Kajin maƙotane ke kacaniya, sanin da ta yi sunsha faɗawa wawakeken masansu azo a yi ta hayaniya ya sa ta zari sanda da sauri ta yi makewayin.
  Sai dai fa turus! Ta yi tana sakin wani razanannen Ihu ganin Mati zaune a dutse daga shi sai gajeran wando, Amarya Timah kuma duƙe saitin hammatar Mati da wani ɗan ƙarfe a hannunta tana ta kwasar gashin hammatar tana hura masa iska, shi kuma yana dariya gami da fadin "Wai, ci gaba, daɗi wallah."

A firgice Faɗi ta yada ɗan ƙarfen saboda yadda ihun Abule ya kiɗimata, Abule kuwa da ƙyar ta jawo sauran numfashinta tana son daidai ta kanta, sai kuma ta ɗaga sanda ba tai wata-wata ba ta saukewa Faɗi ita a kafaɗarta.
"Sai na nakasaki baƙar mujiya me salon karuwai kawai, dan Ubanki ce miki akai nan bariki ne da zaki shiga wanka da Mijina, ko kuwa ce miki akai ni ɗin zan yarda."
Ta sake ɗagawa za ta rafka mata Mati ya riƙe sandan jiki na ɓari, "Karki kuma dukanta, zan fa rama mata, ke Abule ki fa fita idona da wanann jahilcin na ki, baki san aikin lada ba ne take yi? Ba na son sakarci fa." Ai sai ta yi baya tana kallon Mati sama da ƙasa, kafin kuma ta rangwaɗa guɗa.

"Ahl lalle Mati yanzu na san ka ɗauru tamau! a Minjaye, yanzu saboda wannan me zubin botoramin kake cewa zaka dake ni, Ni Abu? Da ka ce aikin Lada na ga dai kwanana ya shiga daga sanda aka kira assalatu."
"To na ji, yanzu dai wuce ki tafi haka ba zai ƙarawa faruwa ba."
"Bazan tafi ba, Ni fa idan ba jini na fidda mata ba bazan ji daidai ba."
"Haba Abu tawa, na ce kije dai, da daddare zaki ji saƙo."
Ta ɓallawa Faɗime harara dake dafe da kafaɗarta, ki sake gwadamana karuwanci gidan nan ki gani, wallahi na lahira sai ya fiki jin daɗi, shegiya da wani idonki kamar tsaka ta saka kwai."
Af! Abu mai sauki, wai kura ta zo gidan Maharbi, idan karuwancin ne ki gwada naki mana mu gani, ai wallahi babu wata me siffar Fanteka da ta isa ta hanani kula da Mijina. Aikin lada ne yanzu na fara, wanann sandar kuma bashi kika ci." Faɗi ta faɗa tana murguda baki.

Sanin Mati ba zai barta ta sake taɓa Faɗi ba, ya sa ta  juya ɗakinta takaici fal ranta.
**  ** **

         Tun bayan da akayi cacar baki tsakanin Abule da Fad'ime gidan ya k'ara kacamewa. Tsakanin Abule da Nene sai ka rantse tun da can kansu a had'e yake tsabar amincin da suka k'ulla na munafunci. Koda suna cikin habaice-habaicen su ne Fad'ime ta fito tsakar gidan nan za su ɓige da shewa suna watsamata bak'ak'en magana a fak'aice. Ko kallon inda suke Fad'ime ba ta yi balle su saka ran za ta tankamusu.

   Ranar wata laraba wanda ya yi daidai da cikar Inna kwanaki goma sha shida a birni, Abule da Nene suna zaune a gaban d'akin Abulen suna k'us-k'us tare da Shafa makwafciyarsu. Shafa ke yi musu tallar magungunan gyara na mata kala-kala. Ta d'aga wani k'ullin gari tana fad'in.
  "Kun ga wannan? Na rantse da daren farkona da jikan Lamid'o yana da masifar kyau. Ke wannan da ku ke gani sunansa 'Saki Matar Uba'."
  Nene da ke soshe-soshenta ta dubi Abule suka yi wata iriyar shewa gami da cafkewa.
  "Inda ranka ka sha kallo! Yo Allah na tuba idan kura na magani ta yiwa kanta mana!" Fad'in Abule.
  "Atoh, taya ni gani! Wai Matar kwarto da tallar maganin mata." Nene ta cafke.
Jin haka ya sanya Shafa kallonsu a fusace kafin ta d'an kalli d'akin Fad'ime, ga dukkan alamu batasan ma me suke yi ba. Ta maido dubanta gare su cike da borin kunya ta ce.
  "Oho dai, gwara ni akan ku, haka za ku k'arata a borori."
Ta hau tattara komatsanta a sadda suka yo mata ca! kowannensu da bak'ar maganar da yake yarfamata.  A daidai nan kuma Faɗi ta fito daga ɗaki da gudu zuwa bakin makwararar  tsakar gida ta hau sheƙa amai kamar ba gobe.
Nene ta miƙe ido waje tana tafa hannu, yayin da Abule ta dafe kirji tana duban Faɗi dake  duƙe.
"Duka-Duka  yau kwana nawane da Auren ni Nene? Taya ni lissafi Abule.
  Abule ta hau kasafta yatsun hannunta, sai kuma ta zare ido waje.
"Duka-duka kwana goma sha bakwai kenan, kar dai da ruɓaɓɓan kwai aka shigo?"
"Oh ni Nene, wannan wace irin haɗama ce haka, ranar farko da rabon ciki kamar marainiyar Karya? Ke kuma maƙaryaciya kika cemin ba ai komai ba ranar jikin tagarsu kika kwana?"
Abule ta ɓalla mata harara, "tuna dai, ke kika cemin ranar da aka kawo ta jini take, koma dai menene ni ban yarda da wannan Salon ba, ban taɓajin cikin dake bayyana kansa daidai da lissafin zuwan Amarya ba. Sai dai idan da shi aka shi..." Nene ta yi Wuf! Ta rufemata baki jin sallama kamar ta Inna.
"Barta ta ƙarasa mana manyan Akuyoyi, ai na dade tsaye ina sauraronku, wanda ya gani dai shi ya ji kunya wai kallon fitsarin makaho. Idan ba ku da kuke cikin ƙauye, haihuwar ƙauye, renon ƙauye, auren ƙauye, ina na taɓa ganin ana laɓewa sabuwar Amarya? Kunyi asara wallahi Nene, matsa ni na duba 'yar mutane, shashashai masu wankin kai da ruwan daddawa, idan ma da cikin ta shigo sai me? Na ce sai ƙaƙa? Irin kune a jahannamar ma can ƙasan wailun kuke. Sannu 'yarnan, sannu."
  Inna ta k'arashe tana mai k'arasawa ga Fad'ime wacce aman ya d'an lafawa.
  Gefe guda ta ajiye akwatin kayanta, ta yaye gyalenta ta dora saman akwatin kafin ta tattare zaninta dinkin rafa siket. Ruwa ta zubo a buta gami da mik'omata.
  "Tayani duba Abule, toh wallahi ba za ta saɓu ba bari Matin ya zo, ni ban yarda wannan cikin nasa bane, ga dukkan alamu dai mutum da abinsa ya zo, ai daman ni nasan za'a rina, angama yawon ta zubar an k'untso.."
"Ki ka k'ara magana a wajennan sai na nunamaki ni ce nan na isa da Mijinki don kuwa yana zuwa zan sanya ya sallamaki ga tsohonki."
  Nene ta yi d'if ta ja hannun Abule wacce ranta ke ƙuna suka fad'a d'aka. Shafa kuma da ke gefe kunne waje, tayi saɗaɗa ta fice daga gidan.

  "Mun shiga uku Abule, yanzu idan ta tabbata matarnan juna biyu gareta ya za mu yi?"
  Fad'in Nene kenan yayinda gumi ke tsirfomata. Abule wacce ta rasa bakin magana tsabar bakin ciki da tashin hankali, sai a lokacin ta iya bud'e bakinta ta ce.
"Hum, ni na rasa ma abin cewa wallahi."

  Sallamar Mati ce a gidan ta katse su, suka  yi shiru suna sauraron yanda Inna ke gayamasa rashin lafiyar Fad'ime da kuma cewar Fad'imen na tunda ta zo ba ta ga Al'adarta ba.

Muna zuwa

Gidan Mati 6

*GIDAN MATI*

© BINGYEL FULANI & RUFAIDA OMAR

KASHI NA SHIDA

Inna ta hau tafa hannuwa tana salati iyakar k'arfinta, kan ka ce me magulmatan makwaftansu sun hau lek'e cike da al'ajabi.
   "Yau na ga abinda ya fi karfina ni Uwar biyu! Kai! Kai! Wallahi ba za ta sa6u ba, Mati!"
  Ta juya ga Mati wanda zufa ke ta karyomasa, gabadaya ya susuce, daman ita Abule ya san k'arya ce ta shukamasa musamman da ya ji tana maidawa Delu irin tuggun da ta shirya na iska, ita kuwa Nene bai ta6a kawowa k'arya ta ke ba, a zatonsa idan Abule ta ɓata rawarta da tsalle to yana da mafaka a wajen Nene. Sai dai ashe dukkansu taron na ayya ne.
  "Eh dole ka rasa bakin magana mana! To wallahi ba za ta sa6u ba! Ko ka k'ara aure ko kuma ka saki kowace shegiya ta koma akurkin ubanta. Za6i ya rage naka, yanzu na ke son amsata."
Inna ta k'arashe tana gyara zaman siket dinta na buje. Nene da Abule suka shiga tashin hankali, kada fa su yi biyu babu.
  "Kai nake sauraro ka tsayamin k'erere kamar liman ya manta Fatiha."
  Mati ya saci kallon Matansa, to da ya rasa tafkekiyar gonar Inna da kuma gida ai ya gwammace ya k'ara auren ya samu haihuwa.
  Ya mai da idanunsa kan Innarsa.
"Shikenan, ki nemo min mata."
Ai sai Inna ta rangad'a gud'a.
"Ayyiriririii! Haba ko kaifa, yanzu na tabbatar da cewa kai jini na ne. Sai ka shirya don kuwa yanzu za ka yi aure."
"To amma..."
"Amma me? Inna ta katseshi tana harararsa.
"A'a wai dama gani na yi su biyun ma mangalar jakai na biyu bata iya rikesu da ita, shi ne nake tunanin kar ta ukun ta shigo kuma idan ina cin abinci sau biyar a rana na dawo sau uku."
"To batunu ƙiyama sarkin ci, in ce dai gidan nan nawa ne?"
"Naki ne har ni d'inma." Ya faɗa yana dukar da kai.
"To tunda ni zan ma auren mene na tunani? Idan ta ciyarwa kake zan ƙarama akuya da rago ka kiwa ta. Ina ce dai shi ke nan?" Ta waigo ɓarin da su Abule ke tsaye.
"Ku kuma sai ku shirya don kuwa falleliyar budurwa zan samar masa, ba irinku zawarcin titi ba."
Bak'in ciki ya turnuk'e Nene da Abule. Musamman Nene da ta tabbatar bata kai na ta matancin ba, amman dai ai ita ce ta fari, kuma  ma ta toshe yanda ba za a gane ba, don haka ta karkata baki.
"Allah na tuba ko dubu zai auro ba kamar ni a zuciyarsa, ni ce dai Nenen Mati, kaf k'auyennan an shai da soyayyarmu."
Inna ta bankamata harara kawai ta wuce d'aki. Shi ma Mati da saurinsa ya fita ya hau jakinsa ya fice. Abule ce ta saki shewa.
  "Aikin banza wai bille a d'uwawu, duk dai abinki bai sanya an fasa auroni ba, dad'in abin ma ba abinda bansani ba. Ina ce da sa hannun aljanu da 'yan bori a aurenki da shi ko?"
  Nene ta fusata, za ta kai mata bugu tuni Abule ta nufi d'aki, ta mai da dubanta ga masu lek'e.
  "An yi asara munafukai da tsakar rana babu ko kunya!"
  Babu wacce ta tankamata acikinsu, ta gama haukanta ta fad'a d'akinta.
      
BAYAN WATA BIYU

Ta faru ta k'are, duk wani shiri da gyare-gyaren da ya dace a yi na zuwan Amaryar Mati an kammala, amaryar ba wata bace illah Faɗime d'iya ga aminiyar Inna, Ladidi. Daidai da lefe Inna ce ta koma birni tare da Ladidi suka haɗo. Abu kamar wasa dai aka sanya biki sati biyu, duk irin borin Nene da Abule bai sa an fasa ba, ganin babu Sarki sai Allah ya sanya suka hak'ura.
  An kawo Amarya lafiya lau da gud'a da komai, cikin 'yan rakiyarta har da Shafa da Delu.
  Kwanan Amarya d'aya a gidan Inna ta tattara ta koma birni da zummar sai nan da sati biyu za ta k'ara lek'owa.
       Nene na zaune ta tsefe kitsonta wanda ya kusa shekara yayin da Abule ke kwance saman tabarmar kaba tana jifanta da wak'e-wak'en habaici tana ramawa suka tsinci muryar Mati da Amaryarsa suna shek'a uwar dariya, suka dubi juna da sauri kamar wadanda aka mintsila suka nufi k'ofar d'akin nata har suna bangaje juna, ƙarshe dai suka nutsu suna lek'esu.
  Amarya Faɗi  ke kwance saman cinyar Mati, shi kuma yana yagar tsire yana sa mata a baki suna hirarsu cike da nishad'i. Nene ta dafe kirjinta gami da had'iyar yawu. Ba ta jira komai ba ta yi wuf ta shige ganin haka Abule ta ja baya tana mai rike ƙugu.
  "Kan uban can! Wato  Mati dama amanarmu ku ke ci? To wallahi ba za ta sa6u ba! Sai dai ayi raba daidai!"
Za ta d'auke ledar naman Faɗime ta cafke hannunta ta mik'e tsaye.
  Baki Nene ta saki ganin shigarta.
  "Riga da wando a gidan nan? Jakar Uba! Mati karuwar birni Innar ta auromaka ashe banda labari?"
Harara Mati ya sakarmata bai ce komai ba don wani sa'in yana shakkarta. Faɗi ta kauda fuska gami da murgud'a bakinta da ya sha jan baki.
"Ke Malama don Allah ki bar nan wallahi warinki na tayarmin da zuciya. Ga dukkan alamu dai ko wankan tsarki ba kya yi."
Ta saki hannunta.
"Kuma wallahi ki ka k'ara ta6a ledar nan sai na  miki ihun mahaukaciya. Ce miki akai Ni haɗamammiya ce irinki? Ga naku kason can a gefe dan bazan yarda Miji na ya tashi da shanyayyen ɓarin jiki ba ranar gobe ƙiyama."
  Nene ta hau tafa hannu da shewa.
"Hehehe!  Yau nake ganin bariki a gidan nan, ashe kuwa yau wata za ta bi tsohon najadu barzahu. Idan kin fasa kirana mahaukaciya ba ki cika d'iyar Ladidi mai siyar da kayan maye ba!"
  Fad'in haka keda wuya, ta kai hannu za ta d'auki ledar,  Faɗime ta damk'i gashinta ta mai da ta baya, tayi taga-taga za ta fadi k'afar Mati dake ƙasa ya miƙe ta kwashe ta sai gata Tim! A ƙasa tayi zaman 'yan bori.
     Faɗi ta juya da Mini-minin idanuwanta ta dubi Mati "Sannu Maigida bata dai jima ciwo ba ko?"
Mati ya washe baki ya ce "Faɗi Amarya ina gabanki ai bana jin ciwo."
Ta yi masa far! Da ido ta ce, "Mai gidana na sha ce maka Timah zaka dinga kirana yarda kawuna na birni ke faɗi.
Taɓɗijam! "Yau na ga sabon salo wai tafiya bariki da Uwa" Cewar Abule daga bakin ƙofa.

        Amarya ta waigo ga Nene dake baje ƙasa tana cije baki, "Ke kuma ki ci gaba da shiga shirgi na, wallahi da ruwan sanyi zan dafaki dan ban iya dambe tsakar gida ba, balle na haifawar maigidana talauci, ku da kuka saba kuje can ku ƙarata, ga tsiyarku nan." Ta faɗa tana tura musu kasonsu na tsire.



Muna zuwa.

MUN GA YABONKI YAKE GARKUWAR MUNANA, MUNA GODIYA.

Gidan mati 5

*GIDAN MATI*

©BINGYEL FULANI & RUFAIDA OMAR

KASHI NA BIYAR

    Inna ta d'aga hanci sama taja iska, sai  kuma ta furzar ta baki tana hararar kwanukan da Nene ta aje gabanta.
"Uhm ni wai da mushe kikai miyar ne Nene?"
"Me kika gani Inna?" Nene ta fad'a tana so sa kai.
"A'a gani nayi tunda kika doso gurinnan ya cika da tsami da k'arni tamkar wacce ke aiki a kwata ko mutuware."
'Ai fa, komai na yi ban burge ba, to ai sai dai ki mutu, aikin na Mati ne, mallaka kuma tawa ce, sai shegen kinibibi da wani bakinta kamar na ba'kar Akuya...' Ta faɗa da gunguni
"Me kike cewa ne?"
"A'a cewa na yi Binta Sudan ne na balbala a jikina saboda kiji ƙamshin."
"Ko kuma Binta Maliya ba? To wanann dai ƙarni yake sai a sake lale, ki kwashe kwanukan nan daga gabana, anjima zansa Mati ya karbomin Abincin daga gidan Larai."
"Uhm gaba ta kaini, dama ke na tsamewa kai da ƙafar kazar." Ta faɗa da 'kun'kuni tana tattara kwanukan.
"Baki ji ba" Inna ta fad'a
"Ina ji Inna" Ta fad'a tana gabda barin d'akin.
"Idan gyaran zaki yi ki fara gyara can cikin, shi ne ko da kinsa turaren zamu ji dadinsa, amman wanann in gayamiki gaskiya yau sai an turaramin dakin nan da miski zan iya zamansa. Yanzu haka sai na sha kanwa sabida kumburin ciki."
"To masharranciya." Nene ta fadi a hankali tana barin d'akin a fusace.
Abule dake maƙe a gefe tana sauraro ta k'yak'yace da dariya tana juyawa Nene mazaunai. Nene ta yi kwafa tana gyaɗa kai, kafin kuma ta yi dakinta tana mai sauke kaba.
                
                    Gab da Maghriba Abule na tsakar gida tayi ɗaurin kirji, da zabira a hannunta tana tsifar kai. Can daga k'ofa kuma Nene ce zaune tana gyaran Tafasa tana yi tana sakin habaici a waƙe.
"Munafuncin dodo dai mai shi yakan ci, yau ba jumma'a ba idi ba, ba kuma kwanan mutum ba ya d'au niyyar wanka harda tazar kai na asara." Nene ta faɗi da karfi tana hararar Abule."

"Oh ni Abu? Lalle idan ta karewa kare barin haushi yake ya koma tunkuyi, na ga dai abin rabo ne auran Mace da ciki. Ki gwada naki salon mana mu gani, ai wani asirin baya ci da turaren hayaki sai an had'a da yan dabaru."

"Uban wa ke asiri da turare?" Nene ta faɗi a fusace tana ture fai-fain tafasa gefe."
"A'a ai kinji matsalarki baki cin ribar magana, yanzu mene na sakin na maguzawa a wannan hirar? Ni kinga wucewata yin abinda zai fisshe Ni. Ta faɗa tana mai sunkutar bokitinta ta fada Makewayi.

Nene ta ciji yatsa tana mai tura baki gaba, sai kuma idanuwanta suka sauka kan kayan da Abule ke d'orawa saman yar katangar bandakin ta langa-langa. Abin mamaki harda wani tsohon dankwalin wata atamfarta me fanteka da mati ya sa mata tun a toshi. Har dai ta juya zata wuce, sai kuma dai ta sake juyowa tana  kallon katangar zuciyarta na kiyastamata abinda Abule ke yi da kaya haka. Nan fa idanuwanta suka sake sauka kan wata tsummar rigar Mati da tun yana Saurayi ta sanshi da ita. Wani makirin murmushi ta saki da ta gama hasaso abinda take zato. Ai sai tayi gun 'yar katangar a hankali ta janye kayan bata bar mata komai ba sai zanin da zata yane jikinta.

      Da sauri tayi ɗaki gurin Inna dake gyangyadin shaiɗan na gabda Maghriba. Itama Innan sai da ta firgita na ganin yarda Nene ta fad'o Mata ba ko gafara dai.

"Lafiya Nene kika katsemin barci haka dan rashin mutunta Uwar Miji?"
"Bari dai Inna, ai abinda na gani yau idan ban sanar miki ba na cika ma-ci Amana, na rantse miki da izifi sittin  Abule cikin zani gare ta. Idan baki yarda da batunnan ba biyoni kofar Makewayin ki gani."

Inna ta watsa mata wani kallo she'ke'ke, sai kuma ta mi'ke tana tura d'aurin kallabinta gaba."
"Muje na gani." Ta fad'a tana yin gaba.
        
                  Abule da ta gama jika-jikan ta mi'ke za ta mai da zannuwanta ta d'aure yanda ta saba, ai sai ta tarar babu, ta d'auka ko baya suka faɗa dan haka ta fito a sad'ad'e tana Addu'ar Allah ya kau da idon Nene har ta kwashe. Sai dai fa turus! Ta yi ganin Inna da Nene tsaye tana sakar mata dariyar Mugunta. Jiki na tsuma ta sunkuyar da kanta 'kasa.

"Shegiya guntuwa me bakin hali, abinda ban zaci gare ki ba sai gashi ya tabbata gunki. Uwar wa ta koyamiki wanann kinibibin ko dan ganin yar uwarki na da cikin? Inna ta faɗi tana mai kai mata rankwashi a jikakken kanta.

"A'a Inna lafiya kike bugurmin Abule" Mati ya faɗa da shigowarsa kenan.
"Zaka rama mata ne? Sha-sha-sha kawai, Matarka na cikin Zani dan sakarci ka kasa gane wa."

Ya kwalalo ido yana  dubanta, sai kuma ya hau sosa kai yana noƙewa.
"A'a Inna ya za ai na sani, abinda rabon da ayi abu tun watan shekaran jiya.
Ai sai Inna ta hau tafa hannu da Sallallami.

"Haka Auren ya mayarmin kai Mati sai abinda Mace take so?Mene amfanin auren idan ba za ka taki mace tamkar gona ba? Ya kinan baƙar Munafuka sai kin faɗimin abinda  kike bawa dana da har kike juyashi haka ko kuma ki tafi gidan Ubanki wallahi."
Ta faɗa tana jawo gashin Abule. Da sauri Mati ya shiga tsakani yana faɗin "Sakarta Inna."

Da dai Abule ta fito daga hannun Inna ai sai tayi kan Nene dake ta sheka dariya a fusace tana faɗin " Bazan fita Ni kaɗai ba sai da ke bakar mujiya muga naki cikin mana in gaske ne." Ta kai mata wawura.
Nene ta kankame jikinta tana ture Abule, ta ɗaga hannu zatai naushi, Abule tayi nasarar bankare hannun ta kuwa gatsa mata cizo a hammata da dazunnan ta barbadawa hammatar toka dan ta rage tsami, ai kuwa bata ɗaga bakinta gurin nan ba sai da ta cisge gashin hammatar Nene har jini yayi tsartuwa.

Nene ta saki ihu tana dafe hammatarta. Abule kuwa ta yi wuf! Ta fisgo zanin Nene sai ga tullin tsummokara ɗaure a ciki. Wani abin mamakin har da wani koren Gajeran Wandon Mati da ya gaje shi tun gurin ƙaninsa yasha doyin jakai da warin fitsari, da Mati ya shafe shekara yana nemansa, yau sai gashi a cikin Nene ɗaure...



Muna zuwa.

Gidan Mati 4

*GIDAN MATI*
 
©BINGEL FULANI & RUFAIDA OMAR
     
     KASHI NA HUDU

Assalamu Alaikum mutan gidan." Fad'in 'yar doguwar dattijuwar kuma tsamurmura mai sharɓa-sharɓan tsagu a gefen bakinta, bak'a ce wuluk kamar d'anta Mati. Mati ne a gaba d'auke da k'aramar akwatin kayanta, ita kuwa tana biye da shi a baya.
Abule ta soma fitowa daga d'aki sai Nene daga band'aki suka saki baki suna kallonta.
'Ikon Allah, wai na kwance ya fad'i.' Cewar Abule kenan a k'asan ranta ganin shigar da surukar ta su ta yi, wata k'aramar Atamfa Super ce ajikinta an mata dinkin riga da siket sai wani babban mayafi da ta yafa a kafad'a ba rufin kai ba. Fuskarnan ta sha farar hoda, ba'a gane wa sakamakon bakin fatarta da ya ciza saidai kuma kana gani ka rantse yanayin hunturu ne wanda ya yi sanadin da fatar fuskar nata ya bushe ya yi furu-furu, ga uban jan janbaki da ta lafta a le66anta masu tudu.
A hankali Nene ta maida dubanta ga Abule, akayi sa'a itama ta kalleta sai kuma suka sauke ajiyar zuciya kafin kowaccensu ta shiga rububin tarbarta da amsa sallamarta.
"Waalaikumussalam, lale maraba." Fad'in Nene kenan ta karasa bakinta a washe ta kar6i akwatin Inna, caraf itama Abule ta sanya hannu da zummar kwacewa ta kai nata d'akin.
"A'a menene haka? Yaushe akayi daren kuma da har ace gari ya waye? Malama sakarmin." Cewar Nene ta na k'ara jogana akwatin a jikinta.
Dole Abule ta saki tana harararta ta karasa wajen Inna cike da kissa ta ce.
"Maraba Inna."
Inna ta hau k'arewa Abule kallo, eh kam ta yarda da rahoton da Aminiyarta Ladidi ta kai mata game da  Amarya d'an nata. Ta tabbatar mata tafi Nene tsafta kuma ta ga alama. Sai dai kuma ta kasa fahimtar me ya ja Mati ga aurenta? Wannan abu a dunk'ule haka?
  "Yauwa sannunki kema."
  Ta fad'i tana mai k'arasawa ta zauna a saman tabarmar da aka shimfid'a. Nene za ta yi ciki da kayanta ta yi saurin dakatar da ita.
  "A'a 'yarnan dakata."
Zani na kuncewa tana sake d'aurawa ta karkata k'ugu ta tsaya gami da dire akwatin tana jan majina.
  "Na'am, to."

Inna ta yamutse fuska.
  "Ai kuma sai dai wannan karon ki hak'ura don a d'akin ita 'yar uwarta ki zan sauka. Na gayamaki bana son kwana kan wannan gadon naki mai warin hammatan wanzamai, da kyar idan kin chanja wannan tsohon zanin gadon wanda na gama yayinsa tun jegon mijinki. Ba wa abokiyar zamanki akwatin na ga na ta kamun ludayinta."
  Ai sai Abule ta kece da dariya, kallon banzan da Inna ta watsamata ne ya sanya ta nutsuwa. Nene ta cika ta yi tam! Yau ita Inna za ta ci wa fuska akan Abule? Lallai ya dace ta zage damtse.
  Tana numfarfashi ta zauna, Inna ta dubeta sannan ta k'ara duban Mati.
  "Wai ni Mati wacece me juna biyun a matanka?"
Mati ya hau washe baki.
  "Ai duka biyun ne."
Inna ta kwalalo idanu cike da mamaki tana duban Nene, karshe ta sauke idanunta akan Abule da ta zauna tana wani sussunne kai ita a dole kunya. Sai kuma ta hau tafa hannuwa da shewa.

Farin ciki ya cika su don a zatonsu ta yarda suna da cikin. Sai dai ga Inna kuwa sam zuciyarta ba ta amince Nene na da ciki ba, shekaru nawa da aka yi ta rad'e-rad'in ba ta da mahaifa, ai kuma ta saka ayar tambaya. Dabara ta zo wa Inna.
  "Yau na ga abin al'ajabi, to ai shikenan, zama ya kamani a k'auyen nan duk da ba na so, amma zan zauna har na ga 'ya'yanka Mati."
Hanjin cikin Nene da Abule ya kad'a sai dai kowaccensu ta yi fuska. Mati kuwa wani dad'i ne ya mamaye zuciyarsa ganin burinsa ya kusa cika.
  Abule ke da girki ita ta shiga hidima da Inna, Nene kuwa d'akinta ta fad'a tana tunanin mafita nan gaba.
     ***    ***    ***
  Bayan kwanaki hud'u da zuwan Inna ana zaman lafiya kowacce ta ciki na ciki. Karshe kuma sai Mati ya tsuro da wuni a d'akin Abule wai hira da Inna, haka za ta yi ta tsinkayo dariyarsu.
  Da abin ya isheta ta shirya ta nufi gidan 'Yar Magaji don neman mafita. Tana isa ta zayyanemata komai, 'Yar Magaji ta buga uban tsaki.
  "Ke ce ai ki ka yi sake da ba ki mallake Mati tun fari ba, yanzu da komai zai zo ma ki da sauk'i."
Jin haka Nene ta gyara zama.
"To yanzu ya za'ayi."
'Yar Magaji ta d'an yi jim, sai kuma ta saki dariya ta mik'e ta fad'a d'aka. Can sai ta dawo d'auke da k'ulli ta mik'amata. Nene ta hau jujjuyawa.
"Na menene?"
'Yar Magaji ta d'an murza hanci tsabar warin da bakin Nene yake yi kamar na 'yan ga ruwa.
  "Kinga wannan, k'asar k'ark'ashin gadon ma'auratan da suka tsufa tare ne suna soyayya, matuk'ar kin yi turare da shi na kwanaki uku Mati ya kusanceki to an gama."
Nene ta girgiza kai.
"Matsalar mun fi wata biyar bai nemeni ba, ni kinsan na tsani a maisheni jaka."
Wani kallo 'Yar Magaji ta yi mata sai kuma suka kwashe da dariya 'Yar Magaji na kauda kai.
  "Dad'ina da ke ba dai warin baki ba."
Nene ta muskuta tana shafa bakin.
  "Um to ya na iya da abinda ya fi k'arfin wuta?"
  Ta6e baki 'Yar Magaji ta yi.
  "Ke ki ka so, ni yanzu dai kinsan ina jiran kaso na, makira ai ina shigowa daman na ga yanayinki na gane makircinne ya motsa."
Nene ta dara.
  Suka gama k'ulle-k'ullensu dai Nene ta koma gida da zummar soma gabatar da aiki.

Muna zuwa...