Friday, 20 January 2017

Abin da ake gudu 23

ABINDA AKE GUDU🙆🏽23

Batul Mamman💖


Hanjin cikin Rashida sai da ya kada da Harira ta gama fada mata dalilin zuwansu.
"Bari na kira Baban Abba na fada masa kafin ta karaso gidan nan."

Ta dauko wayarta sai dai tayi ta kira Sada bai dauka ba.

Harira tace "kema Yaya me zaisa ki amince ku ajiye matar da baku sani ba. Wallahi yanzu duniya babu gaskiya."

"Na sani Harira. Sai dai karki manta mu musulmai ne. Idan har zamu biyewa halin mutane yanzu ko sadaka bazamu bayar ba. Kamar yadda Baban Abba ya fada kayi komai saboda Allah. Idan mutum ya cutar da kai yayiwa kansa kuma dama faruwar hakan rubutaccen al'amari ne. Asmau bata da matsala ko kadan,sai kin zauna da ita zaki gane hakan".

Suna hirar Asmau su Abba suka dawo daga makarantar boko. Dama jira tayi su dawo ta basu mukulli ta tafi gidan bikin da su Baaba Ta Annabi zasu je. Yanzu dole ta hakura tunda Yaya Tagwai ta zo gari.

Sai biyar da rabi Yaya Tagwai ta iso gidan tun daga bakin kofa take fada.

Rashida tayi tsuru tsuru da ita har ta shigo ciki. Gaisuwar ta ma bata amsa ba sai fadan rashin hankalinsu da ta gani sun ajiye matar da basu san asalinta ba. Tana wannan fadan Asmau ta shigo a gajiye tana jan kafa saboda tsufan cikinta.

Sallama tayi ta shigo ganin baki ta durkusa da kyar ta gaishe da Yaya Tagwai. Kamar gaske ta saki fuska "maraba da tsintacciyar mage. Babu kunya kike yawo da cikin shege a cikin gari."

Asmau tayi shiru tana kallon Rashida wadda kunya duk ta lullubeta. Rasa abin cewa tayi ita kuwa Yaya Tagwai ta cigaba da magana
"Rashida yanzu wannan mai kwalakwalan idanun kika ajiye a gidanki da sunan taimako. Kina kallon yadda jikinta ya mulmule babu mai cewa daga gidansu ta gudo."

"Yaya Tagwai don Allah kiyi hakuri. Idan kika ji labarin yarinyar nan sai kin tausaya mata. Kaddara ce ta afka mata. Adduarmu Allah Ya kare 'ya'yan musulmi daga fadawa makamancin halin da ta tsinci kanta a dalilin sharrin waya."

Hannu Yaya Tagwai ta kai zata doke Rashida "yi min shiru shashasha. Sai iya bayani rai-rai-rai kamar wata zabiya. Zabgegiyar mace kamar wannan kika sani ko barauniya ce, ko kuma rufeki Sada yayi cikin ma nasa ne".

Kukan da Asmau take yi ta tsayar ta dago kai da sauri tana kallon Yaya Tagwai.
"Wallahi duk abinda na fada ba karya nayi ba. Kuma ban taba ganin Kawu Sada ba sai a garin nan da ya taimake ni. Kiyi hakuri don Allah idan zuwana ya bata miki rai".

Rashida ma hawaye take yi tace "na yarda dake Asmau nasan amana ce a tsakaninmu.
Yaya Tagwai don Allah kiyi hakuri. Da zarar ta haihu zamu mayar da ita gaban iyayenta".

Ta juya wurin Asmau da take ta zubar da hawaye.
"Tashi ki koma dakinki. Bani mukullin Kemis din nasan ya kusa dawowa ya karba."

Su biyun Yaya Tagwai ta ke bi da kallo cike da mamaki." Mukullin wane kemis din ne?"

Rashida tayi shiru ita kuma Asmau ta tashi ta tafi dakinta.

"Nace mukullin wane kemis din ne?"

Rai a bace Rashida tayi mata bayanin tsarin da suke yi na zaman kemis da Sada.

Hannuwa ta shiga tafawa tana salati.
"Aahaf, ni nasan ba a banza ta barku ba. Yanzu hanyar samun naku ma tare kuke yin komai da ita. To na rantse sai ta bar gidan nan ko kunki ko kunso. Bazan koma Misau ba sai naga abinda ya turewa buzu nadi."

Asmau tana daki tana jin fadan Yaya Tagwai da muryar Rashida da Harira suna bata hakuri. Kuka take yi sosai tana cike da fargabar abinda zai faru a gaba.

Har kusan  magariba Sada bai dawo ba. Dole Yaya Tagwai ta tashi ta koma gidan kanwarta saboda idan duhu yayi sosai ba gani take da kyau ba.

Gidan shiru har Sada ya dawo Rashida ta fada masa abinda ke faruwa. Ko zama baiyi ba ya wuce gidansu sai dai shima babu sa'a. Fada yasha sannan tace ya tashi ya bata wuri.

Haka suka kwana gidan kamar babu mutane. Asmau tasha kuka ga wani ciwon kai da ya kama ta.

Da safe Sada ya kirata suka kara kwantar mata da hankali yace zasu je gidan su sake bata hakuri. Har Kawu Usaini sun kira yace yana hanya zai zo a taru a bata baki. Batun zuwa kemis kuwa ranar babu ita.

Adaidaita sahun ya karbo bayan yaran sun tafi makaranta sannan suka fita shi da Rashida da Harira da ta kwana a gidan.

Ba suyi minti biyar da fita ba Yaya Tagwai ta shigo tare da kanin Sada mai suna Habu. Asmau na daki taji sallamarta. A tsorace ta fito ta bude mata kofa ta bata hanya ta wuce.

Yaya Tagwai ta soma kiran Sada, Asmau ta fada mata sun fita.

"To tunda saboda ke dama nazo ki fada min iyakar gaskiyarki. Shin cikin nan na Sada ne ko wani wanda ya sani?

Asmau ta girgiza kai tana hawaye.

"Alhamdulillahi tunda ba cikinsa bane ina so yanzu yanzu kafin su dawo ki fita ki bar gidan nan."

Gwiwa a kasa Asmau ta durkusa tana rokonta. Yaya Tagwai ta dubi Habu
"Kai da nazo da kai meye amfaninka ne? Ja min ita ka datse kofar gidan. Wallahi idan kika sake dawowa gidan nan sai na kirawo miki 'yan sanda. Haka kawai kin tsaface min yara basa jin maganar kowa sai taki. Kin gama karuwancinki zaki nemi bayin Allah ki  hadasu da wahala. In dai cikin nan ba na dana bane to ki kama gabanki".

Asmau tana kuka tace "ki taimakeni don girman Allah. Bani da wurin zuwa idan na tafi."

Yaya Tagwai ta harareta "daga bishiya kika fado da zaki ce baki da wurin zuwa? Tun wuri ki koma gaban iyayenki."

Ta sake cewa Habu yaja Asmau sai ya kasa saboda tausayinta da yaji. Yaya Tagwai tace
"Idan baki fita ba zan sa iyayensu su zare hannuwansu daga kansu. Idan baki sani ba ina so kisan cewa ina da wannan ikon da kannena".

Jin haka Asmau ta juya zata shiga dakin ta debo 'yan kayanta. Yaya Tagwai ta tsare kofar dakin. "Bazan bari ki sake shiga ba bare ki kunna wani tsafin nima naji ina sonki. Fita tun kafin nayi yekuwa a unguwar nan nace ke mayya ce".

Habu ma sai da yasa baki akan ta bari ta dauko kayanta amma taki. Haka ta ja hannun Asmau daga ita sai kayan jikinta Allah Yasa da mayafi tayi waje da ita ko takalmi babu. Kuka take yi sosai amma a haka Yaya Tagwai ta ja hannunta har suka bar layin. Sai da suka yi nisa ta jefa mata naira dari biyu.
"Matsiyaciya sai ki dauka ki kara gaba wasu masu tsautsayin su dauke ki amma ba gidan 'ya'yana ba. Allah Ya isa idan  kika dawo."

Kukan Asmau ba karamin tausayi ya bawa Habu ba amma yana kallo tayi gaba Yaya Tagwai ta kama hannunsa suka koma gidan Sada.

*****
A gidansu Sada ne Baaba Ta Annabi ta fada musu tun dazu Yaya Tagwai ta tafi gidan nasu. Suna jin haka suka kama hanyar gida hankali a tashe. Suka yi rashin sa'a titin da ya biyo wata mota ta lalace ta hada uban goslow.

Kusan tsalle Rashida tayi da suka iso gida ta fito daga dan sahun. Tana shiga ta tarar da Yaya Tagwai tana yin boli boli da kayan Asmau. Kuka ta saka tana tambayarta ina take Habu yace ta tafi.

Sada na jin haka cikin fada ya tambaye shi hanyar da tabi ya kwatanta masa. Tare suka bi hanyar ko zasuyi sa'ar ganinta. Sai dai sunfi awa biyu suna nema daga baya wani yace ta shiga wata bus amma bai san inda bus din tayi ba.

Da suka dawo gida Rashida ya gani a tsakar gidan ta rungume kayan jariran da Asmau take tarawa tana ta kuka. Yaya Tagwai tace "idan kin gaji kya yi shiru. Irin wannan kuka da kike yi sannan ace ba aikin asiri bane."

Ayatul Kursiyyu ta shiga karantawa tana tofawa Rashida a ka wai maganin sihiri. Sada ya dagata ya shigar da ita daki tana ta kuka. Habu da Harira kuwa sai kallo. Yaya Tagwai ko a jikinta. Tasan komai daren dadewa zasuyi mata godiya saboda ta rabasu da masifa.

*****
Yaya Babba ke bacci harda minshari Zubaida ta samu ta lallaba da kyar ta fito daga gidan.

A iya watannin da tayi duk shegantakar karuwanci 'yar tsohuwar nan ta koya mata. Tun tana nuna bata so har ta hakura tana biye mata saboda a rage matakan tsaron da aka saka mata. Bata taba yarda wani yayi amfani da ita ba. Tace sai ta koma gidan Uwargida. Yaya Babba bata damu ba ita dai aikin da aka sakata tayi.

Tunda tazo gidan sai yau ta samu damar fita. Kullum tana tunanin Asmau. Bata sani ba ko ta haihu yanzu.

Gidan Uwargida ta tafi da niyyar idan Asmau tana nan su gudu tare. Daga bakin kofa ta hadu da wata cikin matan gidan.

"Zuby kin dawo?" Ta fada tana kallon irin shigar Zubaidan da yadda ta kara cikowa.

Zubaida ta rage murya
"Shiga ki kirawo min Asmau bakuwar nan. Don Allah kiyi sauri ga wannan kada ki fadawa Mama kin ganni." Dari biyar ta bawa matar ta karba sannan tace "wannan bakuwar baki dade da tafiya ba ta gudu. Har an sami wasu bakin biyu bayan tafiyarta."

Zubaida tayi wani murmushi cike da jindadi."Alhamdulillah nasan taji shawarata ta koma gidansu."

Daga nan ta dauki jakar kayanta ta juya ita ma. Matar ta biyota tana tambayar ina zata je Zubaida tayi gaba ko kulata bata yi ba.

Daga nan bata zame ko ina ba sai tasha ta nemi motar Kano. Basu dade ba motar ta cika suka hau titi. Indai bata manta ba Asmau tace sunan umguwarsu Hotoro layin kwamishina Adamu. Gidansu zata nema don tasan in Allah Yaso yadda Asmau ke bata labarin Umma zasu riketa har ta sami mijin aure. Ta dan yi murmushi "ko me Asmau ta haifa" ko meye ma zata tayata raino tunda dai taji shawararta ta koma gida. Allah Yasa dai ta gane gidan.

Thursday, 19 January 2017

Silar Ajali 4

Alkalamin Safiyyah Ummu-Abdoul

Babi Na Hudu

Hankalin Goggo ya kai kololuwa wajen tashi,  juyi take kan gado idanunta babu ko alamun barci.  Ta saka wannan ta kwance,  duk hankalin ta bai kawo mata mafita ba. A iya sanin ta ba za ta yarda a kai jininta gidan marayu ba amma kuma in aka kore ta ina zata nufa da yara ita ba wata sana'a take kwakkwara ba.  Haka dai ta kasance har sai da kiran assalatu ya fargar da ita lokacin da ta Share kwance.
   Tashin Salma da ke kwance a gefen ta ya dawo mata da dukkan bakin cikin da take tunanin babu a lokacin.  Kallon ta tayi,  ta gama addu'ar tashi da ga barci ta Mike nan take wata irin tsanarta ta dake ta,  "yanzu ita ma ɗin  ba tsira tayi ba da ga jan abin kunya,  mata ko tsiya"  ta faɗi a ranta.

"kawai ki ba da ita a gidan marayu ki huta da abin bakin cikin da zata iya Kwaso miki" wani sashi na zuciyar ta ke shawartan ta,  kafin ta kai ga amincewa Ɗayan sashin tace da ita

"Me zaki ce da Allah yayin da ya tambaye ki dangane da amanar kiwon da ya baki.  Ki haɗe su ki rike duk rikicin da za'a yi" batai wata wata ba ta amince da shawarar.  Da wannan karfin gwiwa ta tashi ta ɗauro alwala ta gabatar da sallan asuba.

                      ***
Ko da hakimi ya isa gida ya taradda hajiya Aziza a turakansa.  Sanye take da rigar barci doguwa,  kanta babu ɗankwali kitsonta ya kwanta gunin sha'awa,  nan take ya fara jin abu tun daga tafin kafarsa har kwanya.  Zuciyarsa na kara narke mata,  "Daɗi na da ke kenan sanin ciwon kai"  ya faɗi a ransa bai tsaya ɓata lokaci ba ya dumfare ta ya rungumo.

"Kinyi kyau hajiya ta,  always looking sweet my dearest " ya faɗi a saitin kunnen ta,  nan take abubuwa suka dawo masu a rai,  rayuwar su na jin Daɗi sanda yake aiki karkashin mahaifinta.

" tunanin me kake yi bayan ga azizarka a tare da kai? " ta  faɗi tana dariya kasa kasa.

" Tunawa nayi da kuruciyar mu,  hakika da duk haka mata suke da sai in ce ba za'a samu yawan mace macen aure ba ko zaman ukuba a aure,  Allah ya sada ki da aljanna yanda kika zama sanadin wayar dani cewa mata ma mutane ne da suke da hakki a aure kamar maza"  ya faɗi yana shafo  kitso ta.

"ai da sauran ka yallaɓai,  ba zamu gaji da magana ba don muna fatan samun nasara da canji yayin magana,  wasu na tsoron saki sai suka ki magana hakan ya sa suke zaune cikin ukuba"

"Maama  me yayi saura bayan ina iya kokari wajen ganin na kyautata muku.  Ko halinku na yan boko zaki nuna min. " ya karasa yana murmushi don ya san abin da ya tono.

" Ai tsiyar yan Afirka kenan,  ba  dama ace kar a muzguna ma mace sai kuce boko,  alhali musulunci ya koyar da mu haka.  Zancen yaran RAHANATU ne,  shin da ace Batul ce ta wajen mu wannan al'amari ya same ta haka zaka aiwatar?  Dazu na ji zancen ku da wancan jahilin,  wanda ya ki karatun arabi balle a sa ran zai yi boko.  Wallahi kuna kai yaran nan gidan marayu zan haɗa ku da hukuma.  Sannan ka san cewa na bar gidan nan kenan"

"tsaya Azizah,  kin sha wani abin ne da daddaren nan da zaki haɗa Batul da Rahane,  bazan taɓa haɗa jini da shegu ba don ni tsarkakakke ne haka duka mata na" ya faɗi yana kumfar  baki.  Sanin da tayi zai ji haushi sai ta saki ranta ta yi dariya sannan tace

"Meye bambanci tsakanin su biyun? Duk su biyu yaranka ne ko Kaki ko kaso,  sannan ai ita dole aka mata,  amma ina ce nan ka sa Sanah komawa gidan Nasiru Nasiru,  duk da cewa da ake ɗan luwaɗi ne?  Da wanda aka ma fyaɗe da wanda ke aikata luwaɗi Wanne ya fi?  Sannan ita dai aure tayi ta haife su,  ga yarka chan ka Barta a auren da wuta zai kaita saboda tsinuwar Allah da yake kansu. Duk mijin da yayi luwaɗi ai zai yi da matarsa"  nan hakimi ya cika yana batsewa.

"ke dai baki da magana sai ta saki,  yanzu duk kokarin amso taimako da nake yi daga wajen malamai baki gani ba,  mai gani har hanji yace ayi hakuri zai daina" ya faɗi a iya kan gaskiyarsa kenan.

"tab,  ga shirka ga luɗu Allah ya shirye ku.  Duk auren da zai kai mace ko yan uwanta gidan boka Wallahi  ba aure bane.  Ni dai na gama magana kuka kuskura kuka kori yaran nan Wallahi hukuma zasu shigo ciki.  Haba Allah ya ɗaura muku hakki ku nemi watsarwa,  na barka lafiya" ta tashi ta barshi zaune.  Ta san ba zai juri fushinta ba shi yasa ba ta kyashin nuna fushinta a kansa.

                               ***

Tun da ta tafi yake tunanin abin da ya faru da yar sa Sanah.

SATI BIYU  DA SUKA GABATA

Ya shigo gida ya iske yarsa da ke aure a ɗan Musa ta dawo gida.  Da fari yayi tunanin ziyara ta kawo masu sai da Hajiya Aziza ta masa bayanin kara Sanah ta kawo.

"Kowa fa hakuri yake a gidan miji shin ba zaku faɗa mata hakan ba,  ni ba abin da zan ce illa kar ta soma kashe aurenta.  Uwar ta ma hakuri take da ni" ya fadi a fusace,  nan take ta mayar masa da cewa

"neman ta fa yake ta baya, sannan kace kar ta dawo,  cewa a kayi in an aurar da mace Shike nan bata da hakki akan ubanta ?  Ko mai kake nufi "?

" Akan ta aka fara auren ɗan luwaɗi ko cewa akai su sauran basu da mata,  kar ki kashe mata aure ko don ba ke kika haife ta ba" ya bata amsa

"don ba ni na haife taba sai in bari tayi ta kwasar tsinuwar Allah da sunan aure,  aure fa ibada ce,  kuma ibada sai da biyayya ga Allah ba saɓon sa ba. Haba" tana gama faɗi ta barshi a zaune.

Haka tana kuka da magiya ya tasa keyarta har zuwa dakin ta.  Ta kira shi sau biyu tana rokon sa shi kuma yai mirsisi ,  chan ne abokin sa ya shawarce shi da su nema mata taimako daga malamai.

Da tunanin nan barci mai nauyi yai gaba da shi har sai da aka kira assalatu sannan ya tashi yai harama.

Abin da ake gudu 22

ABINDA AKE GUDU🙆🏽22

Batul Mamman💖


Zahra 'yar Rabe ta biyu ke zaune tana waya da mahaifiyarta Laraba wadda Raben ya dade da saki. A hirarsu ne take fadawa Laraban zancen haihuwar Shema'u wadda akayi kwanaki goma da suka wuce. Tun ranar da akayi haihuwar Yassar yazo ya sanar sai akayi rashin sa'a Rabe da Zahran ne kadai a falon. A wurin ya ci mutumcin  Yassar  sannan yace da Zahra kada ta fadawa Hajjo babu mai sake zuwa gidan Bara'atu.

Laraba duk ta gama sauraren 'yarta tace mata su kara hakuri da babansu. Dama ita ta bata shawarar dagewa taje bikin Asmau. Tace idan ta shigo Kano zata zo tayiwa Umma jajen abinda ya sami Asmau da barkar Shema'u.

Hajjo tana tsaye a bakin kofa ta fahimci duk hirar Zahra da Laraba. Ko kwanaki uku da suka wuce sai da ta cewa Rabe wai har yanzu Shema'u bata haihu bane yace wa ya sani ne. Bara'atu da bakin hali kuma. Ta rasa gane irin wannan tsana da yake nunawa iyalin dan uwansa.

Dakinta ta koma jiki a sanyaye ta dauko mayafi ta fito. Karnukan Garzali ne suka yo kanta ba shiri ta koma ciki. Dakinsa ta je yana bacci ta daka masa duka a baya. Shi babu arabi babu boko sannan auren ma ya gagara. Sai dai yaje yawo ya dawo gida ya kwanta bacci.

A zabure ya bude ido ganin wace ke kansa ya turo baki "haba Hajjo yau kuma me nayi zaki doke ni? Na rantse jiya ban sha komai ba. Sansana bakina kiji".

Ta kau da fuska "Allah Ya tsareni na kai hancina bakinka. Ni tashi ka daure karnukan ka fita zanyi. Ka mayar mana da gida kamar dandalin 'yan daba. Motsi kadan sai haushin karnuka."

Dariya yayi tare da zuro kafafunsa zai sauko daga kan gadon. Daga bayanta taji ance "ina zaki je?"

Gabanta sai da ya fadi don firgici ta juya tana kallon Rabe wanda bata san ya dawo gida ba. Murmushin da bai kai zuci ba ta kakalo
"Yaushe ka dawo Alhaji?"

Ya basar da tambayar. "Naji kina cewa zaki fita".

Kamar ba mahaifiyarsa ba duk ta kidime tace "uhmm dama gidan waccan mara kunyar zani. Ashe Shema'u ta haihu shine ko ta aiko mana. Ai bata isa ta rabamu da 'ya'yan Shuaibu ba ko?"

Rabe ya soma jin tsoron yawan ambaton su Bara'atu da take a kwanakin nan sai ya dan dake.
"Yanzu a kanta zaki fita cikin ranar nan? Ki kyaleta kawai da halinta. A ce har 'yar dan uwana ta haihu bamu ji ba kawai don bata daukemu a bakin komai ba. Ni daga yanzu na kafa doka babu mu babu su. Tunda haka ta zaba kowa yayi ta kansa."

Hajjo ta jinjina kai tama mamakin yadda yake gilla mata karya haka. Ta tabbatar maganar da Zahra keyi a waya ba karya bane. Ta sake gwada sa'arta ta hanyar cewa
"Wai dama nace muje ko tare da kai ne mu dan zagesu mu huce haushi"

Juyawarsa yayi don kada ta sake jan zancen.
" Koma daki kiyi kwanciyarki ki huta Hajjo".

Tana kallo ya tafi itama ta juya zata koma dakinta. Hawaye ne ya sauko mata wanda bata san dalilinsa ba ta goge da habar zaninta sannan ta koma daki.

Garzali da bai tanka musu ba yaji tausayin mahaifiyarsa ya ratsa shi. Ya rasa dalilin da yasa dukkansu har Yaya Abu da Yaya Lami basu da katabus sai abinda Rabe yace. Amma zaiyi kokari ko yaya ya kai Hajjo taga jikokinta tunda wulakancin da suke musu yasa suka dena zuwa gidan.

A daki Rabe ya kasa sukuni. Sagira na masa magana ya daka mata tsawa. Dama ba wani matsayi gareta a wurinsa ba. A duniya babu matar da yake matukar so kamar Bara'atu duk da girma ya kamasu. Sai kuma batun Malamin tsibbunsa. Dama lokaci lokaci yake sake biya a toshe bakin Hajjo da 'yan uwansa. Yanzu idan asirin ya karya yasan Hajjo cewa zata yi su tashi daga gidan Bara'atu ta dawo. Matsalar idan suka tashi basu da wurin zuwa. Ya riga ya sayar da gidansu na kofar mazugal ya mutstsike kudin batare da sannin kowa ba.
*****

Baaba Ta Annabi tana zaune kofar wurin girki tana tsintar wake taji sallamar yayarta Hassana wadda suke kira da Yaya Tagwai. Farantin waken ta ajiye ta tarbo su cikin farinciki.

Ta Annabi ta kalli 'yar daya yayan nata Usaini tace "auta ba kya laifi kullum kina kuturin Yaya Tagwai. Naga alama idan anyi bikinki  tare za'a kaiku."

Yaya Tagwai tayi murmushi tana kallon Harira autar dan uwanta . Ita Allah bai bata haihuwa ba shine ya bata Harira take ruko duk da a gida daya ma suke da zama.

Tabarma Ta Annabi ta dauko Harira ta shimfida musu suka zauna aka gaisa. Ta tambayesu ya suka baro mutanen Misau.

Sai da suka ci abinci ne Yaya Tagwai tace ina sauran yaran gidan. Ta Annabi ta fada mata sunje biki ne a dangin Babansu. Ita ma girki zata karasa ta tafi.

Yaya Tagwai tace " gara da nayi sa'ar ganinki. Ke Harira tashi ki tafi gidan yayarki kafin nazo na sameta ita ma."

Fitar Harira ke da wuya Yaya Tagwai ta kalli kanwarta rai a bace "kin kyauta Ta Annabi, wato don ni ban haihu ba shine kika kira Usani kina sanar dashi katobarar da 'ya'yanku suka yi. Allah Yasa ina labe a bakin kofa naji duk abinda kika fadawa Ado ya sanar dashi. Don shashanci sai ji nayi yana sanya musu albarka. Sai da na kare masa tanadi na taho. Duk tsiyarku nice babba dole kuyi yadda nake so daga ku har 'ya'yan naku."

Ta Annabi ta dukar da kanta. Yaya Tagwai akwai rikon zumunci sai dai bata da hakuri. Hakuri ta bata sannan tayi mata bayanin yarinyar da Sada da Rashida suke riko.

Sada da Rashida auren zumunci suka yi. Shi Sada dan Ta Annabi ne ita kuma Rashida 'yar Kawu Usaini. Tun farkon zuwan Asmau yayiwa mahaifiyarsa bayani a kanta kuma ta nuna amincewarta. Daga baya ne ta yanke shawarar sanar da Usaini don yasan me yake faruwa.

Bayan ta gama bayanin Yaya Tagwai taja dogon tsaki.
"Ina tsammani yarinyar dai da asirinta tazo gidan. Idan ba haka ba waye zai ajiye mace mai ciki a gidansa ba dangin Iya ba na Baba. Ni zanje gidan na same su. Lallai ne su koreta ko don tsare lafiyarsu da ta yaransu. Wa ya sani ma ko mayya ce ko kuma duk abinda ta fada musu karya ne."

Abin da ake gudu 21

ABINDA AKE GUDU🙆🏽21

Batul Mamman💖


Sunyi tafiya ta kusan rabin awa kafin su isa gidan. Dan matsakaicin gida ne mai kofa daya. Idan ka shiga siririn soron akwai kofar daki a wurin sai kuma daga gaba ainihin kofar gidan. Tsakar gida ce mai dan fadi da dakuna uku, bandaki da kitchen.

Daya daga cikin kofofin Rashida ta bude suka shiga tana nishi da kyar. Asmau dake tsaya tana jiran su bata izinin shiga taji Rashida na cewa mijinta " gaskiya Baban Abba kana kokari yin tafiyar nan kullum. Kodayake kiba kake son ragewa" ta kare tana dariya.

Labulen kofar ta makale a jikin kofa sannan tace Asmau ta shigo falon. Da sallama ta shiga tana ta addua a zuciyarta ta sami wuri akan ledar falon ta zauna.

Sada ya zauna kusa da matarsa a kan kujera yana dubanta.
"Nan shine gidana kuma kamar yadda na fada miki wannan matata ce. Muna da yara hudu duk maza suna makaranta yanzu. Abba, Abdul, Ahmad da Amir. Mu dai har ga Allah bamu da niyyar cutar dake ina fata kema haka abin yake a zuciyarki. Yanzu al'amarin Dan Adam sai addua. Da mai taimako da mai neman taimako kowa yana tsoron dan uwansa. Idan kin amince zamu zauna dake har ki haihu in Allah Ya yarda sai muyi miki jagora zuwa wurin iyayenki. Na tabbata a lokacin zasu hakura tunda kin haihu babu mai zubar miki da ciki."

Asmau tayi musu godiya sosai tana share hawaye. Bazata taba mantawa da mutanen nan ba a rayuwarta. Dakin soron Rashida ta kaita tace ta jira tana zuwa.

Wurin mijinta ta koma ta kai masa ruwa da abincin da baici a shago ba sannan ta koma bakin rijiyarsu ta janyo ruwa har bokiti uku. Katuwar tukunya ta dorawa Asmau ruwan wanka sannan ta kai mata abinci. Ta karba tana ci Rashida ta dauko tsintsiya ta share dakin tas ta dauko daya daga cikin karifar yaranta ta shimfida mata. Asmau dai sai godiya.

Bayan Sada ya koma kemis dinsa Rashida ta kira Asmau ta bata sabulu da soso tace taje tayi wanka. Sai da ta fara wanke kayanta wanda suka kusa karar da ruwan sannan tayi wanka da wankin kai. A take taji ta zama kamar wata sabuwar mutum. Da ta fito Rashida ta bata riga da zani ta saka. Da kuka ta rinka yiwa Rashidan godiya.

Da yaran suka dawo daga makaranta aka gabatar musu da ita a matsayin 'yar uwarsu. Abba ya kare mata kallo ya dubi mamansa "Mama wannan tayi kama da almajirar da Baba ya siyawa awara rannan."

"Kul na sake jin kalmar almajirar nan Abba. Sunanta Anti Asmau kunji ko" yaran suka amsa sannan duk suka gaisheta cike da ladabi.

Da daddare bayan Sada ya dawo ta fada musu tana son dauko kayanta daga gidan Uwargida. Yace bai amince ba, tunda Allah Ya rabata da gidan kin komawarta shine mafi alkhairi.

Rashida tace "zan duba miki wasu cikin nawa kayan sai kiyi amfani dasu zuwa lokacin da zamu ga abinda Allah Ya nufa."

Washegari Sada da kansa yaje gidan Uwargida don tabbatar da zancen Asmau ya nuna kamar haduwa yayi da ita kuma yana sonta. Daga kwatancen da yayi Uwargida ta gane wa yake nufi tace masa ya dawo washegari tun jiya bata ga 'Yar Da6as ba. A ransa yace kuma bazaki kara ganinta ba.

Cikin kwanaki kadan Asmau ta saba dasu Abba sosai ta dan murmure. Tana fitowa ta taya Rashida ayyukan gida musamman wanke wanke da shara. Da ta gama take komawa daki don kunya take ji ace ta saki jiki sosai ita da ake yiwa alfarma. A nata bangaren Rashida kullum kokarin jan Asmau take yi a jiki saboda nutsuwarta. Har mamaki take yi yadda irin wannan azal ta fada mata. Sai kuma ta tuna babu abin mamaki a rayuwar duniya.
*****

Haka rayuwar Asmau ta cigaba da tafiya tare da wadannan bayin Allah. Zama suke yi na amana kullum tana addua Allah Yasa kada su gaji da ita su koreta wata rana.

Tsakaninta da Sada baya wuce sannu da zuwa, ina kwana ko ina wuni. Wannan yasa Rashida take kara janta a jiki. Don kuwa babu wadda zata so daga taimako taga ana shigewa mijinta. Shima da yake mutum ne mara hayaniya ba shiga sabgarta yake yi ba.

Tayi kimanin sati uku a gidan rannan an kawo wuta Rashida ta tura Amir ya kirawo Asmau tazo suyi kallo. Tana daki tana aikin tunanin rayuwarta taji sakon ta tashi.

Sallama tayi Rashida ta amsa tana murmushi.
"Asmau wai ke haka kike ne da wuyar sabo, uhmm? Kullum sai na aika an kiraki zaki fito muyi hira. Zaman dakin da tunani sai ya haifar miki da matsala ko da babu ciki kuwa."

Ita ma Asmaun murmushi tayi kanta a kasa "kiyi hakuri Antina, in sha Allah zan dena."

"Zaki dena, ba ki dena din ba kenan".

Suka yi dariya su biyun sannan Abba ya kunna tv din suna kallon fim din Zinaru suna dariya.

Sai da fim din ya kare Asmau ta dan karkata tana kallon Rashida.
"Anti dama wata alfarma nake nema amma don Allah idan kinji abin baiyi miki ba kiyi hakuri."

Rashida ta juya ta kalli yaranta. Ba tare da tayi magana ba duk suka fice sannan ta mayar da hankalinta ga Asmau.
"Ina jinki kanwata"

"Anti dama shawara nake da ita idan babu damuwa. Na kula Kawu Sada yana zuwa wani aikin bayan ya taso daga kemis dinsa. Kamar yadda na fada muku na kusa gama aji uku a jamia kuma pharmacy (hada magunguna a kimiyance) nake karantawa. Nayi tunanin ko zai nuna min yadda yake a kemis din na rinka taimakawa da zaman wurin idan yana wani aikin."

Shiru Rashida tayi na dan lokaci tana tunani. Ban da kemis Sada yana 'yan buge buge irin na maza don dai a cigaba da samu. Hakan yasa baya samun zama a kemis sosai. Wani lokacin tun karfe takwas yake rufewa. Tayi masa magana akan ya koyawa Abba yace so yake suyi karatu tukunna. Ta numfasa "bari ya dawo muji ta bakinsa. Amma kin kawo shawara mai kyau. Sai dai ya zakiyi ga ciki ya fara girma?"

Asmau tayi farinciki da Rashida bata yi mata mummunar fahimta ba tace "zama wuri dayan ma yana da illa. Idan na samu ina fita sai naji dadin jikina".

Yau tun bayan magariba Sada ya dawo. Ya ci abinci yake sanar da Rashida ya samu za'a rinka bashi hayar adaidaita sahu daga karfe shida zuwa shadayan dare. Saboda haka yanzu da wuri zai rinka dawowa.

Tana jin haka ta fada masa yadda suka yi da Asmau. Yace ta kirawota suyi magana.

A kasa ta zauna ta gaishe shi yace "Yanzu nake jin shawarar da kuka yi da Rashida. Kina ganin babu matsala ga ciki?"

"In sha Allah babu in dai kun amince".

Ya dubi Rashida "ina ganin hakan wani taimako ne daga Allah. Zan nemi a canja tsarin hayar dan sahun. Yadda ita sai taje da safe zuwa shidan ni kuma naje zuwa shadayan dare."

Asmau tayi musu godiya har zata tashi Sada ya dakatar da ita ya tambayeta nawa zai rinka bata a wata.

Zaro ido tayi "Allah Ya kiyaye na karbi kudi. Matsayinku a gareni ya wuce hakan. Kun bani wurin kwana da abinci duk da ina halin da duniya zata kyamace ni. Irin tawa gudummawar kenan gareku ba don na biya kyautatawarku ba. Wannan Allah ne kadai Yasan ladanku" da kuka ta karashe maganar.

Sada yaji dadi yace ta tafi zasuyi shawara da Rashida amma dole a bata wani abin.

Bayan fitarta Rashida tace "kaga ikon Allah ko. Sai Ya kawo maka taimako idan ka taimaki bawanSa. Yanzu sai kayi aikin cikin kwanciyar hankali kafin ta haihu."

"Haka ne amma ya kamata kafin ta fara zuwa kuje asibiti a duba ta duk da naga bata damu da cikin ba."

Dariya Rashida tayi "da kenan Baban Abba. Yanzu idan muna hira zance kadan sai ta sako abinda ke cikinta. Har hira nake ji tana yi a daki da shi tana fada masa tana sonsa."

Sada yayi murmushi "gara ta so shi domin da yawa matan dake yin ciki a waje idan sun haihu sai tsanar dan ta biyo baya ko su yar. Karshe yaro ya tashi babu tausayi ko imani a zuciyarsa."

*****
Bayan kwana uku Asmau ta fara bin Sada kemis dinsa. Sunje asibiti an bata magunguna irin na masu ciki sannan ance ta rage tunani saboda jininta ya dan hau.

Cikin ikon Allah bata dade ba ta gane kan aikin ta rike kudin kayan shagon, magungunan da lemo. Allura ce kawai bata yi sai tace mutum ya dawo karfe bakwai lokacin Sada ne a wurin.

Duk iya bincikensa ya duba bai samu tana ha'intarsa ba. Komai aka siya sai ta rubuta sannan kafin ta tashi zata yi lissafi ta ajiye masa kudin. A wannan lokacin kam sun sami budi sosai ga kemis ga adaidaida sahu.

*****
Mama da Umma kamar basu sami sabani ba don tuni Mama ta amince da zancen Qasim na cikin  Asmau. Su biyu ke kai kawo a asibiti suna jiran Shemau ta haihu. Mijinta ya tafi dauko kayan haihuwar da suka manta a gida saboda sun fito a gigice.

Nurse ta fito ta sanar dasu ta sauka lafiya an sami da namiji. Bakin Umma da Mama yaki rufuwa don tsabar farinciki sai yiwa juna barka suke yi.

Suna dakin maijegon Zubair mijinta ya dawo. Yana ta murmushi ya dauki dansa yayi masa huduba sannan ya mikawa Mama yace "Allah Ya raya mana Abubakar Saddiq".

A take hawaye ya sauko mata ta kalle shi ta kalli Umma. Ita ma Umman har Shemau hawayen suke yi tace "Allah Ya raya shi bisa sunnah. Mungode sosai Zubair."

Mama ta share hawaye "A lokacin da ko 'yan uwansa babu lallai su sakawa 'ya'yansu sunansa saboda ya mutu ya bar baya da kura shine kayi mana wannan karamcin. Me zance maka Zubairu."

"Mama so nake ku dena tada hankulanku. A rayuwa kowane mutum da irin kaddararsa. Kuma haka ke sawa mu kara imani da sanin cewa ba wayonmu ko ilimi ne yake karemu ba. Rahma ce kawai daga Allah da ibada da kuma tawakkali ."

Shemau tace "mungode Abban Mimi. Allah Ya jikan Yaya Abubakar".
Duk suka ce Amin.
*****
Da taimakon Alh Adamu, Qasim ya tura hotunan Asmau ofisoshin 'yan sanda da yawa ana cigiyarta ko wanda ya ganta.

Abdulhalim kuma ya baza a gidajen rediyo da talabijin. Duk inda suka ji kishin kishin da gaggawa suke zuwa ko za'a dace. DPO din division din da Qasim yake a Zamfara shima ya taimaka ta hanyar dagawa Qasim din kafa a duk inda suke tunanin za'a sameta yana bashi izinin zuwa.
*****

Watanni sun shude cikin Asmau ya kusa kaiwa lokacin haihuwa. Dan kudin da Sada yake bata duk da yace ba albashi bane dashi take siyan dan abinda ba'a rasa ba na jarirai. Kunya tasa take boyesu kada ace tana yiwa dan da bashi da uba siyayya. Sada yace ta dena zuwa kemis din haka tace zata iya tare da alkawarin duk ranar da taji alamun ciwo zata hakura.

Wednesday, 18 January 2017

Silar Ajali 3

Alkalamin Safiyyah Ummu-Abdoul

Babi na uku

Ko da suka isa gida,  Goggo ta fara haraman ɗaura abincin rana,  yayin da Salmah ke manne da ita

"oh ni Salame,  se kace wata kaska ina ɗaga kafa kina saukewa,  ki je cikin yan uwanki ki zauna" ta faɗi sa'ilin da ta bita zuwa madafa.

"zan tayaki ne fa Goggo,  na iya Girki ina ma innarmu a kano" ta faɗa cikin murmushi yayin da Goggo ta saki baki tana kallon ta galala.

"Ita Aminar ce ke saka ki Girki? " ta tambaya tana mai kallon idon ta don ta ga iya gaskiyar ta.

" a'a muna taya ta ne dai,  a haka har muka koya,  ranar da na fara yin tuwo ko Goggo,  rabin sa gari ne,  ranar baba sai da ya make ni wai na faye rawar kai" da fari tana maganar tana dariya ne sai da ta ambaci sunan baba ta gimtse fuska tunawa da tayi da abin da ya baro su. 

"Oh ni salame,  ko dai Almatsutsai gare ki ne,  ana raha sai ki gimtse fuska,  ko dai Kanon zaki koma mu huta" Ta ce tana lakuto mata haɓarta.  Dariya kawai Salma tayi ta watsake. 

A haka suka kammala abincin su na rana,  suka ci bayan sauke farali ɗaukan su tayi zuwa makarantar islamiyya da ke bayan Layin su.

Bayan gwajin da aka yi musu nan aka sa Salman a aji huɗu,  Salma aji uku suhayl kuma rabin aji. Goggo bata tafi ba har sai da ta amshi takardar shiga sashin hadda tare da alkawarin zasu fara zuwa ranar Alhamis kasancewar sashin na karatu ne ranakun Alhamis zuwa Lahadi.

Sun shiga azuzuwan su ana darasi na biyu.  Salma ta iske malamin fiqhu na karantarwa. Nan ta iske kujerar farko a gefen mata da mutane uku ta zauna cikon na ukunsu,  ta natsu tana sauraran karatun.

  "Assalamu Alaikunna, kaif"  ta ce dasu bayan malamin ya fita.

Sai da suka kalli juna sannan suka amsa da "Waalaikumus salam wa Rahmatullah wa barakatuh".

"ismie Salmah Aarif " ta faɗi tana mika musu hannu.

" Rufy kiyi shiru in ansa,  kar ta raina mana wayau,  don ma jiddo bata zo ba da ita zata yare mana ita" cewan ɗaya daga cikin su,

Dariya ya kucce ma Salmah,  ita dama tsoronta irin islamiyyarsu ta Saudiyya ce da ba'a wani yare sai larabci duk da kasancewar suna yankin da mafi akasari bakaken fata ne.

"Wacece Jiddan Halan,  don Wallahi kun bani dariya,  ni fa na sha ba'a wani yare sai zallar larabci ne fa" ta karasa tana dariya.  Nan duk sai suka haɗu suna tuntsira dariya kamar wasu sabbin kamu.

"wai tsaya,  Salma wai dama kin iya hausa ne kike yare mu,  har da wani Alaikunna " faɗin mai kiran Rufy nan suka kara sakin wani dariya.

" Ai Barta Ummita da fari na aza fa bata iya ba,  sai da na ga ta kara karya harshe na ga ai ko da Larabawa take kama" inji  Rufy.  Suna tsaka da dariya wani malamin ya shigo,  suka yi tsit kamar ba su ba har sai da aka kaɗa tashi.

Nan ne Ummita ta haye samar tebur ta ce

"ga bakuwa an kawo muku a aji,  mu dai gare mu ba bakuwa bace don yar wata Goggonmu ce,  balarabiya ce kuma,  ba ma son shisshigi da neman es,  ehe"

"kuma Sunanta Salma Baralabiya,  saura su wa'e su turo wasika Wallahi abinda muka yi lokacin jiddo kaɗan ne akan wanda za muyi ma Salmah" Rufaida ta amshe,  nan suka tafa suna tuntsire da sabuwar dariya.

Mamakinsu ya cika Salma,  duk da tana da tsokana tun tasowarta amma zaman gidan inna ya sa duk ta daina saboda rashin sakewa Matukar baba na gida. 

A bakin kofar makaranta ta haɗu da Salman da Suhayl nan ta gabatar masa da Kawayenta suka yi gaba yan mazan na biye da su a baya.

A hanya take tambayarsu gidan su sai suka faɗa mata Mahaifin Rufaida  yayan Ummita ne, ita kuma jiddo yar kanwar mahaifiyar Rufaida ce.  Ummita ta kara da cewa "ke kuma daga yau yar Goggo na ce. Duk da kuwa Goggo salame kawar kishiyar Mamana ce. Kinga ke ma ya ta ce"  nan Rufy ta kai mata duka ta ce

"sai aukin son girma amma duk mun girme ki"

Nan fa Ummita ta kumbura tana shirin yin rigima sai da Salman ya shiga tsakani sannan ta yi gaba ta Barsu a baya. Su kuma suna ta mata dariya har suka kai kwanar da ta raba su,  duk suka yi hanyar gidajensu.

"Assalamu Alaikum Goggo na" ta faɗi tun daga bakin kofa,  Ras!  Ta ji gabanta ya faɗi don bata san irin tarbon da zata samu daga Goggo ba.

"Waalaikumus salam yaran albarka,  ina suhayl ya karatun zo ka faɗa min mai gidana" ta  ce tana gwasale Salma.  Bayan sun gaishe ta ne take tambayarsu karatun su,  sannan suka yi alwala don gabatar da sallan magrib.

Bayan sallan isha'i ne suka taru don cin abinci.  Suna tsaka da ci ne aka yo sallama,  ashe Kanin Goggo ne da yayanta hakimi. Nan aka sake sabon gaisuwa,  su Salma na shirin tashi suka zaunar da su

  "abin da ya sa muka yo takakkiya ba komai bane sai zancen yaran nan,  mun tattauna da Yaya ga shi nan ni ban goyi bayan a cigaba da rike su ba,  yara dai yaran zina ne,  ba zamu gurɓata alayenmu ba,  shine muka yanke mika su gidan marayu,  in har tana son Yaranta da gaske ta dawo gida tayi aure" Kanin ta ya faɗi yana jijjige-jijjige kamar zai mari Goggo.
Kukan da Salma ta saki ya kara karya zuciyar Goggo duk da zancen Kanin nata ya ɗan sa mata tsanar su.

"Amma Jamilu ka bani kunya,  har zaka kalli kwayar ido na ka danganta jikoki da zina,  Naji yan zinar ne me kai su gidan marayu zai haifar?  Ni dai zan rike su tsakani na da Allah,  yaran nan guda nawa ne da za'a fara jifan su da muggan kalamai. Toh gaskiya da sake"

"Mun baki nan da kwana uku ko ki mika su ga gidan marayu ko kuma in sa a tayar da ke a garin nan" faɗin Hakimi rai a ɓace,  ba tare da ya jira amsarta ba ya Mike ya fice daga gidan,  nan Kaninsa ya bi bayan sa shima

Abin da ake gudu 19

ABINDA AKE GUDU🙆🏽19

Batul Mamman💖


Hira suka zauna yi wadda duk tafi karkata akan rayuwar Asmau ta baya. Zubaida ta gyara zama tana karara jaddada mata kada ta kuskura ta biyewa rayuwar gidan. Idan da hali ma ta koma gidan iyayenta.

"Kinga ni a gidan nan na budi ido. Bansan kowa ba sai Mama kuma ban taba jin ko da wasa ta ambaci sunan wani gari a matsayin garinsu ba ko ta ce wane ne mahaifina. Tun abin yana damuna har na hakura. A 'yar fitar da nakanyi wani lokacin ne nake jin wa'azi a wurin masallacin bakin kasuwa. Sannan Mama ta koya min abinda ta iya na ibada kamar sallah da azumi. Bata  yinsu dai sosai kuma bata matsa min akan inyi. Haka kawai Allah Yasa min kyamar wannan kazantar. Kowane katon banza yazo yayi amfani da mace idan sun ga dama har dukan matan suke yi. Ban saka rai da cewa nan gaba wani zai aureni ba don Mama tace ba'a auren mata masu zaman kansu da 'ya'ya marasa uba. Burina daya ne a rayuwa Asmau, in sami wani wurin da zan kira gidanmu ba wannan ba".

Asmau taji Zubaida ta kara shiga ranta. A duk inda Allah Yaso sai Ya halicci shiryayye.
"Ba'a son raina na baro gidanmu ba nima. A lokacin ji nayi tafiyar ita kadaice mafita gareni da abinda ke cikina. Bana tsammanin su Umma ko Mama zasu taba karbar cikin. Shiyasa na zabi na haife shi a wani wurin da babu wanda ya sanni na kula da shi."

Kofar dakin suka ji an turo wata kyakkyawar mace ta leko da kanta. Cingam take taunawa yana kas-kas kana ganinta kaga wadda ta rasa mafadi. A dakile tace "kije Uwargida tana nemanki".

Zubaida ta tabe baki "tashi muje nasan batun kudin haya ne".

Asmau ta janyo jakarta ta bude. Dubu goma ta kirga ta mayar da jakar gefe duk akan idon 'yar aiken.

Suna fita 'yar aiken mai suna Darling ta ruga dakin kawarta ta sanar da ita irin abin arzikin da ta gani a jakar bakuwa.

Dakin Uwargida ciki da falo ne. A falon su Asmau suka sameta. Sai yanzu da hasken rana ya wadata ta karewa matar kallo. Suna kama sosai da Zubaida sai dai fatar  jikinta babu kyan gani saboda tsabar mayuka da ta sha. Ganin da tayi mata a cikin hasken farinwata ya rufa mata asiri.

Uwargida ta nuna mata kujera ta zauna. Falon sai ka zata na amarya ne saboda irin kayan alatun dake ciki. A darare Asmau ta zauna suka gaisa Zubaida ta zauna a hannun kujerar da Asmau take.

Uwargida tayi murmushi
"Ya bakunta? Ki saki jikinki indai zaki bani kudin haya to nan gidanku ne."

Asmau dai bata amsa ba ta dauko kudin ta mika mata. Ta karba ta soke a cikin riga tana dariya.

"Yarinya ki ce da arzikinki kika fito. Yau sai naga har kinfi jiya sheki ma. Dole na karawa Bulayi kudi don da alama baiyi zaben tumun dare be."

Zubaida ta ce "kinga tashi mu fita"

Uwargida ta tsayar dasu
"Na ce ba, idan kin yarda ki fara sana'a na zaba miki suna 'Yar Da6as. Naga jikin naki a mulmule ki hakura da hijaban nan, babu abinda zasu kara miki sai gumi da rufe kyakkyawan jikinki."

"Mama ita fa ba irin abinda tazo yi ba kenan." Zubaida ta fada tana yiwa babarta kallon raini.

Asmau ta dan gyara tsayuwa "dama ina so inji ko akwai gidan da kika sani masu wadatar da zasu iya daukar mai aiki. Kudin ko ba mai yawa bane zan iya".

Sai da Uwargida tayi dariya mai isarta sannan tace "to ai kin bar kari tun ran tubani. Babu gidan da za'a daukeki aiki alhalin kina zaune a gidan nan. Duk inda kika je koro ki zasuyi idan suka san daga nan kike."

"Niyyata idan na sami aikin na rokesu su barni na rinka aikin kwana."

Kallon mara wayo Uwargida tayi mata.
"'Yar Da6as, bari na baki shawara. Kada ki wahalar da kanki a banza. Wallahi babu matar da zata daukeki aiki kina gidan nan. Idan kin boye musu ma to dole zasu so ganin wata ce ta kawoki ba kawai zuwa kika yi daga wata uwa duniyar ba. Amma kina iya gwada sa'arki".

Daga nan tashi tayi ta shige daki su Asmau suka fita. Zubaida ce ta samo mata ruwan wanka bayan ta shirya suka fita neman aiki. Gidaje masu dan kyau da girma su Asmau ke shiga sai dai har yamma tayi babu inda suka yi sa'a. Da yawan matan da suke samu tambayar da suke fara yi mata shine wace ce cikin masu kawo 'yan aiki ta kawota. Wannan yanayi da ake ciki na rashin yarda babu wanda zai so daukar mutumin da ba'a san komai game dashi ba.

Washegari da zata fita Uwargida ta hana Zubaida bin ta. Duk tsiwa irin ta Zubaida babu yadda ta bata yi ba aka hanata fita. Asmau tace babu komai bazata yi nisa ba don kada ta bata.

Tasha yawo taga kuma mutane kala kala. Wasu da kalamai masu dadi suke nuna basa bukatar mai aiki. Wasu kuwa sai sun zageta musamman idan aka kare mata kalli bata yi kama da wadda talauci ya koro ba.

Ga yunwa ga kishirwa haka ta gaji ta kamo hanyar gida. A cikin kasuwar ta sayi bokiti da tukwane kanana biyu da plate. Har dan risho ta siya na girki da kayan abinci sannan ta koma gidan a gajiye.

Matan gidan babu mai kulata itama banda Zubaida babu harkar wanda take shiga har ta cika sati. A lokacin ne kuma tashin zuciya da amai suka sarketa. Tunda kowace mace girkinta daban take yi yawanci duk a kofar daki sai ya zamana warin girkin yana damunta. Idan taji aman bandaki take tafiya tayi ta fama babu wanda ya sani sai Zubaida. Ita kadai ke tausayinta take zuwa ta taimaka mata. Gashi duk abinda taci sai ya dawo.

Tayi kusan sati biyu tana fama gashi bata hakura da neman aiki ba. Har irin zaman shago da sharar titi duk ta nema. Ta rame tayi baki sosai. Sai dare tayi ta kuka tana kiran Umma.

Uwsrgida kuwa saka mata ido tayi. Jira takeyi Asmau ta kai inda hakurinta zai kare ta aminci ta fara aiki kamar sauran matan gidan.

*****
Hajjo ke kai kawo a tsakar dakinta tana jiran Rabe da ta aiki dansa ya kira shi tun wajen awa daya da ta wuce. Shigowa yayi da tsinken sakaci yana ta sokawa a hakoransa.

"Hajjo kina ta jira ko? Abinci na tsaya ci."

"Babu komai Rabe. Dama nace ya kamata muje gidan yarinyar nan Bara'atu. Kusan sati hudu da batan Asmau mun barta ita kadai tana fama. Duk lalacewa 'ya'yan Shuaibu ne bai kamata mu zare hannu daga kansu haka ba."

Hade rai yayi kafin ya soma magana cikin nuna isa "Hajjo tun rannan kike maganar nan nace bazamu je ba. Ita bata san ta neme mu ba sai mune zamu je kawai saboda rasshin zuciya. Ki kyaleta nasan yarinyar bazai wuce ta tafi yawon ta zubar ba. Kuma da kike tausayinta ai ta raina ki. Tun bayan maganar cikin Asamaun kika ce a turo miki Yassar yake ko wa, da kanwarsa amma ta shafawa idonta toka taki".

Hajjo tayi shiru ganin Rabe yana fada. Har ranta tana tausayin Bara'atu kuma ta shiga damuwa sosai da batan Asmau. Sai dai tana tsoron batawa Rabe rai. 'Yan uwansa gabadaya yanzu tsoronsa suke yi babu mai son ketare maganarsa.

Zuba mata ido yayi tana tunani. Yana gudun Hajjo ta dena jin maganarsa ya shiga uku.

Ita ma ganin bacin ransa tayi murmushi "nifa dama so nake muje ko rashin mutumci ne muyi mata bawai mu nuna tausayi ba. Duk laifinta ne lalacewar yaran. Jeka abinka kawai"

Rabe yana tsare gira ya shuri takalmansa ya fita hankalinsa a dan kwance da jin maganar Hajjo ta karshe.

Da ya fita dan kashingida tayi sai dai sam baccin yaki zuwa. Tunanin yadda ta kasa rike zuri'ar Shuaibu ne yake damunta kamar ba danta ba. Kuma ta duba iyakar dubawa babu wani laifi da Bara'atu tayi mata. Yanke shawara tayi a ranta gobe zata sake tambayar Rabe ko zata yi sa'a ya barta taje gidan Bara'atun.

*****
Umma ta idar da sallah Aina'u ta fada mata wani dan sanda yana nemanta. Ko addu'a bata yi ba ta tashi da sauri.

Qasim ne ta tarar a falon suna magana da Jafar. Bayan sun gaisa yake sanar da ita har yanzu dai bincikensu bai nuna musu komai game da inda zasuyi tunanin samun Asmau ba. Amma tayi hakuri don yayi alkawari bazai taba dena nemanta ba ko a raye ko a mace.

"Nagode sosai Qasim Allah Ya saka da alkhairi."

Tausayin Umma yake ji duk ta rame ta fita hayyacinta. Gidan idan ka shigo tamkar babu mutane saboda halin da suke ciki. Kuma a ganinsa duk laifinsa ne na ziga Abubakar.

"Umma ki dena yi min godiya. Bani da wani buri a rayuwata da ya wuce neman Asmau da zama uba ga abinda ke cikinta. Tsautsayi ne da kaddara ya jefata wannan halin".

Hawaye ne ya saukowa Umma. "Haka ne Qasim. Dukkan *DAN ADAM* yana yin aiki ne da ya dace da kaddarar rayuwarsa. Fatana Allah Ya kare min Asmau daga fadawa mugun hannu ko shiga duniyar sa6o."

Jafar yace "Umma don Allah ki dena kukan nan. In sha Allah zamu ganta komai daren dadewa."

Har bakin gate ya raka Qasim wanda ya koma gidan Mama. A can dinma zancen Asmaun ne dai. Duk da har yanzu ba wai ta gama amincewa bane cikin na Abubakar ne sai dai zaman tare da Umma yasa suka ajiye komai burinsu kawai a ganta.

*****
Yau ma a gajiye Asmau ta dawo gida ga jikinta duk babu dadi. Kamar sauran ranaku bata yi sa'ar samun aiki ba. Dan kayan abincin da ta siya duk sun kare dama ba da yawa ta siyo ba saboda tunanin barin gidan idan ta sami aiki. Da sallama ta shigo wasu suka amsa wasu kuwa ko kallonta basuyi ba ta wuce dakinta.

Jakarta ta janyo zata dauki kudi ta siyo abinci taga babu ko kwandala a ciki hatta sarkarta babu. Jakar ta zazzage gabadaya bata ga kudin ba ta fito ta tafi dakin Uwargida.

Zubaida na jin sallamarta ta fito da murmushi. " 'Yar uwa an dace yau?"

Asmau ta girgiza kai sai kuka. Uwargida ta shigo dauke da buta da kwandon wankanta a hannu daidai lokacin da Asmau tace an sace mata kudi. Kamshin sabulun wankan Uwargida ne ya bugi hancin Asmau tun kafin ta fita daga dakin amai ya kufce mata.

Uwargida tayi galala tana kallonta cike da mamaki. A tsakar gidan ta durkushe tana ta kwara amai Zubaida nayi mata sannu.

Taruwa akayi a kanta Uwargida ta durkusa a gabanta bayan ta gama aman ta gwale mata ido tana gyada kai kamar kadangaruwa sannan ta kalli Zubaida.
"Amma Zuby kin ha'inci sabuwar kawarki da baki fada mata babbar dokar gidan nan ba. 'Yar Da6as ai ba'a ciki a nan. Idan ma ya shiga bisa tsautsayi to sai ki zaba ko ki cire ko ki fita. Sannan da kika ce anyi miki sata to tun wuri ki sani bazan lamunci karya ba. Wannan cikin kuma ki san yadda zakiyi dashi kafin raina ya baci."
Tsaki ta buga ta wuce dakinta tana fadan Asmau zata kashe musu kasuwa.

Da taimakon Zubaida Asmau ta koma daki ta kwanta. Duk yadda taso daurewa kuka take yi sosai. A yanzu bata da wani gata sai Allah. Dan kudin da take takama dashi an sace. Dama tana son siyan kwadon rufe kofa Allah bai nufa ba har aka yi mata sata.

Kwanakin da suka biyo baya ba karamar wahala tasha ba. Rashin kuzari da tashin zuciya kullum dashi take tashi. Ga rashin abinci. Ruwan sallah wannan bata samu sai abinda Zubaida ta dauko a dakinsu batare da sanin Uwargida ba ta bata.

Duk yadda taso daurewa abin ya gagara. Kusan wata guda tana cikin mawuyacin halin nan. Kayanta sunyi dukun dukun kamar wadda take wasan dambe. Ita kanta warin jikinta take ji wanda yake kara sakata jin amai.

Tana zaune a kofar dakinta wanda taci alfarma Uwargida ta daga mata kafa bata biya kudin wannan watan ba. Matar dakin kusa da ita wadda taji ana kira Beauty ce zaune tana cin taliya da manja da yaji. Yawun Asmau duk ya tsinke ta zubawa Beauty ido kamar ta hadiyeta har sai da ta kula ta ja tsaki ta koma cikin dakinta. Haushin Asmau take ji saboda saurayin da yazo wurinta dazu ya nuna yana son Asmaun har yayiwa Uwargida magana.

Beauty na shiga daki Asmau ta rarrafa ta tsinci taliyar da ta zubar a kasa ta cinye tana kuka. Duk abinda take yi akan idon Uwargida tayi murmushin keta. Dama tuni ta hana Zubaida bawa Asmau abinci sai dai a bayan idonta. Karasowa tayi gabanta ta tsaya da alamun tausayin karya a fuskarta.
" 'Yar Da6as kin fiye taurin kai. Zaki iya canja akalar rayuwarki duk sanda kika so. Dazu mutum kusan na tara kenan da ya nuna yana sonki amma kullum sai ki dage ke bazaki amince ba. Ga yunwa tana damunki sannan wannan abin na cikinki yanzu kin amince ki haife shi a wannan yanayin? Ni shawara nake baki nan da sati idan baki zubar da cikin kin fara min aiki ba zaki bar min gida. Na daga miki kafa ne kawai don nayi tunanin zan more ki."

Bayan tafiyarta Asmau ta rike ciki tana kuka. Tabbas idan ta haihu rayuwar danta zata shiga mugun yanayi. Halin da ta tsinci kanta yanzu ji take ina ma bata raye. Shawara daya ta rage mata tunda babu mai tausayinta gara ta zubar da cikin ta nemi kudi kamar yadda Uwargida ta bata shawara.
*****

Karfe biyu da rabi na dare Umma ce zaune akan abin sallah. Addua take yi tana zubar da hawaye....fatanta duk inda Asmau take Allah Ya kareta daga fadawa ga abinda zai zama halaka ga rayuwarta.

Abin da ake gudu 20

ABINDA AKE GUDU🙆🏽20

Batul Mamman💖


Wani mugun fitsari ne ya tashi Asmau daf da kiran assalatu. Ta fito zata je bandaki amma ko ruwan tsarki bata dashi. Haka ta koma daki tana ta matse shi da adduar Zubaida ta fito da wuri ko dan yaya ne ta sammata. Har aka idar da sallah a masallaci Zubaida bata fito ba. Zuwa lokacin Asmau sai gumi take yi tana cilla kafa. A hankali taji ya fara zubowa dole ta tafi bandakin da gudu tayi batare da tayi tsarki ba. Haka ta dawo dakinta ta shafi kura tayi taimama sannan tayi sallar asuba.

Batun jin yunwa dama ba'a magana. Wannan yanayin da ta tsinci kanta a ciki hakurinta ya fara karewa. Ace tayi fitsari ko ruwan tsarki babu gashi tana gani amma gidan nafsi nafsi (kowa na ta kansa)kawai ake yi.

Yau Zubaida bacci sosai take yi don har tara ta wuce bata farka ba. Asmau ta gaji da jiran tsammami ta duba hijabinta wanda yafi kowanne dauda ta saka ta fita bakin titi. Ga rana ta kwale haka ta daure zuciyarta ta zauna duk wanda yazo wucewa tace.

_Sadaka fisabilillah_

Mutumin farko da ya bata naira goma yana yin gaba ta saka kuka. Wai ita da watanni kadan da suka wuce take cikin rayuwar jindadi tare da masoyinta da iyayenta, ita ce take bara tamkar mara galihu. Bara sana'ar da take tattare da kaskanci da mutuwar zuciya. A ranta addua take yi Allah Yasa mufi karfin zukatanmu Ya nesanta mu da kaddara mai muni irin wannan.

Ita kenan ma da tayi nadama amma Allah Ya zabeta don gwada imaninta da kuma nuna aya ga sauran mutane. To ina masu aikata zinar duk da sun san laifine amma basu dauketa a bakin komai ba. A ganinsu suna da sauran lokaci. Ina masu bada muguwar shawara a baki ko a rubuce batare da yin la'akari da tasirin da hakan yake yi a zukata masu rauni ba. Da Abubakar bai tuba ba shikenan haka mutuwa zata riske shi yana halin sabawa Mahalicci.

Taci kuka har ta godewa Allah a wurin. Har rana ta take naira hamsin da biyar ta hada. Ga jiri na dibanta saboda tsabar yunwa. Tashi tayi ta kama hanyar gidan da yanzu shine matsuguninta. A hanya ta sayi fanke na naira hamsin din da pure water guda daya.

Dakinta ta wuce wanda ko jawo kafar batayi ba. To me zata rufe bayan bata da komai. Fanken nan ta janyo tana ci hannu baka hannu kwarya. Ko uku bata ci ba sai amai ya taso mata. Dole ta hakura ta dan jingina da bango tana adduar kada ya fito don ta dan ji kwarin jikinta.

Ba don tana gudun mutuwar kafirci ba gani take yi a wannan lokacin gara ta mutu ta huta. Tana jin shigowar Uwargida ta tashi ta bita daki. Bazata iya cigaba da bara ba gara kawai tayi abinda zai fishshe ta a nata ganin.

" 'Yar Da6as yau tun safe kina ina?"

Asmau ta dan waiga bayanta tana dube dube.

Uwargida tace "indai Zubaida kike nema na kaita wurin uwargijiyata a wannan sana'a. Girma ya fara kamani dolenta ta nema mana kudi. Yaya Babba zata koyar da ita ta karfin tsiya sannan ta dawo gidan nan ta taimaka wurin dago darajarsa kamar da."

Tausayin Zubaida ya kama Asmau. Yarinyar da bata kaunar zaman gidan ma bare sana'arsu ace wai mahaifiyarta da kanta take son lalata mata rayuwa. Sai dai babu taimakon da zata iya yi mata yanzu. Kanta a kasa tace "idan kina da maganin zubar da cikin ki bani".

Wata shewa da tafi Uwargida tayi cike da murna. Tasan za'a rina. Wannan yanzu idan ta fara bawa Asmau abinci na sati tuni zata murmure ta fara caskar kudi da ita.
" kin taimaki kanki kuma na tabbatar bazaki yi dana sani ba muddin kika fara jin jakarki da nauyi. Bari na dauko miki wani jiko da na bawa Darling kwanaki."

Uwar dakinta ta shige ba jimawa ta fito da wata robar swan da ta dafe da datti. Ruwan ciki kore ne fatau ga wasu 'ya'yan ball suna ta shawagi a ciki. Asmau na ganin robar taji amai na yunkurin fitowa. Toshe bakinta tayi ta karbi robar ta fita bayan Uwargida tayu mata bayanin yadda zata sha.

Tun da ta ajiye robar ko kallon wurin bata sake yi ba. A matsayinta na wadda take da ilimi daidai misali tasan shan wannan kazantar babbar illah ne gareta.

Washegari wurin karfe goma ta tashi ta shiga cikin kasuwa. Tasha yawo sannan Allah Ya sa taga abinda take nema wato chemist(kemis). Daga saman an rubuta *SADA AND SONS CHEMIST*.

Mutane ne suke ta shige da fice a wurin ta rakube daga can gefe tana jira suyi sauki ta je ta roki mai kemis din ko zai taimaka mata da maganin zubar da ciki. Sama da awa daya bata ga alamun mutanen zasu yi sauki ba har ta gaji ta soma gyangyadi a gefen wani benci da aka ajiye a wurin shagon.

Cikin bacci taji an soma kiraye kirayen sallar azahar ta bude ido tana hamma sannan ta dan kalli kofar shagon ta ga akwai mutum daya a ciki har yanzu. Daga can nesa  ta hango wani yaro da kayan makaranta da flask din abinci ya nufo wurin shagon. Ta tashi ta kade jikinta da niyyar idan ya iso zata roke shi ko ya rage abinci ya bata.

Yana zuwa kuwa ta dan sauke murya.
"Don Allah in ka rage abincin makarantar ka bani in ci".

Yaron da zai kai shekara goma yana da dan jiki ya kalleta yayi murmushi
"Kwanon abincin makarantana na mayar gida. Wannan na babanmu ne na kawo masa".

Daga haka ya shige cikin shagon. Ba dadewa suka fito wurin 'yar rumfar kofar shagon inda bencin yake. Yaron ya ce "Baba kaga almajirar da tace na bata abincin naka".

Mal Sada mai kemis ya dan kalli Asmau. Tabbas babu wanda zai mata wani kallo daban da na almajira. Dogon mutum ne mai dan haske da kiba. Fuskarsa kadai zata nuna wa mutum yana da kirki.

Da hannu ya yafito wata mai awara yarinyar ta karaso da gudunta don kada 'yan talla 'yan uwanta su riga ta zuwa. Ya zira hannu a aljihu ya dauko naira dari ya mika mata.
"Zuba wa matar nan ta sittin sai ki bata canjin. Abba miko mata ruwa a cikin fridge dinnan guda biyu."

Mai awara da Abba suka yi yadda Mal Sada ya saka su. Asmau na karba ta rinka yi masa godiya da fatan alkhairi sai ka zata ta dade tana sana'ar bara.

Mal Sada ya dan daure fuska "nan ba wurin zaman almajirai bane kinji ko. Idan kin gama ci ki tafi."

Ta gyada kai ta koma gefe ta zauna. Da ledar ruwa daya ta wanke hannunta ta fara cin awarar cikin jindadi. Rabonta da abincin kirki ta kwana biyu. Tana gamawa tasha ruwa sannan ta dauki daya ledar ruwan tayi alwala ta shimfida dankwalinta tayi sallah. Lokacin tuni Abba ya tafi. Sada yana kallonta sai ta burge shi da bara bata hanata ibada ba.

Bayan ya dawo daga masallaci yana bude shagon kafin kowa ya shiga ta bi bayansa. Sai kuma kunya ta hanata fadin abinda ya kawota.

"Kina bukatar wani abu ne?"

Kamar mai rada tace "nawa ne maganin zubar da ciki?"

Cak ya tsaya yana kallonta. Wato ban da bara har jikinta take sayarwa. Ransa a bace yace "idan baki fice min daga nan ba ranki zai baci. Ku baro gidajenku kuna bara saboda mutuwar zuciya karshe almajirai da marasa zuciya irinku su rinka yi muku ciki. Ko ina dashi bazan bayarba."

Asmau ta soma kuka tana rokonsa ya taimaka mata.

Daga hannu Sada yayi kamar zai maketa shiyasa ta fita. Amma a kofar shagon nan ta zauna har taran dare lokacin da yake rufewa. Ko kallonta baiyi ba da zai wuce tana ta masa magiya.

Washegari tun kafin yazo shagon ta iso. Yinin ranar da ta ga babu mutane sosai sai ta shiga ta roke shi. Tun yana mata fada ta fita har ya dena kulata sai ta ga wani zai shigo ta fice a sanyaye.

Dansa Abba ya sake kawo masa abinci amma yau bai bi ta kanta ba. Yana ciki yana cin abincin ne ya jiyo kakarin amanta. Tun awarar jiya bata sake samun wani abincin ba.

Kamar ya share sai ta bashi tausayi ya dauko flask din ya mika mata. Idanunta sun kara fitowa waje sai hakora gayau kamar ta shekara tana jinya. Kusan fizgar flask din tayi ko wanke hannu bata yi ba ta soma cin abincin. Abinda bata taba ji bane ya faru a wannan lokacin. Motsi taji a cikinta wanda ya kara tabbatar mata lallai ba ita kadai take rayuwa ba. Yanayin da ta shiga da jin motsin yasa ta farinciki ta dafe cikin. Tunowa da Abubakar da halin rayuwarta kuma yasa ta koma yin kuka. Abincin da bata iya cinyewa ba kenan.

Da Sada zai tafi ta mika masa flask din yace ta rike ya bar mata. Yana kallonta ta tafi har ta bace masa.

*****
Sau biyu kenan Rashida tana fadawa maigidanta ta kai masa ruwan wanka sai yace to ina zuwa. A karo na uku ta zauna kusa dashi cikin damuwa.
"Baban Abba me ya faru ne? Allah Yasa ba laifi nayi ba."

Dan murmushi Sada yayi yana kallon abar kaunarsa.
"Ko kadan Maman Abba. Bari nayi wankan dai."

Sai da ya gama cin tuwo sannan ya bata labarin Asmau mai zuwa kofar shagonsa.
"Ni bansan daga ina take ba sai dai ta bani tausayi. Muna ganin kanmu kamar marasa arziki amma wallahi cikin rufin asiri muke akan wasu. Tsorona daya kada taje wurin wani mara imanin ya bata maganin."

Rashida tace "to ai dama kaine kullum kake ganin kamar shagonka kadai baya wadata mu. Amma gashi yara hudu duk suna makaranta kuma bama rasa abinci.
Idan bazaka damu ba gobe sai na kawo maka abincin da kaina na ganta. Kila idan  na bata shawara ta hakura da zubar da cikin ta koma gida".

*****
Asmau ta dauko robar da Uwargida ta bata. Tana son sha kuma har ranta bata son zubar da cikin. Dama gudun zubarwar yasa ta fito daga gida. Dan motsin nan da taji ya sa ta kara son abinta. Robar ta dauka ta zubar da kadan a bakin rariya sannan ta mayarwa Uwargida. Bakin Uwargida a washe tace
" nan da wayewar gari ma yana iya zubewa. Kinyi kyan kai 'Yar Da6as."

Yau ma ta riga Sada zuwa shagonsa. Ita kanta bata san me ya dawo da ita ba. Da yazo har kasa ta durkusa ta gaida shi. Ya amsa mata fuskarsa babu yabo babu fallasa. Yayi mamaki da ko sau daya bata sake batun maganin ba. Tana dai zaune ne kawai a gefe guda.

Wuraren shabiyu wata mace ta sha katon mayafi ta iso kafar shagon da flask din abinci. Matar tayi mata murmushi Asmau ta gaisheta. Sada ya fito daga cikin shagon yace "wannan ce yarinyar".

Rashida taji tausayin Asmau ba don komai ba sai don yanayin da ta ganta. Har wani wari take yi saboda rashin wanka. Sada yace su shigo ciki ya dan kara kofar alamun ko anzo kada a shiga.

Asmau na zaune a kasa a gabansu Rashida tace ta fada musu daga ina take kuma ina uban dan dake cikinta.
"Kada kiyi mana karya domin kuwa Allah Yana kallonmu".

Karo na biyu kenan tana bada labarinta. Kafin ta gama Rashida tayi ya6e ya6e da hawaye don tausayi. Mata da yawa idan an tambayesu game da ciki a irin wannan yanayin sai suce fin karfi aka yi musu. Amma wannan yarinyar ta zabi ta fada musu abinda suka fi tunanin gaskiya ne. Wato biyewa rudin shaidan da son farantawa masoyi. Shi kansa Sada yaji tausayinta matuka. Lokaci guda tarbiyarta ta wargaje a dalilin kawa da kafafen sada zumunta.

Waje suka ce ta fita ta jira su. Muhawara sukayi inda yace su mayar da ita gida Rashida tace kada ta koma sai ta haihu ta yiwu iyayen su yafe mata idan suka ga dan a hannu. Duk da suna tsoron halin Dan Adam yanzu. Kayi masa rana yayi maka dare amma zukatansu sun amince da taimakonta musamman ma suna jin tsoron kada ta zubar da cikin ta fada sana'ar banza.

Sada ya rufe shagon suka ce ta biyosu. Babu musu tabi bayansu tana adduar Allah Yasa alkhairi ne a tattare da mutanen.

Sunday, 15 January 2017

Silar Ajali 2

Silar Ajali
Alkalamin Safiyyah Ummu-Abdoul

Babi na biyu

Sai karfe tara na dare suka samu isa gidan Goggo Salame kamar yanda mutane suke kiranta. Tafiya ce mai tsawo daga Katsina zuwa marke,  ga rashin sanin takamaiman wajen zuwa hakan ya haddasa ma Salman damuwa ga yunwa yana ji hakan ya sa siraran hawaye gangarowa daga idanunsa.  Da tambaya da ɓatan hanya suka iso gidan Goggo Salame wacce da farko kin sauraransu tayi sai da suka faɗa mata daga inda suke.
Faɗi take
   "oh ni Salame,  yanzu duk tsawon lokacin nan kuna wajen Amina bata taɓa nuna min ba.  Ita uwar taku kuma abinda ta zaɓa ma kanta kenan.  Allah ya shirya" 

Ta sa musu tuwo da miyan kuka bayan ta tabbatar da sun watsa ruwa don kauda dauɗan da su kayi.  Ci suke kamar wanda suka Share Shekaru babu abinci,  nan take tausayinsu ya dira a zuciyar ta karo na farko tun bayan isowarsu gidanta. Bayan sun gama ci ta mika musu tabarma sannan tayi masu jagora zuwa ɗaya ɗakin da ke kallon tsakar gida.  Suna godiya gaba ɗaya suka shige ba tare da ɗaukan lokaci ba barci ɓarawo yayi awon gaba dasu.

                         ***
Washegari,  tun bayan asuba Salma bata koma ba,  gari na yin haske ta fito ta Share tsakar gidan tas,  sai a lokacin ta kare ma gidan kallo.  Tsakar gida ne sai ɗaura biyu da ke kallon tsakar gidan,  chan daga yamma kuma akwai ɗaki amma da gani rabon da ɗakin ya amshi bakoncin mutane an manta.

"Haba,  Salama,  kya bari ki huta mana ,  ai kin san kina cike da gajiyan jiya kin fito kina ta aiki" Goggo ta faɗi tana kallon Salma.

   Fara ce siririya, shekarunta basu wuce goma sha biyu ba, amma tsawon kafarta ya zarce na sa'o'inta.  Gashin ta ya leko ta Kasar kallabinta, murmushin da Salma tayi don ba Goggo ansa ya sa kumatunta lotsawa nan take hawaye ya fara sintiri a idon Goggo tunawa da mijinta da tayi saboda wajen sa Rahanatu ta yi gado gashi ya bayyana a jikin jininta.  An take bakin ciki ya cika mata zuciya tunawa da tayi da  SILAR AJALIN mai gidanta masoyinta. 

Juyawa tayi fuuuuu zuwa cikin daki kamar guguwa,  sakin tsintsiya Salma tayi ta bita da na mujiya,  in har ba idon ta ya gwada mata karya ba hawaye ta gani a idon tsohuwar.  Toh ko me yasa?  Taɓe baki tayi ta ɗauki tsintsiyar ta cigaba da shara.  Sai da ta Share gidan tsaf sannan ta yi wanka ta chanza kaya,  haka ma sauran yan uwanta.

Bayan sun gama cin abinci Goggo ta sa suka shirya ta kai su gidan yayanta hakimin Marke Alh Yunusa Ladan, ko da suka shiga, falonsa ta wuce bayan ta gaisa da matan sa, da sallama suka shiga falonsa, bayan sun gaisa ne take ce da shi,

"sai ka ganni da yara ko?  Yaran yarinyar nan ne,  jiya Amina ta turo su da yake chan wajenta ta kai su a Kano, wai mijinta ya gaji da rikonsu" ta faɗi cikin Yanayin ɓacin rai ko a ce bata son magantawa

"Dama kin san da zaman su ne, ina ce tun Shekaru goma sha takwas da ta bar garin nan bata sake dawowa ba,  ko ta dawo ne bani da labari,  kuma ina ta samo yaran da zata turo miki ki amsa" ya faɗi rai a ɓace.  Bai tsaya jin ta bakin ta ba ya cigaba da cewa,

"ko akanta aka fara fyaɗe,  duk wanda aka mawa shiru suke yi su rufa ma kansu da iyayensu asiri,  amma ta kunso ciki sannan a ce fyaɗe,  amsa min salame dama kin san da zaman su ne ko kuwa kin san da auren da tayi ta haife su" ya faɗi yana kara huhhura hanci da zare idanu.

Numfashi ma a tsorace su Salma ke fitarwa Salman ne mai karfin hali da jarunta,  kukan da suka saki ya kara ankarar dashi zaman su a wajen.

"ku fita ku ban waje yayan gaba da Fatiha" ya faɗi a tsawace yana mai nuna musu hanyar kofa.  Cirko Cirko suka taradda matan gidan a tsakar gida kasancewar sun ji duk abin da ya ke faɗi a ɗakin.

"Yaya ban san da zaman su ba sai zuwan da Amina ta yi bara wancan,  kasan cewa gwamnati ta biya musu aikin haji, a can suka haɗu da RAHANATU ɗin wai tayi aure,  da zuria.  Kasancewar tsadar rayuwa a can ba irin na mu na nan bane bayan dawowarsu da yan kwanaki ta turo yaran.  Yanzu shekaran su biyu kenan da dawowa.  Kayi hakuri yaya,  bani son ranka ya ɓaci sannan ni kaina ban ɗauki zancen Rahanen da mahimmanci ba wallahi.  Kayi hakuri" ta faɗi tana kankantar da kai alamun neman gafara.

"in ba zata zo ba inaga za'a tura mata Yaranta.  Bana son shiririta,  a yi rainonta ayi na Yaranta,  Sam ba zai faru ba" ya karasa alamun nuna ya sauko daga Fushin.

"kun ga kuyi hakuri ku yi shiru,  in Goggo ta kore mu bamu da wajen zuwa,  kun san dai sai an shiga jirgi za'a je inda innarmu ta ke,  kuma ko a chan ɗin babu wani tsaro,  amma ai tace mana zata zo ai ko" Salman kenan yake rarrashin Salma da Suhayl da suke ta kuka tun tsawan da ɗan uwan Goggo yayi musu,  nan suka ɗaga masa kai alamun gamsuwa,  shi kuma ya cigaba da cewa,

"Kunga in ta dawo baza mu yarda ta koma ba sai da mu, kuyi hakuri banda kuka banda riko,  ba zaku gane gatan da Goggo tayi mana ba sai a gaba. Kunga dole muyi hakuri da ita "

Tashi su ka yi  zuwa gareshi ya rungomo su.  Haj Aziza uwargidan yayan Goggo nan take ta ji tausayin su da kaunar su ya mamaye ta,  ba tare da ɓata lokaci ba ta ja su zuwa ɗakin ta. Sannan ta karɓa musu zoɓo da atine amarya ke siyarwa ta ba su suka sha.
   "kar ku damu kunji  nan gidan kakanku ne, dangin mqhaifiyarku kenan bata da kamar mu haka ku ma, Insha Allahu ba zaku yi dana sanin dawowa nan ba kunji.  Duk abin da kuke so ku zo waje na kunji.  Ba kuma zaku rasa ba Matukar bai fi karfi na ba."
    Nan take zuciyar su ta fara haske,  murmushi ya bayyana a fuskokinsu hakan ya sa ta cikin farin cikin da bata san dalilin sa ba.
  
Ko da Goggo ta shigo ɗakin bayan sun gama tattaunawa da Yayan ta hakimi,  zama tayi suka sake sabon gaisuwa da hajiya.

"Yaran nan dai amana ne a gare ki da mu duka,  in kika yarda aka raba ki dasu kamar yanda aka raba ki da uwar su ke kika so,  don na lura har yanzu Sam baki san 'yancin da musulunci ya baki a matsayin mutum ba. Shi da ya aikata mugun aikin ba wanda ya tsangwama ma rayuwarsa sai su da ya nakasa" faɗin Hajja Aziza bayan sun gama gaisawa.

"kai matar yaya,  kullum ke dai maganar ki yancin mata,  ai musulunci bai yarda mu dinga fito na fito da maza ba,  namu ko da yaushe hakuri ne,  shi da ya yi fyaden ai ado ne macece dai bai kamata ta fita ba balle har a ganta ayi mata fyade,  kin manta har haddi aka yanke ma malam,  Allah ya masa rahma" ta faɗi tana murmushin da kallo ɗaya zaka  masa ka san cewa iyakarta fatar bakinta..

"Musulunci ya ba maza da mata yancin neman ilimi,  haka zalika fita aiki.  Matsalar mu mata ba ma zurfafa ilimi sai ayi amfani da al'ada a dankwafar da mu da sunan addini.  Laifin RAHANATU fita neman ilimi ko a ina aka karanta mata kar su nemi ilimi,  mata sun rike mukamai a zamanin annabi ke mace sai da ta zama shugaban kasuwa, Umar ibn Al-Khattab da kansa ya zaɓi Samrah bint Nuhaik ta shugabanci kasuwa, Khadija yar kasuwa ce amma annabi bai hanata ba,  Nusayba bnt kaab Alansariyya jaruma ce da ta fita jihadi da takobi. Ai da sai annabi yace mata basa fita aiki ko karatu,  Kawla bint Azwar taje yakin Yarmuk tare da Khalid bn Walid,  Aishat ummul muminin makaranta gareta a gida, Zainab bnt Ali itama tayi jihadi da ɗan uwanta Hussain.  Kinga kaɗan daga cikin fita da mata suka yi a lokacin annabi.  Al'adanmu ce hana mata fita, ko mai mace tayi don samun cigaban al'umma sai a hana ta saboda ana mata kallon mai rauni.  Ɗaukakan kowace al'umma yana ga samun mata masu ilimi da nagarta.
  
Shi yanzu ya mata fyade,  tsoron tsangwama yasa tayi shiru,  ina ce satin da aka fahimci tana da ciki aka kama shi a ɗakin Amaryar kawunsa yana shirin mata fyade,  ihun da tayi don tsabagen son rai ya ja mata saki daga Kawun nashi. Ke ba zaki ja taki jiki ba kin tsaya biye ta alhaji. Kar inji kin yi abin da ya ce,  in ita ta dawo don kanta fabi Ni'ima amma in bata dawo ba fatan Allah ya albarkace aurenta da zuri'ar su. "

" Aameen ya rabbi,  hajiya na gode,  zan dinga zuwa kina bani tarihin mata sahabbai,  don na lura ba boko ya wayar miki da kai ba,  ilimin tarihin annabi da sahabbai ne ya buɗe miki idanu har ake ganin kin waye da yawa ashe tsabagen sanin yancin da musulunci ya tanadar miki a matsayin ki na mace mutum kamar kowa" Goggo ta faɗi tana dariya.

  "kai Salame kenan,  Toh akwai gatan da ya wuce wanda musulunci ya bamu,  kawai al'ada muke ba fifiko shi yasa muke wahala.
  Yanzu misali na RAHANATU,  a dole akai zina da ita Kinga a musulunci ba ta da zunubi amma a al'ada tayi gagarumin abin kunya,  hakan ya sa aka kore ta,  maimakon a hukunta shi wanda ya fi karfinta yayi zina da ita.  Yanzu dai ga gudunmuwa ta nan a sa su a islamiyya anjima.  Allah ya raya mana su" ta karasa tana mai mika mata naira dubu uku.  Nan ta karɓa tana godiya sannan suka yi sallama suka kama hanyar gida.

Abin da ake gudu 18

ABINDA AKE GUDU🙆🏽18

Batul Mamman💖


Bacci barawo ne ya sace Asmau ba don taso ba. Ta raba dare tana kuka wanda ya haddasa mata mugun ciwon kai ga jikinta da yayi tsami. Washegari wurin karfe takwas da rabi ta fito daga dakinsu zata shiga kitchen dora ruwan tea ta tarar Umma har ta dama kunu tana buga kosai.

Gaishe da Umman tayi sannan ta yunkura zata karbi aikin ta karasa Umma tace ta bari ya jikin nata. Kafin ta amsa Umma ta dakatar da ita
"Asmau ki fada min gaskiya meye yake damunki? Ji yadda fuskarki ta kumbura ga wata tafiya kina yi kamar me tatata".

A dan tsorace Asmau tace "zamewa nayi a toilet da zanyi alwala."

Umma ta bita da kallo na rashin gamsuwa.
"To fuskar taki fa? Kinsan bana son boye-boye idan rigima kuka yi da Abubakar jiya ki fada min tun wuri ayiwa tufkar hanci."

Murmushi Asmau ta kalalo "Umma lafiya kalau muke. Kaina ne har yanzu yake ciwo sosai kamar bansha magani ba".

"Idan anyi breakfast sai Jafar ya kaiki asibiti tunda dai kin sha magani jiya bai warke ba gara kiga likita sosai. Allah Ya sauwake. Bari na soya kosan sai kici kiyi wanka."

Jikinta a sanyaye ta fita ta koma daki tayi wanka.  Zuciyarta ta gama raunana amma cigaba da kukan bazai amfaneta da komai ba sai tonon silili.

Umma kuwa sai tattalinta take yi har daki ta kai mata abinci tana ta sannu. Wannan ya kara sawa taji ta tsani kanta. Ji yadda mahaifiyarta ke kula da ita bayan ciwon nata baya bukatar tausayawa daga kowa.

Sunje asbiti tasha allurai saboda zazzabi sannan aka bata magunguna.

Da suka koma gida Umma ta sanar da ita Abubakar yazo amma ya wuce Kaduna ana nemansa akan wasu takardu da ya kulle a office. Kai kawai Asmau ta gyada ba don ta yarda ba. Daga dawowarsu zuwa wayewar gari tayi masa text yafi goma banda waya da ba'a kirgawa. Gani take yi kawai zai gujeta ne kamar yadda take yawan jin labarai na samari da suke yaudarar 'yan matansu.
*****

Kafin azahar Abubakar ya isa Kaduna. Jiya ko kadan bai runtsa ba sau tunani da ya addabi zuciyarsa. Ji yayi Kanon tayi masa zafi shiyasa ya dawo saboda baya son yawan tambaya akan me yake damunsa.

Kwanansa biyu da dawowa  baya zuwa ko ina daga office sai gida sai ko masallacin unguwar da yake. Rabonsa da abincin kirki ma ya manta. Yana kwance ya kurawa fanka dake juyawa ido wayarsa tayi kara.

Sunan Qasim ya gani shiyasa ya dauka. Qasim ya sanar dashi wani aiki zai kawo shi garin yanzu zai kamo hanya. Addua Abubakar yayi masa sannan ya dan gyara dakin da ko shara baya samu.

Tun zuwan Qasim ya kula da canjawar da abokinsa yayi. Yayi tambayar har ya gaji babu amsa. To me zai fada masa?

A nata bangaren Asmau ji take yi kamar tayi hauka. Tayi wayar har ta gaji. Hawayenta ma ya kafe jira take kawai azo ace Abubakar ya fasa.
*****

Ranar juma'a da safe Abubakar ya gama shirin tafiya office Qasim yace
"Karfe nawa zamu tafi Kanon?"

"Wannan satin bazan je ba ayyuka sunyi min yawa" Abubakar ya bashi amsa.

Kayan da yake sawa a 'yar jakarsa ya ture ya koma kallonsa "Abubakar nayi nayi ka fada min abinda ke damunka kaki na rasa dalili. Ni mai sonka ne da alkhairi idan ka fada min ko addua sai na tayaka".

Kwalla yaji ta cika masa ido ya dan dake "na fada maka babu komai bari naje na dawo mu tafi. Shikenan ko".

Qasim dai bai gamsu ba. Yana nan zaune aka kawo wuta ya saka wani CD na wa'azi da ya gani a kusa da tv din dakin. Ko minti goma ba'ayi da farawa ba Abubakar ya shigo lokacin shabiyu saura.

Zamansa ke da wuya aka yiwa malamin dake wa'azin tambaya akan ZINA. Malamin yace
"Lallai zina tana daga cikin manyan kaba'ira da Allah SWT Yayi hani dasu. Ban da lalacewar zamani yanzu da muka dauketa ba a bakin komai ba zaka ga yawanci duk addinin duniya yayi hani da zina saboda muninta da kazantar dake cikinta. A cikin suratul Furqan ayoyi na 69 zuwa 71 Allah Yana cewa
*WADANDA BASA DAUKAN WANI BAYAN ALLAH A MATSAYIN UBANGIJI KUMA BASA KASHE RAI BA BISA SHARI'AH BA, KUMA BASA ZINA WANDA DUK YA AIKATA HAKA ZAI SAMI ZUNUBI DAIDAI AKIN DA YAYI*.
*ZA'A NINKA MASA AZABAR RANAR ALKIYAMA KUMA ZAI KASANCE A CIKINTA HAR ABADA*.
*SAI WANDA YA TUBA KUMA YAYI IMANI KUMA YA AIKATA AIKI MAI KYAU, WADANNAN SUNE ALLAH YAKE CANZA MUSU ZUNUBANSU ZUWA GA LADA. ALLAH MAI RAHMA NE MAI JINKAI* Abin duba a nan shine an lissafa zina da ayyuka masu matukar muni wato shirka da kisan rai ba tare da hakki na shariah ba"

Haka malamin ya cigaba da janyo ayoyin AlQurani da hadisan Annabi SAW wadanda suka yi hani da zina ko azabar dake jiran masu yinta.

Ya kawo aya ta 32 a cikin Sural Isra' wadda Allah Madaukakin Sarki Ya umarce wadanda suka yi imani da kada su kusanci zina.

Sai aya ta 2 a cikin suratun Nur wadda Allah SWT Yake cewa: *MAZINACIYA DA MAZINACI IDAN SUKA YI ZINA KU BULALI KOWANE DAYA DAGA CIKINSU BULALA DARI. KADA KUWA WANI TAUSAYI YA KAMAKU GAME DA TABBATAR DA HUKUNCIN ADDININ ALLAH IDAN KUN KASANCE KUN BADA GASKIYA GA ALLAH DA RANAR LAHIRA. KUMA LALLAI NE WATA TAWAGA DAGA MUMINAI SU HALARCI WURIN YI MUSU HADDIN*

Abubakar da Qasim duk hankalinsu yana ga bayanin wannan malami. Duk su biyun jikinsu yayi sanyi musamman Abubakar da yasan abinda ya aika.

Malam mai wa'azi cikin bayaninsa ya kawo hadisin Bukhari wanda Annabi SAW yake cewa _MAZINACI BA SHI DA IMANI A LOKACIN DA YAKE AIKATA ZINA...._

Da wani hadisin na Abdullahi ibn Mas'ud  wanda yake cewa _MUN KASANCE TARE DA ANNABI SAW MATASA MARASA KOMAI NA DUKIYA_. _SAI ANNABI SAW YACE DAMU_:
_YA KU SAMARI, WANDA YA SAMI IKO A CIKINKU YAYI AURE DOMIN YAFI AKAN KARE KALLO DA MUTUMCI. WANDA BAZAI IYA BA SAI YAYI AZUMI SABODA ZAI ZAME MASA KARIYA._

Kallon kallo ne ya koma tsakanin Abubukar da Qasim a lokacin da malamin ya soma bayanin lahira da tanadin da Allah SWT Yayiwa bayi masu biyayya da masu sa6o. Ya karanto ayoyin Suratul Haaqqa wurin da Allah SWT Yake fadan irin farincikin da masu aikata aiki nagari zasu shiga idan sun karbi littafinsu da hannun dama da tanadi mafi kyau da Yayi musu a aljannah. Da kuma tashin hankalin ma'abota sabawa Allah a lokacin da suka karbi nasu littafin da hannun hagu(Ya Allah Kasa bama cikinsu. Amin) da azabar da zasu tarar.

Duk da Qasim ya shiga tashin hankali da jin wadannan bayanai saboda abinda yake aikatawa na shafa jikin 'yan matansa saboda gusar da sha'awa, yayi matukar mamaki ganin Abubakar ya fashe da kuka. Dafa abokin nasa yayi yana cewa
"Ba kaine zaka yi kuka ba Abubakar. Ni ne ya kamata nayi kuka saboda nasan na sabawa Allah sosai. Irin wannan abin da na fada maka akalla nayi da mata wurin biyar."

Abubakar ya kalle shi hawaye na kwararo masa." Qasim nawa sabon yafi naka. Na cuci kaina na aikata zunubin da bana hangowa kaina komai sai azaba."

A tsorace Qasim ya dago kan Abubakar dake kallon kasa" ban fahimceka ba, kada dai kace maganarmu ta rannan tasa kaima kaje kayi romancing wasu. Na shiga uku, ai ni ne cikin matsala tunda duk wanda yayi umarni da mummunan aiki yana da zunubi kwatankwacin na wanda ya aikata kamar yadda yake ga mai umarni da kyakkyawa".
Dafe kansa kawai yayi yana tunanin wannan sabon tashin hankali da ya saka kansa a ciki.

Zuciyar Abubakar cike da danasani yace "Qasim zina nayi"

"What??? Abubakar garin yaya? Da wa?"

Sai da ya hadiyi yawu da kyar ya iya amsawa "Asmau".

Qasim yana girgiza kai yana karanto La haula...
"Marainiyar yarinya, wayyo Abubakar ni ne sila ko? Tun yaushe ne? Garin yaya ka aikata hakan kai da ka kusa aure? Idan aka gane fa? Ga mahaifiyarta mutuniyar kirki."

Tambayoyin da Qasim keyi shima Abubakar din sune suke masa yawo a kansa. Yana hawaye ya sanar da Qasim abinda ya faru da irin kunya da bakincikin da ya sami kansa a ciki. "Yanzu shikenan nima da hannun hagu zan karbi littafi na ranar lahira. Lallai Annabi SAW yayi gaskiya da yace a hadisi na hudu cikin arba'una na Annawawi wanda aka karbo daga Ibn Mas'ud yake cewa ..
_......Hakika dayanku zaiyi ta aikata aiki irin na 'yan aljannah har sai ya kasance tsakaninsa da ita bai wuce zira'i ba sai littafinsa ya rinjaye shi sai ya aikata aiki irin na 'yan wuta sai ya shigeta...._

Qasim ya soma hawaye " in sha Allahu bazamu shiga wuta ba. Ka manta Allah Yayi alkawarin yafe zunubin masu tuba.?"

Sai da suka sha kukansu sannan Abubakar ya bawa Qasim wayarsa ya karanta wasu cikin sakonnin text da Asmau ta turo masa.

_Yaya Abubakar ka dubi girman Allah ka daga wayata. Kada ka gujeni a wannan lokacin_

_Idan ka rabu dani rayuwata bazata kara wani amfani ba. Me zan fadawa duniya nan gaba._

_Kai kadai ne zaka iya taimakona a wannan halin. Ka daure kada ka fasa aurena._

_Na amince ko washegarin aurenmu ne ka sakeni wallahi bazan yi korafi ba. Amma yanzu idan ka kini duk wanda ya aureni zai iya tona min asiri._

Kasa kara karatun Qasim yayi saboda tausayin Asmau da ya kama shi. Sun dauki wasu mintuna babu mai magana sai muryar malamin nan kawai suke ji yana kara tsorata mutane game da aikata zina.

Qasim ya tashi tsaye yana kashe kayan wuta na dakin dake kunne "ka tashi mu tafi ka bawa yarinyar nan hakuri sannan mu san yadda zamuyi su Baba su amince a matso da bikin nan zuwa wata biyu tunda kace mai hayar naka har ya gama ginin da wuri."

"Kana ganin zasu amince? Wata hudu ya rage da 'yan kwanaki yanzu nace a maido shi baya?"

"A nawa ganin hakan ne zai kara kwantarwa Asmau da hankali tasan cewa da gaske bazaka gujeta ba. Wallahi Abubakar ban taba zaton   zamu wayi gari mu ga rana irin wannan ba. Ba don da bakinka ka fada min ba Allah bazan taba yarda ba."

Rufe dakin suka yi sannan suka fita zuwa motar Abubakar. Qasim ne zai tuka su. A hanya suka sami masallaci sukayi sallar juma'a sannan suka wuce Kano suna ta tattauna yadda zasu bullowa su Baba domin su yarda a dawo da bikin baya. Kafin su rabu sai da Abubakar yasa Qasim yayu masa alkawarin wannan zancen zai zama sirri a garesu har mutuwa.

*****
Ko gida Abubakar bai shiga ba yana sauke Qasim ya tashar unguwar kabuga zai wuce Shanono, gidansu Asmau ya wuce kai tsaye. Lokacin Umma na wurin aiki ita kuma tana daki tana sana'ar kuka. Ta gama sawa ranta Abubakar ya gujeta kenan yanzu abinda ya faru matsalarta ce ita kadai. Jafar ne ya buga mata kofar daki ya sanar da ita zuwan Abubakar.

A zabure ta tashi ta lulluba mayafi ya rufe mata rabin fuska ta fita ta same shi a wurin da Umma ke ajiye mota.

Tana zuwa gabansa bata yi la'ari da cewa wani zai iya ganinsu ba ta zube gwiwoyinta a kasa tana kuka mai sauti.
"Don Allah Yaya Abubakar kada kace kazo rabuwa dani. Gara na mutu da in ga ka juya min baya a wannan yanayin."

Waigawa yayi ya tabbatar babu mai ganinsu sannan yayi mata alama da ta tashi. Shima hawayen yake shirin yi.
"Asmy kiyi hakuri ki yafe min. Naci amanarki na cutar dake. Amma ina so kisan cewa bazan gujeki ba. Wannan tsautsayin ni ne na tilasta miki saboda haka tare zamu fuskance shi. Idan kin amince zanyi magana a gida a dawo da bikinmu nan da wata biyu".

Wani hawayen ne ya sakko mata ga dariyar farinciki duk a lokaci daya.
"Da gaske? Wallahi na amince. Na yarda. Nagode Yaya Abubakar."

"Ki dena yimin godiya. Ni dake duk bamu fi karfin kaddara ba. Kuma kowane bawa akwai irin jarabawarsa a duniya. Dama Annabi SAW yace _Shaidan yana gudu a jikin mutum kamar yadda jini yake yi._
Kinga ashe bamu fi karfin fadawa tarkonsa ba. Sai dai Ubangijinmu mai rahma ne da gafara. Idan muka tuba sai kiga kamar ba'ayi ba."

A sanyaye yake maganar ciki da nadama.

Daga wannan lokacin suka fara azumi da tashi cikin dare neman gafarar Allah. Yaso samun matsala da su Baba amma daga baya sun amince an matso da auren. Tun daga lokacin Asmau take bashi girma fiye da na da, tsoro take yi kada ta kuskure yace ya fasa asirinta ya tonu.

Haka lokaci ya tafi har zuwa bikinsu da abinda ya faru bayan nan.

*****
*CIGABAN LABARI*

Asmau ta share hawayenta bayan ta gama bawa Zubaida labarinta. Ita ma Zubaidan kukan take yi na tausayi ga bakuwar da kwanansu daya da haduwa amma jininsu ya hadu.

"Tabbas kinga tashin hankali a rayuwarki Asmau. To amma abinda ya daure min kai shine yadda kuka tuba amma duk da haka kika tsinci kanki a irin wannan rayuwar".

Dan murmushi Asmau tayi "Zubaida kenan, tubanmu ba shi zai hana faruwar kaddarar rayuwarmu ba. Komai da kika gani ya faru ga bawa rubutaccen al'amari ne tun kafin zuwansa duniya. Wani abin yana faruwa ne domin ya zama darasi ga wasu don su kiyaye. Ni bana bakinciki da ikon Allah. Nasan bazai barni na tabe ba albarkar Annabi SAW."

Zubaida ta gyada kai ta gamsu da bayanin Asmau.
"Allah Ya jikan Abubakar"

Asmau tace "Amin " tana share kwalla.

Saturday, 14 January 2017

Silar Ajali

Silar Ajali
Alkalamin SAFIYYAH UMMU-ABDOUL

BABI  NA DAYA

Kwance ta ke kan gadon karfen ta, zuciyarta na bugu fiye da bugun sa, cikinta na murɗa mata tamkar mai shirin  gudawa, duk da haka kwakkwaran juyi ma kasa yin shi ta yi,  tsoro ne fal a cikin ranta Kasancewar ba ta san abinda daren yau zai zo mata da shi ba .

Da ya ke wata ya kai ashirin da shida, duhun daren ya wuce misali,  gari yayi baki kirin ko ganin tafin hannunta bata yi. Sassanyar iskar bazara da ke kaɗawa,da kuma kugin iska da ke tashi daga rassa da bishiyoyin kankarar bai hana zufa keto mata ta koina daga jikin ta ba, sai ma tsoron da ya ke daɗa shiga cikin ran ta don har ganin kamar gilmawar inuwar mutum take hakan ya sa ta kara gimtse idanunta gam, don bata ma son tsautsayi ya sa ta buɗe su. Duk da dai ba ta san takamamman lokaci a yanzu ba, ta san dai akalla karfe ɗaya na dare zai yi.

"Ba shakka ya kusa zuwa, yanzun kuwa zai zo"

Ta faɗa a ranta don kuwa kusan sati daya kenan a jere ya kan zo mata Idan ta na bacci sai dai kawai ta ji hannaye na bin kafar ta ko ma jikin ta, da fari ta yi zaton ko tunanin ta ne ko kuma aikin aljanu ne, sai da ta kama hannu ta rike kamin ta tabbatar da mutum ne ba aljani ba.

Ko da ta fadawa Yagana, wato babbar ɗiyar kanwar mahaifiyar ta wacce ta ke hannun ta, ita kuma ta ba ta shawarar ɗaukar mataki.

Jin kamar an tura kyauran ɗakin, gaban ta ya faɗi , ta yi karfin halin daɗa jawo goran da ta ajiye kusa da ita hannu na rawa, sannan ta yi lamo kamar mai bacci. Kusan minti goma ne ya shuɗe ba tare da ta ji wani abu ba, har ta fara tunanin tsoronta ne kawai, ilai kuwa sai hannu ta ji yana shafar kafar ta, daskarewa tayi a nan wajen don kasa numfashi tayi tsabar firgita, ji ta ke rayuwarta ta zo karshe don duk tattalinta wani na shirin wargaza mata rayuwa duk da karancin shekarunta.

Ta na jin hannun na shafa ta, har aka zo ga cinyarta, ganin hannun na yin gaba-gaba fiye da kullum ya sa ta yi saurin ɗaga sandar ta rantama dai-dai saitin da take tunanin mai hannun na wajan.

Ta ko ci sa'a dan kuwa ihu ta ji an saki, hannun na rawa ta ɗauki fitilar toci ɗin da ta b'oye karkashin matashin kai ta  kunna don ta tabbatar da muryar da kunnuwanta suka jiyo mata. Kunnawar da tayi yasa hasken ya garwaya  ɓangaren da ta haska cikin ɗakin.

Nan take idanun ta suka sauka a kansa in da ya ke kwance ya na burgima, jini ya wanke fuskar sa sanadiyar fasa masa kai da ta yi. Ganin hasken ya sa shi tashi zai fice a guje.....kan ya kai ga bakin kofa,  ya ji muryar ta da ke kakkarwa, cike da mamaki ta ke furta

"Baba.....Baba...Baaaaba"

Dakatawa yayi, sai da yai jim na wasu dakiku kana ya juyo ya na mai watsa ma ta wani irin mugun kallo, nan ta kara tsorata ganin irin raunin da ta ji masa, sannan ya fice da sauri.

   Cike da tsoro, ta kasa ko motsa yatsanta balle ta nemi tashi daga inda ta ke dan kuwa sam ba ta yi zato ba, ba ta taɓa tunani ko kawo abin cikin zucuyar ta ba

"Baba!  Baba!!!!! Baba fa......."

Abin da ta ke ta maimaitawa cikin zuciyar ta kenan amma kwakwalwarta ta kasa ɗauka, don kuwa idan har Baba zai iya aikata mata wannan mugun aiki haka, toh wa za ta yarda a duniyar nan?
  
                         ***

   Washagari da asubar fari ta ji hayaniyar Baba da Inna, wacce ke cikin ɗanyen jego, hayaniya ce ke  tashi daga tsakar gida wanda ya sa Sauran mutanen gidan firfitowa don jin ba'asi da samun rahoton kai wa gaba,  abinka da gida ba su kadai ba, gida na haya mai ɗauke da ɓangare ɓangare har goma.

Hakan bai sa Baba ya sassauta ko ma ya dai na kururuwar da kumfar bakin da ya ke ba, Jin ana buga qyauren ɗakin da ta ke, ya sa ta tashi da sauri ta na mai raba idanu.

   "Za ki fito kokuwa sai na shigo na fito da ke yar nema gantalalliya"

Faɗin Baba kenan ya na mai kumfar baki da haki kamar in ta qara wasu mintoci zai ɓalle kofar ne ko ma fushi ya kai shi ga rusa ginin  gaba xaya. Jin haka ya sa ta fitowa da sauri zani a hannu ko ɗankwali bata tsaya ɗaurawa ba.

Baba ta gani tsaye bakin kofa, Inna rike da jinjirinta ɗan sati biyu tsaye ta na zubda hawaye, ga kuma sauran yaran Inna biyar,suma ɗin kuka su ke, duk da dai kananun ba wani fahimtar abin da ke faruwa su ka yi ba, ganin hawayen Inna ya sa su kuka. Sai kuma sauran jama'ar gidan da su ka fito jin kwakwaf.

   Ba kunya ba tsoran Allah Baba ya dube ta yana mai mazurai tare da faɗin

"Faɗa mu su da bakin ki, abin da ya faru jiya"

Da sauri ta ɗaga ido ta kalleshi, duk da dai yarinya ce qarama ta san a iya tunanin ta wannan ba magana ba ce da za'a yi ta gaban jama'a ba, dan haka sai ta yi saurin yin qasa da idanun ta,ta ba tare da tayi magana ba. Shi kuwa Baba dama abin da ya ke so kenan, dan ya san a zahiri ba za ta iya buɗe baki a cikin jama'a haka ta tona masa asiri ba, dama da gangan ya tambaye ta dan ya samu ya ɗaure ta da hakan.

Tun da hakan sa ya cimma ruwa, buɗar bakin sa sai cewa yayi

"shegiyar kaya, dama ai ba kya iya magana ba! Toh ke Amina (Inna) ga ta nan, dama na faɗa mi ki in dai wannan hatsabibiyar yarinyar ce sai ta sa ki kuka da idanun ki, gashi tun ba'a je ko ina ba ta nuna halin ta, yanzu sai ki tasa ta a gaba ta miki bayanin gun wa take zuwa duk tsakar dare na duniya, sati guda kenan ina ganin ta, jiya da daddare ko da na bi ta a baya, saɗaf saɗaf na ga ta buɗe kofa  ta fice. Ban yi kasa a gwiwa ba na bi bayanta, don ni a gani na yarinyar nan amana ce gun mu, ko ma menene ya same ta mu mu za mu ji a jiki, ashe yarinyar nan fako na ta ke, ta haɗa baki da kwarton da ta ke gani, ban ankara ba sai saukar gora na ji bisa kai na, ku duba ku gani ya fasa min kai........"
Ya qarasa yana mai fashewa da kuka.

Gaba ɗaya wajen ya kaure da hayaniya, kowa na faɗan albarkarcin bakin sa, wasu na faɗin za ta aikata, wasu kuwa faɗi suke abin da mamaki, dan kuwa yarinya dai natsattsiya ce, kuma dai mutum babba kamar Baba ba zai yiyu ya yi karya ba.

Ita kuwa don mamaki kasa magana ta yi, baki na rawa ta ke duban Baba da ke ta faman kukan munafunci. Inna ce wacce ta kasa gane komai, ta ce da ita ta shiga ɗakin ta, yanzu za ta biyo ta. Ta juya za ta shiga kenan Baba ya yi saurin dakatar da ita ta hanyar tare hanyar da za ta kai ta ga ɗakin ya na faɗin

"Lillahi warasulihi yarinyar nan sai ta bar min gida a yau! ke ba ma ita ba, har sauran shegun yan uwan na ta!"

Jin haka Inna na fidda kwalla ta ce
"Shegu fa ka ce Malam! yanzu yaran yar uwar tawa ce kake kira da shegu, wani asiri naka ne bata rufe ba?"

Ya shiga kif-kifta idanu ya ce

"Su kuwa, na ce wanene uban su? ko kin taɓa ganin sa bayan ga labarin kanzan kurege da ta aiko mi ki na ta yi aure a Saudiyya, ta auri ɗan Sudan, sai kuma bayan shekaru biyar ta turo miki yara har uku, wai saboda tsada da wahalar rayuwa ki rike mata su,  ina ki ke da tabbacin da gaske auren ta yi? idan auren ne uban su ko dangin sa su riqe mata su mana! wallahi sai sun bar min gida! su je can idan ma hali irin na uwar ta ta za ta yi ba dai a gida na ba!" ya na faɗin haka ya rufo kofar ɗakin Inna.
    Kuka Inna ta sa, dan kuwa ya kwance mata zani a kasuwa, haka ma yarinyar da tabbas ko Baba bai ce su bar masa gida ba ta san zaman gidan dai ya kare musu, ba ma gidan ba garin kano gaba ɗaya, dan kuwa dai ta san kafin gari ya waye tuni sunan su da aka san su da shi zai ɓata a koma kiran su da shegu. Da wannan ɗacin a ran ta juya a guje ta shige ɗakin ta, ta shiga haɗe yan kayan ta cikin Ghana must go, ta na yi ne ta na kuka har ta gama haɗa kayan,  ta zauna a saman jakan kenan sai ga yan uwanta maza biyu sun shigo, babban wanda kallo ɗaya zaka masa ka san ya girme mata,  shi ke dauke da jakan kayan su, karamin da ko gama watsakewa bai yi ba fuskar sa duk  yawun bacci ko ina ya ce da ita

"Didi wai Baba ya ce mu bar masa gida, ina zamu Didi? Ko wajen su Mama za mu?yaushe za mu ga Mama Didi?"

Ya fashe da wani sabon  kuka mai. Karya zukata. Hannun sa ta ja ta na mai faɗin

"Kar ka damu autan, Allah shi ne gatan mu"

Babban kuwa bai iya furta komai ba, jakan hannun ta ya karɓa su ka fito tsakar gida in da Baba ke tsimayen su, haka ma sauran yan gulma. Ga shi dai an tada sallar asuba amma gulma ya hana su zuwa masallaci.

     Gaban Inna ta je ta durkusa, ta na mai neman gafara. Ganin haka shima karamin yayi hakan yayin da babban ya kara rike hannun jakan tare da sunkuyar da kanshi  don baya so kowannen su ya ga rauninsa. Inna na kuka ta rungume ta,kana ta ce da Baba

"Malam ka yi wa Allah ka yi hakuri ka bar yaran nan"

Baba ya gyara tsayuwa sannan ya ce

"Kin san Allah,wallahi sai sun tafi,yanzun nan ma kuwa!"

Nan fa mokota su ka yi yunkurin sa baki, amma Malam yayi kyememe ya hana. Inna ta kwance gefan zanin ta,ta fiddo da kuɗin cinikin ta na daddawa ta mik'a masa , kana ta ce

"Gashi kuyi kuɗin mota zuwa Katsina sai ku je MARKE,  ku je wajen salame  kun san ko da ace kowa zai guje ku salame ba za ta taɓa guje muku ba don ita ta haifi uwar ku, akwai wasu dangin mu a nan unguwar Gwammaja, amma ban san tak'amamman in da su ke ba, da can zan ce ku je ku neme su, Allah ya fishe ku alkahairi"

Hannu biyu ya sa ta karɓa, nan fa kowa ya shiga ba su abin da ba'a rasa ba, mai Ashirin, hamsin har naira ɗari. Inna ta k'ara rokon Baba da ya bari gari ya k'ara wayewa sa tafi,tun da yanzun asubahi ne. Maimakon ya amsa mata, sai ma tasa su gaba da yayi, Inna da yaran ta na kuka, haka ma yarinya da yan uwanta ta,har su ka fice daga gidan.
Sai da ya tabbatar ya raka su har bakin titi kafin ya juya ya bar su cikin halin ko in kula. Babban ne ya dubi yarinya ya kira sunan ta da
"Salma"

Ta na me goge hawaye,ta amsa da

"Na'am, Ya Salman, wallahi Baba sharri ya ke min, shi ne fa duk dare sai ya shigo min ɗaki....."

"Yi shiru da maganar nan Salma, za mu yi ta amma ba yanzu ba, tun da kin tsira da mutuncin ki shikenan ai,kan sa ya yiwa. Yanzu ɗaura kayan ki bisa kan ki, bari na goya Suhayl, dan mu yi sauri, kin ga mik'ak'k'iyar tafiya ce a gaban mu, Allah ya taimake mu, mu sami mota tashin farko a tasha" Da wannan Salma ta aza kayan ta bisa kan ta, Suhayl a bayan Salman, ga kuma sauran kayan na su a hannun shi, su ka sa hanyar tasha a gaba. Tun gari na da sauran duhu har gari ya waye tangararan.

    Ba k'aramin tafiya su ka yi ba kafin su k'arasa tasha. Duk da safiya ce tashar ba laifi akwai mutane da dan dama, ga motoci jere direbobi sai ihun neman passenger su ke, ga kuma yan kabu-kabu da dako, wanda da sun ga mutum ɗauke da kaya sai su yi kan sa da sauri su na mai riga-rigen karɓan kayan domin yin dako. Haka kuma yan tallan abubuwa Iri-iri kamar su koko, gyad'a da dai sauran su, da kuma mai tuyan kosai.

  Ganin su Salman ɗauke da kaya yan dako su ka yi kan su da sauri. Salman ya dakatar da su ta hanyar ɗaga musu hannu ya na mai faɗin

"ku bar mana kayan za mu iya d'auka"

Jin haka su ka bar su da kayan su suna masu faɗin

"Dan bakin ciki sai ku rike tsiyar ku ai!"
   Wani ne ya k'araso gare su ganin sun yi cirko-cirko tsakiyar tasha, ya na duban Salman ya ce yaro ina kuka nufa ne? Buɗarbakin Salman sai cewa yayi "MARKE aka ce mu je, cikin garin Katsina" kai mutum ya gyad'a ya ce motar Katsina  za ku hau kenan, golf za ku hau ko bus?golf dai dubu ɗaya ne ko wani mutum ɗaya , bus kuma ɗari biyar.

Ba tare da wani dogon tunani ba Salman ya bashi amsa da

"Bus din zai fi"

Dan kuwa ya san nauyin aljihun su ba lalle kuɗin da ke hannun su ya kai su ga hawa bus din ba. Mutumin ne ya kai su har bakin bus ɗin, in da ya umarci Salman da ya kawo kuɗin motar na su. Ko da ya haɗa ɗan kuɗin da ke hannun su sai ya ga dubu ɗaya ce cis. Ya nemi a musu ragi mutumin nan yak'i, dan kuwa haka su ke karbar kudin kowa. A k'arshe dai sai kuɗin maneji ya biya mu su ɗari uku-uku, sannan su ka sami matsuguni cikin motar.

Ɗarin da ta rage a dole ya siya mu su k'osai da pure water, dan kuwa yunwa su ke ji, bare Suhayl da tuni ya fara mu su kukan yunwa dan kuwa ba ya jure yunwa.

   Sai da motar ta yi awa ɗaya har da ɗoriya kafin su gama lodi a ɗau hanya. Zaman na su Salma sam ba daɗi sun takura kwarai, jere su ke kan maneji, kafafun su a takure ga wani turiri da ke tashi ta tankin motar, ga shi mai motar ya kwashi mutane da kaya da ya fi karfin motar. Ga haniya da kukan yara da ke tashi ciki, amma hakan bai hana Suhayl gyangyad'awa, shi kuwa Salman gaba ɗaya tunanin sa ya ta'allaka ne kan yanda za su yi su je MARKE neman dangin mahaifiyar su, idan suna da rai kenan,  ko da yake baba salame na nan a raye.

Tafiyar awa biyu sai da su ka yi ta awa uku, saboda lodi da rashin gwabi na motar, ga kuma hanyar ba kyau. Isar su Katsina a babban  tashar garin aka sauke su. Tashar cike ta ke fam da jama'a, matafiya da wanda su ka iso, yan talla da yan dako, jami'ai ma su kula da tashar, almajirai da kuma yan zaman banza. Hayaniya da cikowa na jamar tashar ba karamin firgita Suhayl ya  yi ba, tuni ya kudunnune rigar Salman idanun sa na shirin kawo ruwa. Su kan su Salman da Salma hankalin su ba kwance ya ke ba, musammam ganin yanda yan dako ke ta kawo mu su harin daukar kayan su, Salman na hanawa, haka kuma masu abin hawa na ta mu su tayin hawa babur din su, wanda  ke kira "Adaidaita Sahu" amma su ma din sun ki yi.

   Sai da ya ga jama'ar sun dan sarara, tukun ya tsada wani dan saurayi ya na mai tambayar hanyar da za su bi ya kai su ga unguwar Marke.

Saurayin ya na mai duban sa ya ce
"da gani dai ku baki ne,  MARKE ai gari ne chan a karamar hukumar Dan Musa,  ko daga nan zuwa chan ai awa biyu ne, ba motar Katsina ya kamata ku shigo ba ai don kuwa da ta hanyar Gwarzo zaku bi sai Dayi junction daga nan sai ku biyo ta Gora zuwa kankara daga Kankara sai Yan tumaki,  sai Danmusa,  yanzu kun san inda zaku shiga motar?" ya tambaya yana mai kallonsa

Salman ya girgiza kai sannan ya ce "Ah ah,a kasa za mu je ai,hanya kawai mu ke so a nuna mana"

Dariya saurayin yayi, har da kyakyacewa kafin ya ce "Gaskiya ne mutumin kauye, ka tabbata bako a garin nan shi ya sa ba ka san girma da fad'i irin na jihar Katsina  ba, kai idan ka ce za ka silafa har MARKE da k'afa kai kaɗai ma ba tare da yan uwan nan na ka da kayan nan ba, ace ka fita tun safe ba ka isa ka kai marke  ba sai ka wuni  ka kwana a hanya, bare kuma da su, ai sai kun yi kwanaki! Kai ni ina da abin yi, in da za ka rage ciki ka biya a kai ku toh, ni ka ga tafiya ta!"

Su na ji suna gani saurayi ya wuce su ya na mu su dariyar kyeta. Salman ya yi jigum ya zubawa sarautar Allah ido. Ga wata rana da ake zubawa wanda ta haddasa mu su azababban k'ishin ruwa. Ga shi kuma ko karyawar kirki ba su yi ba, shi kan shi Salman bakar yunwa ce ta sa cikin shi a gaba, bare Suhayl da Salma. Ilai kuwa nan take Suhaly ya sa mu su kukan yunwa. Salma ce mai iya rarrashin sa, shi kuwa Salman wajen ɗaya daga cikin masu yunifon ɗin yuniyo ya isa, ya nemi da ya taimaka  ya kai su marke, amma fa fisabilillahi, dan kuwa kwandala ba sa magani. Cike da takaici ɗan yuniyi ya fatattake shi, ya na mai zargin sa da mutuwar zuciya, matashin yaro kamar shi ya ce a kai shi har marke a kyauta!

Da dai Salman ya ga babu sarki sai Allah, inuwa ya ja su Salma da Suhaly din da har lokacin be daina kukan yunwa ba, ya ce su zauna su jira shi, kada Salma ta yarda ta kula kowa, ta kula da Suhaly, bara ya je ko dako ne ya yi, sai ya samo mu su na abinci da ma na mota gaba ɗaya. Da haka ya bar su zaune, ya kutsa cikin tasha. Ya ci sa'ar samin dako har sau biyu, ana ba shi naira hamsin,domin kuwa tashar cike take da yan dako ko ta ina. Da ya sake gwada sa'ar sa be samu ba, sai kawai ya k'arasa wajan mai abinci ya siya mu su shinkafa da wake, wajen mai abuncin ya tsinci gorar ruwa mai tambarin faro,ya d'auka ya d'auraye. Ciki ya taro mu su ruwan sha.
  Ganin abincin ba karamin murna Salma da Suhayl su ka yi ba, kan kace mai tuni sun far ma abinci. Ganin ba zai ishe su ba Salman ya bar musu su ci su biyu, ya sake kutsawa cikin tasha, ya na mai fatar barin tashar kafin la'asar, azahar har ta kawo kai, gashi zaman Salma cikin tashar ke ɗaga masa hankali, dan kuwa mutane ne iri iri ciki, ba ka san waye mugu, waye na gari ba.

   Lokaci lokaci ya ke samin dako,ya na yi ya na duba su Salma, a haka har azahar ta yi, ya sa su ka yi sallah. Kan la'asar ta k'arasa kuwa Allah ya taimaki Salman ya had'a kud'in sa har d'ari biyar da hamsin. Ya na mai share zufar da ya haɗa ya ke tsadancewa da ɗan yuniyo din Ɗazu don a ɗauke su a maneji, wanda shi kuma ya dage a lalle sai dai Salman ya biya shi d'ari uku, a hakan ma wai sauki ya masa. Da kyar da magiya, Salman ya masa bayanin halin da su ke ciki, sannan ya yarda za'a kai su din a d'ari biyu. Su ka jera kayan su a baya, Salma ta fara shiga, Sahayl ya bita sai Salman a kusa da kwansasta. Nan direba ya tayar da mota kasancewa motar ta cika, Salman na mai sauke ajiyar zuciya.