Friday, 13 January 2017

Abin da ake gudu 17

ABINDA AKE GUDU🙆🏽17

Batul Mamman💖


Kafin ya fito ya kira Asmau a waya ya sanar da ita zai zo. Jikinta a sanyaye ta amsa masa don ita yanzu kunyar ganinsa take yi. Ko ba'a fada ba daga nasihar Anti Bintu tasan cewa duk abinda ya faru laifinta ne.

Har daki taje ta sanar da Anti Bintun zai zo kamar yadda ta saba.
"Ki dora abinci dashi amma ki bar dan waken sai gobe don bazan bawa suriki dan wake ba"

Ita da Asmau duk dariya sukayi sannan ta wuce ta dora shinkafa da miya.

Wuraren karfe uku ya iso Anti Bintu tazo suka gaisa sannan ta basu wuri.

Yau Asmau hijab ta saka dogo har kasa fuskarta babu kwalliya sai hoda da kwalli. Jikinta duk babu kwari tayi nadama sosai. Abubakar kuwa tamkar ya hadiyeta da kallo. Anyi sa'a yaran gidan suna ta gilmawa a falon. Da laasar suka tafi islamiyya  shi kuma yaje yayi sallah.

Ana idarwa ya dawo ya kalli Asmau dake zaune a can gefe.
"Asmy dawo nan kusa dani nafi jindadi". Ya nuna kujerar gefensa.

Tashi tayi kamar wadda kwai ya fashewa a ciki. Tana zama ya kama hannunta ya rike yana lumshe idanu. Can kasa take jin muryarsa
"I love you so much Asmy. Ina ma anyi aurenmu kiga irin abinda nake nufi."

A kwanakin baya har so take ya rike mata hannu amma yau sai taji ta tsani hakan. Tana son nuna masa kuskuren abinda tasan ya fita sani amma dole tabi lamarin a hankali kada yayi mata mummunar fahimta ko yace ta mayar dashi dan iska.

Har lokacin tafiyarsa yayi bata iya sakin jiki dashi ba. Shi kuwa gabadaya ya kasa samun nutsuwa. Bakin motarsa da ya ajiye a wajen gate ta raka shi ai kuwa yana bude motar ya rungumota jikinsa. Dama layin ba mutane sosai  saboda unguwar bata gama cika ba ga duhun dare.

Wasu hawaye masu zafi Asmau taji sun taho mata ta hadiye. Dole ta sami lokaci suyi magana da Abubakar akan wannan abin. Rungumar da take jindadi daga gareshi yau bata so. Tana wannan tunanin taji yayi mata abinda bai taba yi ba. Abinda take ta mararin faruwarsa. Bakinsa ya hada da nata yayi mata rikon da bazata iya kwatar kanta ba koda tayi niyya.

Hawayen da take boyewa ne suka sakko ganin Abubakar tamkar baya cikin hayyacinsa. Abubuwan da yake  mata sun fara wuce gona da iri. Ba shi ya saketa ba sai da don kansa yaji hankalinsa ya fara dawowa gareshi.

Ganin tana kuka ya soma bata hakuri.
"Asmy kiyi hakuri please. Na rasa dalilin da yasa nayi miki hakan. Ki sani ina sonki tsakani da Allah kuma in sha Allah bazan sake kwatanta miki haka ba sai munyi aure".

Yadda yake maganar sai ya bawa mutum tausayi. Tabbas baya son abinda yake yi sai dai karfin sha'awarsa da tsananin rudin shaidan yasa ya kasa hakuri.

A hankali ta share idonta "Yaya Abubakar don Allah mu dena irin wannan abin kaga babu kyau."

"Na sami Asmy, ni kaina na rasa gane yadda akayi muka fada ga  wannan masifar. Ki share idonki kinji matar Abubakar".

Kafin ya tafi sai gashi ta sake sosai hankalinta ya kwanta. Suka rabu zuciyar kowa tana nata sake saken.
*****

Abubuwan da suka gudana tsakanin Abubakar da Asmau su suka rinka yi masa yawo a kwakwalwa. Yayi tunanin zaiji saukin sha'awar dake damunsa sai abin yayi tsanani sosai. Kullum cikin mafarkinta yake yi. Baccin kirki ya gagare shi sai tunanin yadda zaiyi ko dai a matso da aurensu ko ya kashe yunwarsa ko sau daya ne.

A nata bangaren hatta hirar da suke yi a waya yanzu tana kame bakinta daga hirar da bata dace ba. Ta tarkarta tunaninta kaf zuwa lokacin aurensu ko sa sami nutsuwa da kwanciyar hankali saboda tasan duk su biyun yanzu a matse suke da ganin wannan lokacin.

Bayan kwana biyu ya sake zuwa wannan karon ko waya baiyi mata ba. A hirarsu da Anti Bintu ya nemi izinin ranar asabar da Asmau zata tafi zai zo ya kaita da kansa a cewarsa baya so ta shiga motar haya.

Anti Bintu tayi shiru na dan lokaci saboda ba haka sukayi da yayarta ba. Dama tasha za'a kaita ta tafi saboda motar Kawu Yusuf tana gareji wurin makanike. A duk dan tunaninta bata hango wata matsala ba duba da irin siffa ta kamala da suke dashi su biyun.

Asmau kanta bata ji komai ba saboda yau hirarsu duk irin ta da ce. Cikin nutsuwa da kiyayewa. Soyayya mai tsafta irin wadda masu yinta basa son rabuwa da juna.

Kwanaki ukun da suka zo kafin tafiyarsu Abubakar yaji babu dadi. Har wani zazzabi ne ya kamashi saboda ji yake tamkar ana hura masa wutar sha'awar kasancewa da mace. A yadda yake ji ko ba Asmau bace wannan karon zai iya nema.

Ranar da zasu tafi wurin karfe goma ya iso. Asmau da yaran harda dan kukansu na rabuwa.

Suna mota ita da Abubakar babu wata hirar kirki don basu taba kadaicewa a mota haka ba na tafiya mai nisa.

Hanyar cikin gari ya nufa ya kashe motar a gefen titi.  Asmau ta kalle shi zata yi magana sai ta kasa ganin idanunsa sunyi wani iri kamar wanda yake cikin tashin hankali.

A raunane yake dubanta har sai da tsigar jikinta ta tashi don tsoro da ya dora hannunsa a kan nata.

"Asmau"

Yaushe rabon da ya kirata da sunanta haka. Gabanta na dukan uku-uku ta amsa.

"Idan na rokeki alfarma zaki yi min?"

Ita fa Yaya Abubakar tsoro yake bata da yanayinsa na yau.
"in sha Allahu idan baifi karfina ba".

Gwauron numfashi ya ja.
"Asmy ina cikin matsala kuma ke kadai ce zaki iya yi min maganinta. Ko sati ba'ayi ba da muka amince mun dena taba jikin juna.."

Bugun zuciyarta ne ya karu tana ganin kamar ta fara fahimtar inda zancensa ya dosa.

"Ni mutum ne mai yawan bukata, ina tsammanin baki san me hakan yake nufi ba."

A ranta kuwa tace sai dai na fadawa wani. Rabe-raben mutane ta fannin sha'awa tuni ta san shi a posts din waya. Muryarsa wadda take rawa taji a kusa da ita.

"Ina cikin tashin hankali da son kasancewa tare dake. Wallahi bazan iya kaimu Kano ba a yanayin da nake ji yanzu musamman da kike zaune kusa dani. Ki taimakeni ko sau daya ne na kawar da wannan masifaffen tunanin."

Kofar motar ta kama a gigice hawaye na wanke mata fuska jin ya saka lock. Sanyin AC bai hanata gumi ba.
"Yaya Abubakar ka rufa min asiri ka mayar dani gidan Anti Bintu. Duk ni na jawo wannan matsalar da na rinka saka kaya masu matse jiki ina zama kusa da kai. Sharrin shaidan ne da na zuciya don Allah kayi hakuri nan da wata hudu zamuyi aure fa".

Magiyar da take masa jin muryarta yake kamar tana masa busa. Wannan wace irin masifa ce??? Shiyasa tun a da yake nisanta daga duk abinda zai jawo masa sha'awa tunda ya gane yanayinsa.

Hawaye ne ya zubo a idonsa wanda bai san dalilinsu ba.
"Ke kadai nake so kuma da ke kadai na amince Asmy. Idan baki amince ba wallahi nayi miki rantsuwa zan nemi wata. Bani da lafiya duk a dalilin sonki da son kusantarki. Ko kinsan satin nan ko sau daya banje wurin aiki ba saboda halin dana tsinci kaina a ciki".

Kuka Asmau take yi sosai gashi tausayinsa ya mamaye zuciyarta.
" Yaya kada mu aikata haram. Kuma idan ka rabani da abinda duk budurwa take takama dashi yaya zanyi?"

Hannuwanta duka biyun ya rike. "Asmy kinsan dai nine mai aurenki ko? Kuma ni ba wai zanyi miki yadda zaki tashi daga budurwa bane. Akwai yadda zanyi babu wanda zai ce namiji ya kusanceki. Ki taimake ni.

Har bincike nayi wasu malaman sunce kudin aure daidai yake da sadaki. Ko baki ga iyayenmu maza ke zuwa ba ayi a gaban shaidu. Al'ada ce kawai sake taruwar da ake yi a daura aure. Amma yanzu ma a haka ni da ke matsayin mata da miji muke." Shi da yake fada mata hakan ya tabbatar karya yake yi amma babu yadda ya iya da zuciyarsa.

Roko da rarrashi haka ya rinka yiwa Asmau tana kuka haka ta amince saboda tausayin da ya bata da tsoron kada ya nemi wata.

Wani hotel ya sama musu kuma da yake duk sunyi shigar mutunci babu mai cewa ba ma'auratan gaske bane. Haka ya karbi mukullin dakin zuciyarsa tana kwabarsa da abinda yake shirin aikatawa amma gangar jikinsa bazata iya hakuri ba.

A kofar dakin da kyar Asmau ta shiga. Yana rufe kofar ta kara fashewa da kuka. Abubakar yayi nisa duk da yana tausayinta hakan bai hanashi biyan bukakarsa ba. Alkawarin da yayi mata na yin dabara kada ta rasa budurcinta tuni ya manta dashi.

Sai da komai ya kammala yaji kamar tashin hankalin duniya duk ya kare a kansa. Gefen gado ya koma ya dafe kai ya rasa inda zaisa kansa.

Asmau tana kwance sai sautin kukanta ke tashi. Ga ciwo ga bakinciki.

Sun kusa awa daya sannan yayi wanka ya umarceta da itama tayi. Wannan masifa da yawa take...Ya Allah Ka tsare mana imaninmu.

Haka suka fito babu wanda yake yiwa dan uwansa magana. Ya biya kudin hotel suka wuce Kano yana ta zabga gudu a hanya.

A bakin gate din gidansu ya sauketa zuciyarsa tana kuna. Ya rasa me yake ji game da Asmau. Ko kayanta bai taimaka mata da dauka ba haka ta fito dasu ta shige gida fuska a kumbure.

Su Umma sai murna suke yi ta dawo amma ganin yanayinta Umman ta tsorata tana tambayarta abinda ya faru.

Asmau ta fashe da kuka ta rungume mahaifiyarta. Yau taci amanar addininta kuma taci amanar Umma.

Taruwa suka yi a kanta Jafar ya taba jikinta. Zazzabi ne sosai a jikin hatta kanta ya dau zafi.
Ya danyi murmushi "Umma wannan 'yar taki ta fiye shagwaba da raki. Daga zazzabi kuma sai kuka?"

Sai a lokacin tayi dan murmushi ganin cewa idan ta cigaba da kukan zata tonawa kanta asiri.
"Yaya Jafar ji nake kamar kan zai tsage biyu"

Umma ta tasheta tsaye
"Ki dena tsorata ni irin haka Asmau. Baki ji yadda gabana ya fadi ba. Muje ki dan watsa ruwa sai kici abinci kisha magani. Ina Abubakar din?"

Har zuciyarta ta razana jin an ambaci sunansa.
"Ya tafi gida amma yace zai shigo ku gaisa anjima".

"Babu komai ai kun sha hanya ga rana. Allah Yasa ba kukan nan naki kika rinka yi masa ba saboda baki jindadi."
*****

Har washegari Asmau tana kiran wayar Abubakar saboda bai zo ba kamar yadda tayi tsammani. Babu waya babu text. Nata kiran kuma yaki dauka. Hankalinta yayi matukar tashi. Yanzu idan ya fasa aurenta saboda abinda suka yi yaya zata yi da ranta.

Shima a gida kwana yayi kuka. Idan yaga wayar Asmau ji yake kamar yasa ihu. Zuciyarsa ta kasa rabe masa haushinta yake ji don ta bashi kanta ko kuwa haushin kansa da ya tilasta mata.

No comments:

Post a Comment