Wednesday, 18 January 2017

Abin da ake gudu 20

ABINDA AKE GUDU🙆🏽20

Batul Mamman💖


Wani mugun fitsari ne ya tashi Asmau daf da kiran assalatu. Ta fito zata je bandaki amma ko ruwan tsarki bata dashi. Haka ta koma daki tana ta matse shi da adduar Zubaida ta fito da wuri ko dan yaya ne ta sammata. Har aka idar da sallah a masallaci Zubaida bata fito ba. Zuwa lokacin Asmau sai gumi take yi tana cilla kafa. A hankali taji ya fara zubowa dole ta tafi bandakin da gudu tayi batare da tayi tsarki ba. Haka ta dawo dakinta ta shafi kura tayi taimama sannan tayi sallar asuba.

Batun jin yunwa dama ba'a magana. Wannan yanayin da ta tsinci kanta a ciki hakurinta ya fara karewa. Ace tayi fitsari ko ruwan tsarki babu gashi tana gani amma gidan nafsi nafsi (kowa na ta kansa)kawai ake yi.

Yau Zubaida bacci sosai take yi don har tara ta wuce bata farka ba. Asmau ta gaji da jiran tsammami ta duba hijabinta wanda yafi kowanne dauda ta saka ta fita bakin titi. Ga rana ta kwale haka ta daure zuciyarta ta zauna duk wanda yazo wucewa tace.

_Sadaka fisabilillah_

Mutumin farko da ya bata naira goma yana yin gaba ta saka kuka. Wai ita da watanni kadan da suka wuce take cikin rayuwar jindadi tare da masoyinta da iyayenta, ita ce take bara tamkar mara galihu. Bara sana'ar da take tattare da kaskanci da mutuwar zuciya. A ranta addua take yi Allah Yasa mufi karfin zukatanmu Ya nesanta mu da kaddara mai muni irin wannan.

Ita kenan ma da tayi nadama amma Allah Ya zabeta don gwada imaninta da kuma nuna aya ga sauran mutane. To ina masu aikata zinar duk da sun san laifine amma basu dauketa a bakin komai ba. A ganinsu suna da sauran lokaci. Ina masu bada muguwar shawara a baki ko a rubuce batare da yin la'akari da tasirin da hakan yake yi a zukata masu rauni ba. Da Abubakar bai tuba ba shikenan haka mutuwa zata riske shi yana halin sabawa Mahalicci.

Taci kuka har ta godewa Allah a wurin. Har rana ta take naira hamsin da biyar ta hada. Ga jiri na dibanta saboda tsabar yunwa. Tashi tayi ta kama hanyar gidan da yanzu shine matsuguninta. A hanya ta sayi fanke na naira hamsin din da pure water guda daya.

Dakinta ta wuce wanda ko jawo kafar batayi ba. To me zata rufe bayan bata da komai. Fanken nan ta janyo tana ci hannu baka hannu kwarya. Ko uku bata ci ba sai amai ya taso mata. Dole ta hakura ta dan jingina da bango tana adduar kada ya fito don ta dan ji kwarin jikinta.

Ba don tana gudun mutuwar kafirci ba gani take yi a wannan lokacin gara ta mutu ta huta. Tana jin shigowar Uwargida ta tashi ta bita daki. Bazata iya cigaba da bara ba gara kawai tayi abinda zai fishshe ta a nata ganin.

" 'Yar Da6as yau tun safe kina ina?"

Asmau ta dan waiga bayanta tana dube dube.

Uwargida tace "indai Zubaida kike nema na kaita wurin uwargijiyata a wannan sana'a. Girma ya fara kamani dolenta ta nema mana kudi. Yaya Babba zata koyar da ita ta karfin tsiya sannan ta dawo gidan nan ta taimaka wurin dago darajarsa kamar da."

Tausayin Zubaida ya kama Asmau. Yarinyar da bata kaunar zaman gidan ma bare sana'arsu ace wai mahaifiyarta da kanta take son lalata mata rayuwa. Sai dai babu taimakon da zata iya yi mata yanzu. Kanta a kasa tace "idan kina da maganin zubar da cikin ki bani".

Wata shewa da tafi Uwargida tayi cike da murna. Tasan za'a rina. Wannan yanzu idan ta fara bawa Asmau abinci na sati tuni zata murmure ta fara caskar kudi da ita.
" kin taimaki kanki kuma na tabbatar bazaki yi dana sani ba muddin kika fara jin jakarki da nauyi. Bari na dauko miki wani jiko da na bawa Darling kwanaki."

Uwar dakinta ta shige ba jimawa ta fito da wata robar swan da ta dafe da datti. Ruwan ciki kore ne fatau ga wasu 'ya'yan ball suna ta shawagi a ciki. Asmau na ganin robar taji amai na yunkurin fitowa. Toshe bakinta tayi ta karbi robar ta fita bayan Uwargida tayu mata bayanin yadda zata sha.

Tun da ta ajiye robar ko kallon wurin bata sake yi ba. A matsayinta na wadda take da ilimi daidai misali tasan shan wannan kazantar babbar illah ne gareta.

Washegari wurin karfe goma ta tashi ta shiga cikin kasuwa. Tasha yawo sannan Allah Ya sa taga abinda take nema wato chemist(kemis). Daga saman an rubuta *SADA AND SONS CHEMIST*.

Mutane ne suke ta shige da fice a wurin ta rakube daga can gefe tana jira suyi sauki ta je ta roki mai kemis din ko zai taimaka mata da maganin zubar da ciki. Sama da awa daya bata ga alamun mutanen zasu yi sauki ba har ta gaji ta soma gyangyadi a gefen wani benci da aka ajiye a wurin shagon.

Cikin bacci taji an soma kiraye kirayen sallar azahar ta bude ido tana hamma sannan ta dan kalli kofar shagon ta ga akwai mutum daya a ciki har yanzu. Daga can nesa  ta hango wani yaro da kayan makaranta da flask din abinci ya nufo wurin shagon. Ta tashi ta kade jikinta da niyyar idan ya iso zata roke shi ko ya rage abinci ya bata.

Yana zuwa kuwa ta dan sauke murya.
"Don Allah in ka rage abincin makarantar ka bani in ci".

Yaron da zai kai shekara goma yana da dan jiki ya kalleta yayi murmushi
"Kwanon abincin makarantana na mayar gida. Wannan na babanmu ne na kawo masa".

Daga haka ya shige cikin shagon. Ba dadewa suka fito wurin 'yar rumfar kofar shagon inda bencin yake. Yaron ya ce "Baba kaga almajirar da tace na bata abincin naka".

Mal Sada mai kemis ya dan kalli Asmau. Tabbas babu wanda zai mata wani kallo daban da na almajira. Dogon mutum ne mai dan haske da kiba. Fuskarsa kadai zata nuna wa mutum yana da kirki.

Da hannu ya yafito wata mai awara yarinyar ta karaso da gudunta don kada 'yan talla 'yan uwanta su riga ta zuwa. Ya zira hannu a aljihu ya dauko naira dari ya mika mata.
"Zuba wa matar nan ta sittin sai ki bata canjin. Abba miko mata ruwa a cikin fridge dinnan guda biyu."

Mai awara da Abba suka yi yadda Mal Sada ya saka su. Asmau na karba ta rinka yi masa godiya da fatan alkhairi sai ka zata ta dade tana sana'ar bara.

Mal Sada ya dan daure fuska "nan ba wurin zaman almajirai bane kinji ko. Idan kin gama ci ki tafi."

Ta gyada kai ta koma gefe ta zauna. Da ledar ruwa daya ta wanke hannunta ta fara cin awarar cikin jindadi. Rabonta da abincin kirki ta kwana biyu. Tana gamawa tasha ruwa sannan ta dauki daya ledar ruwan tayi alwala ta shimfida dankwalinta tayi sallah. Lokacin tuni Abba ya tafi. Sada yana kallonta sai ta burge shi da bara bata hanata ibada ba.

Bayan ya dawo daga masallaci yana bude shagon kafin kowa ya shiga ta bi bayansa. Sai kuma kunya ta hanata fadin abinda ya kawota.

"Kina bukatar wani abu ne?"

Kamar mai rada tace "nawa ne maganin zubar da ciki?"

Cak ya tsaya yana kallonta. Wato ban da bara har jikinta take sayarwa. Ransa a bace yace "idan baki fice min daga nan ba ranki zai baci. Ku baro gidajenku kuna bara saboda mutuwar zuciya karshe almajirai da marasa zuciya irinku su rinka yi muku ciki. Ko ina dashi bazan bayarba."

Asmau ta soma kuka tana rokonsa ya taimaka mata.

Daga hannu Sada yayi kamar zai maketa shiyasa ta fita. Amma a kofar shagon nan ta zauna har taran dare lokacin da yake rufewa. Ko kallonta baiyi ba da zai wuce tana ta masa magiya.

Washegari tun kafin yazo shagon ta iso. Yinin ranar da ta ga babu mutane sosai sai ta shiga ta roke shi. Tun yana mata fada ta fita har ya dena kulata sai ta ga wani zai shigo ta fice a sanyaye.

Dansa Abba ya sake kawo masa abinci amma yau bai bi ta kanta ba. Yana ciki yana cin abincin ne ya jiyo kakarin amanta. Tun awarar jiya bata sake samun wani abincin ba.

Kamar ya share sai ta bashi tausayi ya dauko flask din ya mika mata. Idanunta sun kara fitowa waje sai hakora gayau kamar ta shekara tana jinya. Kusan fizgar flask din tayi ko wanke hannu bata yi ba ta soma cin abincin. Abinda bata taba ji bane ya faru a wannan lokacin. Motsi taji a cikinta wanda ya kara tabbatar mata lallai ba ita kadai take rayuwa ba. Yanayin da ta shiga da jin motsin yasa ta farinciki ta dafe cikin. Tunowa da Abubakar da halin rayuwarta kuma yasa ta koma yin kuka. Abincin da bata iya cinyewa ba kenan.

Da Sada zai tafi ta mika masa flask din yace ta rike ya bar mata. Yana kallonta ta tafi har ta bace masa.

*****
Sau biyu kenan Rashida tana fadawa maigidanta ta kai masa ruwan wanka sai yace to ina zuwa. A karo na uku ta zauna kusa dashi cikin damuwa.
"Baban Abba me ya faru ne? Allah Yasa ba laifi nayi ba."

Dan murmushi Sada yayi yana kallon abar kaunarsa.
"Ko kadan Maman Abba. Bari nayi wankan dai."

Sai da ya gama cin tuwo sannan ya bata labarin Asmau mai zuwa kofar shagonsa.
"Ni bansan daga ina take ba sai dai ta bani tausayi. Muna ganin kanmu kamar marasa arziki amma wallahi cikin rufin asiri muke akan wasu. Tsorona daya kada taje wurin wani mara imanin ya bata maganin."

Rashida tace "to ai dama kaine kullum kake ganin kamar shagonka kadai baya wadata mu. Amma gashi yara hudu duk suna makaranta kuma bama rasa abinci.
Idan bazaka damu ba gobe sai na kawo maka abincin da kaina na ganta. Kila idan  na bata shawara ta hakura da zubar da cikin ta koma gida".

*****
Asmau ta dauko robar da Uwargida ta bata. Tana son sha kuma har ranta bata son zubar da cikin. Dama gudun zubarwar yasa ta fito daga gida. Dan motsin nan da taji ya sa ta kara son abinta. Robar ta dauka ta zubar da kadan a bakin rariya sannan ta mayarwa Uwargida. Bakin Uwargida a washe tace
" nan da wayewar gari ma yana iya zubewa. Kinyi kyan kai 'Yar Da6as."

Yau ma ta riga Sada zuwa shagonsa. Ita kanta bata san me ya dawo da ita ba. Da yazo har kasa ta durkusa ta gaida shi. Ya amsa mata fuskarsa babu yabo babu fallasa. Yayi mamaki da ko sau daya bata sake batun maganin ba. Tana dai zaune ne kawai a gefe guda.

Wuraren shabiyu wata mace ta sha katon mayafi ta iso kafar shagon da flask din abinci. Matar tayi mata murmushi Asmau ta gaisheta. Sada ya fito daga cikin shagon yace "wannan ce yarinyar".

Rashida taji tausayin Asmau ba don komai ba sai don yanayin da ta ganta. Har wani wari take yi saboda rashin wanka. Sada yace su shigo ciki ya dan kara kofar alamun ko anzo kada a shiga.

Asmau na zaune a kasa a gabansu Rashida tace ta fada musu daga ina take kuma ina uban dan dake cikinta.
"Kada kiyi mana karya domin kuwa Allah Yana kallonmu".

Karo na biyu kenan tana bada labarinta. Kafin ta gama Rashida tayi ya6e ya6e da hawaye don tausayi. Mata da yawa idan an tambayesu game da ciki a irin wannan yanayin sai suce fin karfi aka yi musu. Amma wannan yarinyar ta zabi ta fada musu abinda suka fi tunanin gaskiya ne. Wato biyewa rudin shaidan da son farantawa masoyi. Shi kansa Sada yaji tausayinta matuka. Lokaci guda tarbiyarta ta wargaje a dalilin kawa da kafafen sada zumunta.

Waje suka ce ta fita ta jira su. Muhawara sukayi inda yace su mayar da ita gida Rashida tace kada ta koma sai ta haihu ta yiwu iyayen su yafe mata idan suka ga dan a hannu. Duk da suna tsoron halin Dan Adam yanzu. Kayi masa rana yayi maka dare amma zukatansu sun amince da taimakonta musamman ma suna jin tsoron kada ta zubar da cikin ta fada sana'ar banza.

Sada ya rufe shagon suka ce ta biyosu. Babu musu tabi bayansu tana adduar Allah Yasa alkhairi ne a tattare da mutanen.

No comments:

Post a Comment