Tuesday, 19 September 2017

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) 17

®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

1⃣7⃣

Sidiya ce...✍🏼




Bintu na k’arasa magana ta shige uwar d’aka. Baiwa kuwa tashi ta yi cikin jinjina maganar ta na mai gyad’a kai ta fice ta bar Manman Cangwai da su Ladiyo cikie da mamakin sauyin Bintu lokaci guda duk akan kishin bayi. Minti kad’an sai ga ta ta fito sanye da lifayar nan da ta cire kafafun ta sanye da cikin farin takalmin fata ta ce da Ladiyo

‘’wuce mu tai d’akin horo’’

Da sauri Ladiyo ta yi gaba Bintu na biye da ita, ita kuwa Maman Cangwai bin Bintu ta yi da ido, cikin ran ta kuwa fad’i ta ke lalle dole ta aika da sak’on neman taimako Sa’ayrasa domin kuwa alamu ya nuna Bintu mai yin gaban kan ta ce.

Cikin sak’ar zuci Sadauki wanda ke zaune bisa daddumar da ke shimfid'e a lambu ya ke duban baiwar da ta zo masa da amsar Bintu gare shi. D’aya da ka cikin bayin sa ne ya furta

‘’gide Gimbiya d’iyar Sa’ayrasa ba ta da masaniya akan girman Yarima Sadauki, ko shakka babu za ta tuba Allah shi taimaki Yarima’’

Baiwa na mai gyad’a  kai cikin amincewa da maganar na bawan ta ce

‘’kwaran gaske, tuba ta ke ran Yarima ya dad’e’’

Murmushin mugunta Yarima Sadauki ya saki, cikin ran sa ya na mai jaddada dana sanin da Bintu za ta yi bisa ga kuskuran da ta yi a gare shi, tabbas ta tari aradu da ka dama dai ta bar abin ya tsaya ga mijin ta da ya fi mata sauk’i, zai kuwa nuna mata bakin rijiya ba wajan wasan makaho ba ne. Mik’ewa yayi tsaye yayinda bawan sa yayi saurin matso da takalman sa gaban sa. Cike da tak'ama ya sanya bayi na masu ram masa baya su ka d'au hanyar fita.

‘Dakin Horo kuwa Lantana ce ta idda sak’on Maman Cangwai, nan da nan kuwa Dogarin horo ya shiga gyara tsumagiyar sa domin aiwatar da umarnin Gimbiya Fatima. Sauran bayi fada kuwa tuni labari ya zaga, sun yi tattaki zuwa d’akin haro domin ganin yanda baiwa za ta fuskanci hukunci. Kujerar horo aka sanya baiwa ta zauna yayinda aka zuba mata ruwa bisa cinyar ta har zuwa k'asan k'afafun ta yanda ko da zafin tsumagiya zai sa fitsari ku6uce mata ba zai nuna ba. Waje yayi tsit kuka baiwa kad’ai ke tashi yayinda Dogarin horo ya d’aga tsumagiyar sa ya na shirin sauke ta bisa cinyar baiwa muryar Ladiyo ya dakatar da shi ta hanyar fad’in

‘’dakata Dogarin horo, Gimbiya Fatima ce tafe!’’

Tsayawa yayi cak yayinda Bintu ta taho, bayi na bud’a mata hanya  haka kuma ba su fasa kai gaisuwa gare ta ba har ta iso gaban dogarin horo. Cikin bayin kuwa har da Bakar number wato babban bawan Barde wanda jin an ambato sunan Bintu ya shiga baza ido domin ganin matar uban gidan sa.

Ganin Bintu gaban sa Dogarin horo ya saki tsumagiya k’asa ya na mai kai gaisuwar sa ga Bintu ta hanyar nuna ladabi da mik’a kai a gare ta cikin aminci. Bintu na duban baiwar da ta had’a hawaye da majina, a hankali ta k’asara gare ta, hannu ta sanya ta tada ita tsaye kana ta ce

‘’gide bar kukan ga haka, wagga hukunci baya bisa kan ki, maza tai abun ki, idan uwar gijiya ba ta zama mai tausayawa ga bayin ta ba shin ana tunanin za mu sami tausaya daga mai duka wanda mu an bayi  gare shi?’’

Jin haka bayi su ka hau sowa, shewa da tafi, daga masu fad’in

‘’Allah shi ta ya mi ki, Allahu y ja da ran gimbiya, Allah ya sa ki dad’e ki na yi’’
Sai masu fad’in

‘’madallah da Gimbiyar Sa’ayrasa, mun biki, mu na madallah da ke’’

Ita kuwa baiwa ba ta san sa’in da ta zube k’asa hannayen ta rungume da k’afafun Bintu tsabagen farin ciki ma kasa magana ta yi. Bintu na mai murmushi a gare ta tare da duk kanin sauran bayi da ke wajan ta zame k'afafunta, bayi na mai darewa domin su bata hanya cike da nuna k’aunar su gare ta haka ta d’auki hanyar komawa turakar ta.

Babban bawan Barde da tun kan Bintu ta bar wajan ya ruga domin komawa ga Barde, tuni ya labarta masa yanda ta kasance tsakanin Bintu da bayi, ya k’are da

‘’lillahi warasulihi Gimbiya Fatima ta isa d’iya adala wacce  ta san darajar bayi ko shakka babu halayyar ta ya yi kamanceceniya da na ka ran ka shi dad’e,  aradu ma kuwa. Bayin Fabarusa za su zama su na alfahari da ita tun daga rana ita yau’’

Barde na mai duban Bakar number, duk maganar nan da ya ke hankalin sa ba gun sa ya ke ba, tunanin K'amariyya ne ya addabi ran sa ya na mai takaicin ina ma dai ita aka d’aura masa ba k’anwar ta ba, shin da wani ido ake so ya dube ta a matsayin mata har ya kai ga kusantar ta?

****

Sadauki da tashi tawagar kuma a nasu 6angaran fitowar shi daga lambu bayan ya gama d’an shawagin sa ya na mai tunanin matakin da zai d’auka bisa matar Barde ya hangi Bintu da Ladiyo a kan hanyar su na komawa turaka. Tsayawa yayi cak idanun sa bisa Bintu ba komai ya ja hankalin sa ba sai yanayin zubi da tafiyar Bintu da ya gani iri d’aya sak da na baiwar nan ta Sa’ayrasa da ya gani a daren jiya har ya kai ga aikawa Gimbiya Fatima muradin sa na ganin bayin Sa’ayrasa. Idanun sa kan Bintu ya furta

‘’gide wagga d’iya ba ita an baiwar Sa’ayrasa da na gani a daren jiya ba?’’

Bawan sa na mai duban Bintu da Ladiyo ya furta

‘’kwaran gaske, waccar mai tafe bayan Gimbiya Fatima na d’aya daga cikin bayin Allah shi taimaki Sadauki’’

Sadauki na mai girgiza kai cikin nuna rashin yarda da maganar bawa ya ce

‘’bayan Gimbiya Fatima? Wacce Gimbiya Fatima? Matar Barde gide? Yoto ai ni bayi biyu na ka gani, waccar mai tahiya irin na d’awisu, ma’ana mai sanye da lifayar can, ko shakka babu ita na gani sanye cikin kayan bayi a daren jiya, ba na mance abu mai kyau, ba zan manta da wagga tahiya irin ta ta ba, duk duniya ita d'ai ta na gani da wagga baiwa na iya taka k'asa kamar d'iyar Saraki'’

Bawa na tsoran kada ya yiwa Yarima Sadauki musu ya fuskanci hukunci, dan haka wannan baiwar da ta kawo sak’on Bintu ya yiwa nuni da hannu ya na mai tambayar

‘’ya ki nan, gide shin ko waccar mai tahiya tare da baiwar Sa’ayrasa baiwa ce?’’

Ko da baiwa ta ware ido ta hangi Bintu tuni ta shiga girgiza kai kana ta ce

‘’ina mai tuba, wagga Gimbiya Fatima d’iyar Sarki Inuwa na Sa'ayrasa ce ran Yarima ya dad’e’’

Jin haka Sadauki ya shiga shafa gashin bakin sa, har ila yau be d’auke idanu daga kan Bintu ba, dan ya tabbata ita d’in ya gani cikin shigar bayi, abun da ya kasa ganewa shi ne

‘’me zai sa Gimbiya, d’iyar Sarki kuma matar Barde shigar bayi? Shin menen dangantaka ko alak’a da ta ke da Shi mai k’arfi haka tsakanin ta da bayi da har za ta aiko masa da bak’ar magana dan kawai ya nemi ya gana da bayin Sa’ayrasa? Ko dan ta san ya gan ta daren jiya ne? Shin akwai wani lamarin 6oye dangane da ita?’’

Tambayoyin da ya ke ainawa cikin ran sa kenan yayinda tunani kala kala ke ratsa zuciyar sa. Ya na mai duban bawan sa ya ce

‘’ban yarda da wanga lamari ba, ina so a yi min bincike akan lamarin wagga Gimbiya, a gaggauta yi ba tare da sanin kowa ba, in kuwa na ji magana ta fita rariya sai da uwar mutum ta haifi wani!’’


🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) 16

®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.


1⃣6⃣

Sidiya ce...✍🏼

Ta na tafe ta na hawaye haka ta isa 6angaran Bintu in da ta tadda Ladiyo zaune gaban Bintu ta sha kuka ta k'oshi, daga gefan Bintu kuwa Maman Cangwai ce zaune a k’asa, d'ayan 6angaran Hansai da lantana ne zaune. Bintu ta sallami dukkanin bayin Fabarusa domin samarwa Ladiyo masalaha.

A gaban Bintu baiwa ta aje fanteka ta na mai rawan jiki, tun gaisuwar da ta kai ga Bintu, bakin ta na motsi amma tsoro da kwarjinin Bintu ya sa ta kasa furta komai. Maman Cangwai na me duban ta ta furta
‘’ke mu ke sauraro ya ke d’iyar Fabarusa....’’
Maimakon Baiwa ta fad’i dalilin zuwan ta da kuma sak’on Barde, sai gani su ka yi ta fashe da kuka ta na mai fad’in
‘’tuba na ke ran Gimbiya ya dad’e, ki min rai na tuba ki rufa min asiri, tuba na ke’’
Nan fa su Ladiyo da lantana su ka shiga kallan kallo cike da mamaki. Bintu ma mamaki ya ne ya lullu6e ta, cikin ba da umarni ta ce da Maman Cangwai ta bud’e fantekar ta ga abun da baiwar ke tafe da shi. Ko da Maman Cangwai ta bud’e fanteka sai da gaban ta ya fad’i ganin turaruka iri daban daban masu yawa ciki. A hankali ta kai kallan ta ga Bintu wacce ita ma ta hango me ke cikin fantekar kafin ta maida kallan ta ga baiwar, kana ta furta
‘’wannan kuma daga ina?’’
Baiwa ba ta fasa hawaye ba ta furta

‘’gide sak’o ne daga Yarima Barde zuwa ga Gimbiya Fatima, hallo ya na mai sheda mata cewar Yarima Barde ma’abocin k’amshi da tsafta ne, ta gaggauta sauya gimshikin kusurwar ta.......’’

Ta k’arasa furucin na ta ne cikin rawan murya. Shiru kake ji babu mahalukin da ya furta komai tsabagen bazata da kalamin baiwar ya mu su, babu shakka Barde na me shedawa Bintu wani abu daga 6angaran ta ya na wari duk da dai be fayyace mata ko menene ba, wanda turo fantekar turaren da yayi ba k'aramin cin fuska a gare ta ba ne, ba dan ma an riga an d’aura mu su aure ba da hakan daidai ya ke da ya ce ya fasa auren ta saboda wari da ya ji na daga wani 6angare da ya shafe ta.
Sai a sannan Maman Cangwai ta gane kukan da baiwa ta ke, dan kuwa a k’aida ya zama dole Bintu ta hukunta ta bisa ga sak’on cin fuska da ta iya duban tsabar idanun Bintu ta sheda mata, in kuwa ta yi sake ta rabu da ita salin alin, toh tabbas ta siyawa kan ta raini daga kan jama’ar fada har izuwa sauran bayin na fada babu wanda za ta k’ara yiwa kwarjini bare a ji shakkar ta.
Jin Bintu ba ta furta komai ba Maman Cangwai ta dawo daga gefan ta, in da ta zauna kamar me jiran umarni daga Bintu, a kaikaice yanda baiwar ba za ta fahimta ba ta ce da Bintu
‘’hattara Gimbiya, wanga batu ba na sassauci ba ne, dan haka zan ari bakin ki in ci albasa, ina mai neman alfarma rashin maganar ki bisa hukumcin da zan aiwatar kan wagga baiwa ta fabarusa’’
Ba tare da ta jira amsar Bintu ba ta mayar da kallan ta ga baiwa, sannan ta ce
‘’bisa ga umarnin Gimbiya, ta yaba da kyautar Yarima a gare ta, sa'annan wagga baiwa da ta kawo sak’o gare ta, zaki amshi bulala hamsin na daga tsimagiyan Gimbiya Fatima’’
Da sauri Bintu ta kai kallan ta ga Maman Cangwai cike da 6acin ran jin furucin na ta ta yi k’ok’arin dakatar da ita, wanda hakan ya sa Maman Cangwai saurin fad’in
‘’na yi kuskure Gimbiya, bulala sittin Gimbiya ta ke nufi, maza Lanta tashi ku fitar da ita zuwa d’akin horo, ki kuma sheda ma su umarnin Gimbiya kowa ya ji ya gani ya kuma sheda!’’

Baiwa na kuka ta na fad’in
‘’tuba na ke ran Gimbiya ya dad’e’’

yayinda Lantana ta tasa ta gaba, ta na mai fad’in
‘’godiya ta ke Allah shi taimaki Gimbiya’’
Su na fita hawayen da ya ciki idanun Bintu tuni ya gangaro bisa kuncin ta tsabagen tausayin baiwa da ba ta san hawa ba ba ta san sauka ba an k'ak’aba mata horo tsabagen rashin adalci. Cike da 6acin ran da ita kan ta Maman Cangwai ba ta san Bintu na da irin wannan fushin ba, ta furta

‘’akan wani dalili za a yiwa baiwa horo? Gide ita na ta ba sak’o ba ne? idan adalci ne na lalle sai kin nuna an min ba daidai ba ki hukunta shi Barde wanda ya aiko ta mana? Saboda ita baiwa ce? Su bayi ba su ‘yanci? Bayi su an bola?’’
Jiki a sanyaye Maman Cangwau ta furta
‘’hakan da na yi kad’ai zai nuna matsayin ki na d’iyar sarki, dan kuwa babu d’iyar sarakin da za a yiwa wanga cin fuska ta kasa aikata yanda na aikata, in ba dai so ki ke asiri ya tonu ba. Na san yanda ki ke ji, amma fa kada ki manta ko nima baiwar ce, ina fatan za ki fahimce ni.....’’
A fusace Bintu ta tashi tsaye, ta na mai girgiza kai ta ce da Maman Cangwai
‘’ba zan ta6a fahimtar ki ba in dai bisa zalinci ne, ba da yawuna ki ka aiwatar da hukuncin ga ba, umarni na anan shi ne ki gaggauta dagatar da shi!’’
A fusace ta wuce d’akin ta, wanda kan ta kai ga shiga sallamar wata baiwa ya tsaida ita. Ta na ji baiwar na gaishe ta amma 6acin ya sa ta kasa amsawa ta d’aga k’afa za ta shige kenan amma jin furucin na baiwar ne ya tsada ta. Jin ta na fad’in

‘’Yarima Sadauki ya na da murad’in ganin dukkanin bayin Sa’ayrasa!’’

A hankali Bintu ta juyo, wato 6acin ran da take ciki ya sanya ta rikidewa hatta Maman Cangwai, bare kuma su Ladiyo, tashi guda ta tashi daga Bintun da su ka sani ta zame mu su wata daban mai wuyan fasaltuwa. Ta na mai duban baiwar ta furta

‘’wa an Sadauki? A matsayin sa nawa ya ke da muradin ganin bayin Sa’ayrasa gide? Akan wani dalili?

Baiwa ta yi jim  dan kuwa ta tsorata da yanayin da ta ga fuskar Bintu, cike da 6acin rai da kwarjini ga kuma tambayoyi na gadara da ta mata akan Yarima Sadauki. Nisawa ta yi kafin ta amsa mata da

‘’Allah huci zuciyar Gimbiya, Yarima Sadauki shi an Yaya ga Yarima Barde wanda ya ke maigida a gare ki, dalilin sa na murad’in ganin bayin Sa'ayrasa shi kad’ai ya barwa kan sa sani’’
Bintu na mai jinjina kai ta ce da baiwa
‘’ki koma ki shedawa Sadauki ni Fatima na ce bayin Sa’ayrasa ba za su isa gare shi ba muddin be zo mana da gamshashshiyar dalilin sa na murad’in hakan ba!’’

🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) 15

®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

1⃣5⃣

Sidiya ce...✍🏼

Jin haka hankalin Bintu ya tashi, cike da fargaba ta kai duban ta ga Maman Cangwai, wacce ta gane halin da Bintu ta ke ciki kana ta ce

‘’ki nuna masa hanya ya iso gare ta, ni da sauran bayi za mu tsaya daga wancan d’aki, ke kuma Ladiyo da ke  ku tsaya daga wajen kofa kafin Gimbiya ta sallame ki’’

Cikin rawan jiki Ladiyo ta tashi ta na mai fad’in
‘’an gama ran gimbiya shi dad’e’’
Ko da ta koma gun su Yarima Barde, Maman Cangwai ce ta fito da kan ta ta sallami sauran bayi zuwa ga d'ayan d’akin, duk da kuwa bayin Sa'ayrasa ba haka su ka so ba, su ma dai so suke su ga Yarima Barden nan da jama’a ke yawan ambaton sa wajan kyawu. Ladiyo a gaba, biye da Ita Yarima Barde ne in da shi kuma Bakar numb ya tsaya daga waje, su ka shigo falon Bintu.
Warin nan da ke d’aga masa hankali shi ya ke bunk’asa ya na dad’a bakuntar hancin shi duk sanda ya d'aga k’afa ya sauke a falon. Isar su tsakiyar falon Yarima Barde ya tsaya cak, ga mamakin Ladiyo ji ta ya furta

‘’gide bayi masu shiga irin ta ki nawa ne cikin wanga turaka?’’
Ladiyo na mai susa k’yeya yayinda ta shiga kame kame ta cikin fargabar kar dai ya gane ita ce mai bin bayan sa cikin lambu ta yi saurin fad’in
‘’iye na’am? Mu na da d’an dama ran Yarima Barde ya dad’e, wagga shiga ita an shigar bayin Sa’ayrasa, dukkanin mu wagga shiga mu ka yi Allah shi da ran Yarima’’
Yarima Barde na mai duban ta ya ke d’an tuntuntuni, dan kuwa ko shakka babu ya san wagga baiwa ta gaban sa ba ita ce mai warin da ya gani a lambu jiya ba, duk da dai be ga fuskar waccan da kyau ba amma ya san a jiki waccan tafi domin kuwa Ladiyo irin k’ananan matan nan ne. Shi kuma a yanzu be da buri da ya wuce ya gano baiwar nan da ke wari ko ya sami lafiya domin kuwa muddun ta na nan ba zai iya zama ko da na minti hud’u a turakar amaryar ta sa ba, abun mamaki shi ne ta yaya bayin Gimbiya kamar Fatima za su na zama da wari har haka ba tare da ta d'auki mataki ba? Hakan ke tabbatar masa da k'azantar da ke tattare da ita.
Juyawa yayi ba tare da ya sake tankawa Ladiyo ba, wacce ta yi kasake ta na duban sa ta rasa yanda za ta yi da ran ta, ganin dai da gaske ficewar ya ke ta bi bayan sa da sauri, amma ina kan ta cima su tuni ya d’au hanya, Bakar numba biye da shi. Da gudun ta ta dawo d’akin Bintu in da ta zu6e k’asa ta na kuka fad’i ta ke
‘’ki min rai Gimbiya, kwankwatsi ban san shi an Yarima Barde ba, aradu da na san shi na da ban bi bayan shi ba, in k’arya na ka yi aratta kashe ni’’

Cike da mamaki Bintu ta yane lifaya da ta rufe fuskar ta, tambaya ta ke

‘’gide lafiya? Yo to minana? Mi Yariman yay mi ki da har ya sanya ki kuka Ladiyo? Ina Yariman ya ke?’’

Ladiyo wacce duk a zatan ta Yarima Barde ya gano ta ne ran sa ya 6aci har ya juya ya fasa ganin Bintu ta ce

‘’ Yarima Barde ya juya ya koma, ki min rai kar ya sa a tsire ni, ina ni ina lek’en surrun Yarima Barde, ki taimaka ki min rai, wayyo ni Ladiyo sai kuma yanda aka yi da ni d’an daudu a kabari’’

Ganin dai Ladiyo ba ta da niyar bata cikakkiyar amsa ya sanya Bintu tashi ta fita da kan ta, ita ma Ladiyo bayan ta ta biyo wanda kukan ta ya sa sauran bayi fitowa. Maman Cangwai na mai tambayar ko lafiya? Ina Yariman ya ke? shin me ya fito da Bintu daga uwar d’aka ita kuma Ladiyo kukan me ta ke?
Kasa amsa mu su Ladiyo ta yi har sai da Maman Cangwai ta daka mata tsawa sannan ta iya labarta mu su yanda ta bi bayan Yarima Barde zuwa Lambu ba tare da ta fad’i jan  Bintu zuwa lambu da ta yi ba, yanzu haka ya gano ita ta ke lek’en asirin sa.

Cikin jimami kowa ya ke duban Ladiyo wacce ta had’a zufa, hawaye da majina. Ita kuwa Bintu waje ta samu ta zauna cikin neman mafita, dan kuwa muddin abun da Ladiyo ta fad’a gaskiya ne, ko shakka babu dole sai an hukun ta ta, lek’en asirin Yarima ba k’aramin laifi ba ne, za a iya amfani da wannan ace so ta ke ta idda wani mugun nufi kan sa ko kuwa dai ta ha’d’a baki da abokan gaba ta na san halaka shi.

Yarima Barde kuwa da fitar sa kai tsaye gun Jakadiya ya nufa. Ya tadda ta bisa sallaya tana lazumi kan ta zo ta shiryawa sarki sauwar dare. Ganin Barde ta san da matsala wanda shi ma be 6oye mata ba ya sheda mata cikin azanci ba tare da ya fayyace mata komai ba.
‘’ya Jakadiya, a had’a fanteka na turaruka, na jiki zuwa na kaya, a aika ga Gimbiyar Sa’ayrasa, a kuma sheda mata Yarima Barde ma’abocin k’amshi da tsafta ne, ta gaggauta sauya gimshikin kusurwar ta’’

Cewar Yarima Barde, wanda ya juya ya tafi ba tare da ya tsaya amsa tambayoyin da Jakadiya ke shirin jera masa ba. Abun da kuwa ya fi d'aure mata kai shi ne fantekar turaren da za a kai, ga kuma batun na Barde na Bintu ta gaggauta sauya gimshikin kusuwar ta, ko shakka babu Barde ya ji wari daga wani 6angare na Bintu ko kuwa bayin da ke tattare da ita.

Ba tare da 6ata lokaci ba Jakadiya ta aikata yanda Barde ya ce. Cikin baitul mali ta shiga, daga cikin daular iyalan Sarki Abdulrahman ta jido turarurruka fanteka guda, cikin bayi ta za6i wacce ta fi tsana sannan ta d'aura mata fanteka ta tere da bata sakon Barde zuwa ga Bintu. Jin sak'on da aka bata sai ga baiwa a k'asa ta na yiwa Jakadiya magiya da kada ta tura ta da wannan mugun aike, amma ina sai ma tafiyar ta yi ta barta ta na share hawaye dan kuwa dai ta ta ce ta same ta kishiya tara  rana d’aya.

🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) 14

®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

1⃣4⃣

Sidiya ce...✍🏼

Barde kuwa a nasa 6angaran komawar sa turakar sa har da amai. Hankanlin sa be kwanta ba sai da ya amayar da dukkanin abun da ke cikin sa. Abun da ya ke bashi mamaki be wuce yanda yaji dan adam ya na wari kamar na mushe ko kuwa ja6a ba, daga ganin shigar ta ya san baiwa ce sai dai ba irin kalar shigar bayin Fabarusa ba ne, ko koma baiwar wata masarauta ce dole ya sa a nemo masa ita a sallame ta daga cikin fada ta je ta nemi magani gyambon da ke jikin ta idan dai ba so ake kar shi har lahira ba. Da wannan ya sami mafakar rashin zuwa ya ga amaryar sa, yayi kwanciyar sa abun sa.

Washagari da sassafe Jakadiya ta je masa da karin kumallo na musammam bisa ga umarnin Sarki Abdulrahman. Wanda Yarima Barde ya san ba komai ba ne illa tambayar
‘’shin ka je wa matar ka?’’
Saboda haka ko da Jakadiya ta tashi tafiya sai Yarima Barde ya bata sak’o zuwa ga Gimbiya Fatima, ya na mai fad’in
‘’a shedawa Gimbiya Fatima, bayan gaisuwa da fatan ta na lafiya, ta saurari zuwan mu bayan fad’uwar rana, kada ta tsawaita buri ba ma buk’atar komai daga gare ta’’

Kalaman da Barde ya k’arasa da su be hana Jakadiya rangwad’a gud’a ba, dan kuwa ta san tabbas idan aka juri kai zuga gabas wata ran ta zo da ruwa. Ai kuwa ko da sak’on ziyarar Barde ya riski su Bintu, nan fa Bintu ta ga ta kan ta dan kuwa tun da safiyar Manman Cangwai ta shiga gyara ta da su turarukan wuta, tsimi ne da cukwid’i kai har da wanda ma ba a sa ta ba, domin fa Maman Cangwai ita ta na da nata manufar na musammam cikin ran ta na game da Bintu, sai dai sa6anin sauran ita kad’ai ke san Bintu da alkhairi.

In dan ban da fad’uwar gaba babu abin da Bintu ta ke, bini bini ta ke duba lokaci ta na mai fargabar fad’uwar rana da abun da za ta zo mata da shi na daga ziyarar Yariman Fabarusa. Haka kuma kaman nin wannan da ta gani cikin lambu be dena mata gizo ba, da za ta sami dama ko shakka babu ta na komawa cikin lambu ko Allah ya sa ya k’ara bayyana a gare ta.
Yarima Barde ma cikin zulumin had'u da k’anwar Gimbiya K’amariyya a matsayin matar shi ya wuni. Rana na fad’uwa ya shirya cikin shigar sa na saraki, biye da shi amintaccan bawan sa ne wanda ake kira Bakar namba, su ka nufi 6angaran su Bintu.

Lifaya fara kyal Bintu ta d’aura bayan ta sha turaruka na hayaki da humra. Ta na daga zaune bisa gado gaban ta na fad’uwa tsabagen fargaba ji ta ke kamar ta zura a guje. Maman Cangwai ce ta sa ta a gaba ta na ta jera mata bayanai tare da kashedi, fad’i ta ke

‘’kin san dai ke d’iyar Sarki ce ba d'iyar bayi ba, ki kasance mai rowar muryar ki a gare shi, ban da yawan surutu in dai ba ya zama dole ba, ki kasance gwanar iya kalamai duk san da zaki bud’i baki ki yi furuci, ki tabbatar kin tauna kin juya kan ta hito daga leban ki.........’’

Daga waje tun isowar Yarima 6angaran na Bintu warin nan da ya ji a lambu ya fara bakuntar hancin sa, hankalin sa ne ya fara tashi yayinda ya ji bugun zuciyar sa na dad’a k'aruwa. Cikin wannan hali ya yi tsaye bakin k’ofar falon Bintu, yayinda bak’ar namba ya shiga kwad'a sallama.
Ladiyo na mai amsa sallamar ta fito, ganin wanda ke gaban ta tsaye ta yi ta na duban sa. Sanye ya ke cikin fara Jabba wanda aka mata ado da koran zare, bisa babban rigar sa ce na dokakkiyar shadda fara kyal sai d'aukan ido ya ke. Haka rawanin da ke bisa kan sa irin na buzaye zuwa huffin da ke sanye cikin k’afafun sa farare ne kyal kai ka ce shirya shi aka yi.
Ganin ta saki la66a da su ga66a ta na duban Barde, ba ta da niyar motsawa bare ta kai gaisuwar ta gare shi, ya sanya Bakar numba fad'in
‘’hattara d’iyar talakawa! Yarima Barden Mahadi shi an gaban ki’’

Tuni Ladiyo ta zu6e k’asa jin buzun nan dai ba kowa ba ne illa mijin Bintu, fad’i ta ke
‘’tuba na ke Yarima, Allah ya huci ran Yarima, babban Barde babban bako’’

Shi kuwa Barde ganin tufar jikin ta ne ya dad’a d’aga masa hankali ba wai yanda ta masa ba, dan kuwa tabbasa wannan baiwar mai wari da yayi arba da ita cikin lambu a daran jiya irin shigar ta kenan. Idan kuwa haka ne to lalle d’aya daga cikin bayin matar da aka aura masa ne ke wannan mugun warin da ke neman halaka shi.
Bakar numba ne ya amsa da
‘’an gaishe ki d’iyar talakawa, ki shedawa Gimbiya Fatima Yarima Barde na neman iso gare ta’’

Da sauri Ladiyo ta tashi har tana hard’ewa, yayinda ta ke fad’in
‘’an gama ran Yarima ya dad’e’’
Ciki ta shige jiki na rawa,  ta tadda bayin da ke hidima cikin falo wanda k'atuwar muryar Bakar numba ya sanar mu su da isowar Barde, kowannan su ya nutsu jere cikin sahu, musammam bayin Fabarusa wanda dama sun fi na Sa’ayrsa sanin darajar Barde. Kai tsaye cikin d’akin Bintu Ladiyo ta shige ta na mai zubewa k’asa gaban Bintu dan kuwa ganin Barde ya sa ta tsorata da sa’a tare da nasarar da ke tattare da d’iyar bayi
‘’ran Gimbiya ya dad’e, Yarima Barde ya iso ya na mai neman iso gare ki Gimbiya’’

🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) 12

®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

1⃣2⃣

Sidiya ce.....✍🏼

6angarn Bintu kuwa kamar yanda ta saba, yau ma ta sallami dukkanin bayin ta, ya rage daga ita sai Ladiyo, wacce ita dama d’aki d'aya su ke kwana idan ta tabbatar kowa ya d’auke k’afa, tsabagen tsoro da rashin sabon kwana ita kadai. Bintu na kwance bisa gadon ta, tunanin Innar ta ta take da rayuwar ta na da wanda shi ya fi mata dad’i akan wannan daula da ta tsinci kan ta a ciki. Ladiyo da ke tsaye bisa taga idanun ta kan hanyar lambun da ke kyetare da 6angaran Bintu, sai ajiyar zuciya ta ke ba tare da ta san ta na yi ba saboda tsabagen muradin sake zuwa lambum da ya addabi zuciyar ta, ba dan komai ba ko dan ta ga wannan buzun da ta gani ciki mai irin sifar aljanu tsabagen kyauwu.
Gashi ran da ta fara shiga lambun satar hanya ta yi bayan Bintu ta yi bacci ta ga wucewar sa, kasancewar shi kad’ai ne ya sa ta yi tunanin kila talakan Sarki ne, wanda su ke da daurin gindi wajan fadawan Sarki ko kuwa d’aya daga cikin ‘ya’yan hakiman masarautar nan. Nan ta gan shi zaune bisa kan dutse ya na sakar zuci, har ta k’are masa kallo be san ta na yi ba tajuya tana tasbihi ga Allah bisa tsarin halitta da yayiwa bawan Allah nan.
A hankali ta kai kallan ta ga Bintu, kana ta ce

‘’gide Gimbiya ba ki da muradin ganin farin wata ne? aradu zaman cikin kurya ya ishe ni’’

Jin haka Bintu ta yi farat ta tashi zaune ta na fad’in
‘’yo to Ladiyo mu tai mana, ba tun yau na ke da muradin mik’e k’afa, kwankwatsi ni ma na gaji da zaman nan, hallo ki na ga babu matsala aka gan ni a rariya?’’
Abun da Ladiyo ke so ta samu duk da kuwa ba ta yi tsammanin haka daga wajan Bintu, ko da shike dama ai d’iyar bayi ce Ladiyo din ce ke sha’afa. Ta yi saurin dawowa gaban Bintu jiki na rawa ta ce da ita

‘’gide ai da yawa ba su san fuskar ki ba, ba na jin za su waye ki, kai in ki na son badda kama ma zai fi na ara mi ki d’aya daga cikin kaya na na bayi......idan fa Gimbiya za ta iya sanyawa’’
Ta k’arasa ne cikin d’ard’ar kada Bintu ta ce ta raina ta, duk dai ita kan ta ta san babu laifi Bintu ba ta canza mata ba, in har ba wai akwai mutane gun ba yanda ta saba mata tun tana baiwar ta hakan ta ke ma ta. Ga mamakin Ladiyo sai gani ta yi Bintu ta tashi cikin hanzari ta na mai fad’in
‘’kayya ku ji mu da Ladiyo da yasasshen zance, tuwo ne towo ba a sake masa suna, maza d’auko mu tai ko ba komai na sha iska’’
Cike da farin ciki Ladiyo ta da’aukowa Bintu d’aya daga cikin kayan ta na bayi, kan kace me sai ga Bintu ta koma gidan ta na da, wato shigar kayan bayin Sa’ayrasa, Ladiyo har ta na mata tsiyan ya ta ga kayan sun kar6e ta sun zauna jikin ta sosai, ko da shike daga jikin ne.

Bintu na duban kan ta cikin madubi, idanun ta cike da kwalla ta ce
‘’Allah Sarki wata rana, aradu Ladiyo na fi san rayuwa ta a da akan wagga sabuwar rayuwar’’
‘’yo to Bintu ina ga cigaba ki ka samu, wani sa’ilin sai na ji dama ni ce ke aradu da kin ga yanda ake tsiya da mulki. Mu tai dan Allah kar wani abun ya zo ya sa mu fasa hita’’
Bintu na me goge kwalla ta bi bayan Ladiyo. Daga waje su ka tadda bayi mata wanda Goggon nan ta bawa Bintu zaune. Ganin su sai da Bintu ta ja da baya gudun kar da su waye ta. Ladiyo ce ta yi maza ta ja hannun ta tana mai fad’in
‘’barkan ku da dare’’
‘’barka dai Ladiyo, an fito shan iska ne?’’
Su ka amsa mata amma idanun su na kan Bintu. Ladiyo ta ce
‘’eh Gimbiya na da muradin a bar ta ita kadai’’
Kai su ka jinjina su na mai musu fatan dawowa lafiya. Har sun yi gaba su tsaida su ta hanyar fad’in
‘’ba ku ji ba’’
Cak su ka tsaya, Bintu na mai rawan jiki, cikin ran ta fad’i ta ke
‘’shikenan sun gane ni’’
Ita kanta Ladiyo mutawar tsaye ta yi ta na jiran tsammani. D’aya daga cikin bayin ce ta matso gare su kana ta ce
‘’Ladiyo wagga baiwar ban waye ta, shin ko ita ce Lantana?’’
Ta na magana ne yayinda ta ke k'ok'arin ganin fuskar Bintu wacce ta 6uya cikin duhu. Ladiyo na mai sosa k’yeya ta ce
‘’ah ah wagga  Batula sunan ta’’
‘’Batula?’’
Baiwa ta sake maimaitawa, Ladiyo ta jinjina kai kafin ta ja hannun Bintu su ka yi gaba ta na fad’in
‘’bari dai mu je mu dawo....’’
Ko da su ka k’urewa ganin bayin sannan su ka karya kwanar da za ta sada su ga lambu, har lokacin gaban Bintu be dena fad’uwa ba, haka kuma Ladiyo ba ta fasa mitar gulma irin na bayin Fabarusa ba.

Hankalin Bintu be kyauta ba sai da ta tsinci kan ta cikin lambu. Lambu ne mai ban sha’awa wanda ya sha ado da bishoyin kayin marmari iri daban daban. Hasken wata da yayi fari kal a tare da hasken lantarkin da ke daga cikin kowacce kusurwa na cikin lambun ba k’aramin k’ayata shi yayi ba. In ban da koken tsuntsaye da na kwari babu abun da ke tashi cikin lambun.

Tuni Ladiyo ta shiga raba ido ko Allah ya sa ta ga wannan mutumin, ita kuwa Bintu wani dutse ta samu ta yi zaman ta kai ta na fad’in

‘’kai Ladiyo wagga lambu ba dai ni'ima ba, ni dai na yi wajan zama daga nan’’
Ladiyo na mai raba idanu ta ce da Bintu ita dai za ta d’an taka to, yanzu za ta dawo. Nan bisa dutse ta bar Bintu yayinda ta kutsa cikin lambu domin neman wannan mutumin.

Barde kuwa da daman shi Ladiyo ke nema zaman Lambun ne ya ishe shi, gaba d’aya ya kasa samin nutsuwa. A hankali ya ke shawagi cikin lambu, wani irin wari ya ji yana bak'untar hancin sa sannu a hankali, tun ya na iya jurewa har ya kasa ya yanke hukuncin ficewa daga Lambun gaba d’aya dan kuwa warin ya fi k’arfin na mataccen dabba. Ko da ya d’auki hanyar fita daga Lambun nan ya ji wari na k’ara gabato shi. Nan bisa dutse yayi kaci6us da ita kishingide, idanun ta runtse tamakar mai bacci, hakan nan wani irin wari da tun da yazo duniya be ta6a jin irin sa ba ya daki hancin sa har sai da ya ja baya da sauri wanda k’aran sautin motsin na sa ya sa Bintu bud’e idanun ta yayinda ta kai kallan ta ga kyakkawan buzun da ke tsaye gaban ta, hannayen sa biyu bisa hancin sa da alama yana k’ok’arin kare hancin daga jin wari ne.

🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) 11

®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

1⃣1⃣

Sidiya ce.....✍🏼

Da  hantsi Sarki Abdulrahman zaune bisa kujerar mulkin sa, ana zaman fadanci sai ga Yarima Barde. Ganin sa Sarki be san sanda ya murmusa ba, dan kuwa ya lura wasan 6uya Yarima Barde ya ke da shi, idan har ba zaman fadanci ba ba ya ta6a yarda su had’u da Sarki duk dan gudun duk wate magana da ya shafi Bintu wanda tun da aka d’aura auren ba su sami kye6ewa da Sarki ba bare su tattauna batun.
Sanye ya ke cikin fararan kaya an masa d’inkin hannu irin na sarauta. Ya sha rawani irin na buzaye kai da ka gan shi ka ce daga sahara ya ke. da shigowar sa dogarai su shiga yiwa Sarki kiran lafiya su na mai sanar ma sa da isowar Barde
‘’ kimtsi gyara daidai alher, gyara kimtsi ga kyau’’

Gaban Sarki Yarima ya zube, hannun sa na dama dunk’ule ya kai jinjina ga Sarki, dogarai fad’i su ke
‘’jinjine dama lafiya alher, an gaishe ka Yarima Barde’’

Da ga gefe kusa da Yarima Sadauki ya ja ya zauna. Nan fa aka ci gaba da fadanci ana tattaunawa akan abin da ya shafi cigaban al’umma da ma kuma matsalolin al’umma da yanda za a magance su. Har aka yi aka k'are idanun Sarki na kan Yarima Barde. Ko da Sarki zai tashi sai cewa yayi da Barde su na san ya riske su a turakan su. Yayinda Sarki zai tashi dogarai su ka rufe sarki ta hanyar baza babban rigunan su yanda ba wanda zai iya ganin motsin sa bare tashin sa. Fad’i su ke

‘’ rangwame Tafsawa, sannu rangwame alher, lafiya Adali, lafiya Mataimakin Musulunci, gyara kyamtsi ga kyau’’

Haka su na masa kiran lafiya har ya kai ga ficewa daga fada. Bayan fitar sa ne Yarima ya kai gaisuwar sa ga sauran Hakiman, ciki har da wanda ke masa Allah ya sanya alkhairi. Ya zo fita kenan Yarima Sadauki ya shagaban sa, ganin sa Yarima Barde ya Murmusa ya na mai dunkule hannun sa na dama ya jinjinawa Sadauki sa’annan ya furta

‘’Sadauki ne kai’’

Cike da tak’ama, shi lalle Yarima mai jiran gado, Sadauki ya maida masa da martani yanda ya saba ta hanyar fad’in
‘’kai ma Barde ne, musammam sa’in da na hau kujerar mulki’’

Barde be fasa murmushin da ya ke ga d’an uwan na sa ba duk da kuwa ya san magana ya ke fad’a ma sa. Kana ya ce

‘’barka da hantsi, da fatan mu na lahiya’’
‘’lahiya lumi fa, ya kwanan amaryar dole? Ko da shike har yau ba mu ji labarin budurcin ta ba bare mu ce ango ya sha k’amshi, d’iyar abokan gaba ce duk da kuwa abun ba dambe ba ne ba, kada Barde ya ba mu kunya!’’

Ya na gama fad’in haka ya yi gaba. D'if Yarima Barde ya d’auke wuta, Khalil da ke tsaye daga bayan su, ya kuma ji dukkannin maganan da Sadauki ya fad’a ne yayi saurin ta6a kafad’ar Yarima Barde, kana ya ce

‘’ba kai an babba ba, amma babba gare ka Barden mahadi maida garin wani kongo’’

Jin haka ya san hakuri Khalil ya ke ba shi. Ya ko yi na’am da Khalil ta hanyar murmusawa ya na mai fad’in

‘’ina da muradin zuwa wucan gadi mutumi na, ko za mu sami dama tafiya kafin na sami saduwa da Sukuku Bakaka(Sarki)’’

Cikin jin dad’i Yarima Barde ya fara sakewa Khalil ya nemo Yarima Jafar domin su tafi wucan gadi.

Da yamma likis bayan Yarima Barde ya dawo daga wucan gadi ya isa ga Sarki. Turakar Sarki su ka d’an ta6a hira sama sama, kafin Sarki ya kawo batun Bintu ta hanyar tambayar

‘’ya amanar da mu ka ba ka? Shin an duba kuwa?’’

Barde na mai durk’usar da kai k’asa ya kasa magana. Ganin haka Sarki ya fahimci in da ya dosa, kana ya ce

‘’kar ka damu d’an mu, ka bi sannu a hankali ba laifi ba ne, amma dai mu na ruk’on ka da kar da mu zamo daga cikin azzalumai ta hanyar d'auka lokaci mai tsayi, wannan gona ta ka ce, kada ka manta akwai idanu dayawa bisa kan ta, da fatan za ka kula a wadata ta, san samu ma a ziyarce ta ko da kuwa daga yau zuwa kwana uku ne’’

Maganar Sarki ba k’aramin nauyi ta yiwa Barde ba, dan kuwa ji ya ke ina ma zai iya masa musu ko da kuwa na sakan d’aya ne, amma ina tsaintar kan sa yayi ya na mai fad’in

‘’an gama Sarkin yakin musulmi, bango madafan bayi’’

Sarki kuwa ba k’aramin jin dad’in yanda Barde ke masa biyayya ya ke ba, cikin ran sa ya na mai jin ina ma shi ne babban d’an sa ba Sadauki ba. Sai bayan da su ka idda salar isha’i sannan Barde ya baro wajan Sarki. Kai tsaye lambun nan da ya saba zama duk dare ya nufa, zuciyar sa na sak’a masa yanda zai yi ya gujewa had’uwa da amaryar da aka d’aura masa, wato kanwar budurwar sa.

🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) 10

®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

1⃣0⃣

Sidiya ce....✍🏼

Ana gama wankan amarya Bintu ta ja jik’akken mayafin ta ta rufe fuskar ta tana mai shar6ar kuka. Ba tare da 6ata lokaci ba d’aya bayan d’aya sauran iyalan Sarki su ka dinga zuwa Jakadiya na gabatar da su, har su ka k’are sannan aka rufe taro da addu’a. Da aka gama maimakon a kai Bintu d'akin auren ta, 6angare ne na musammam cikin gidan Sarki, sai wani 6angare aka sake kai ta na daban daga cikin 6angaran Goggon nan wanda ya kunshi d’aki biyu kowanne  da bayi sai kuma falo. Nan za ta zauna har sai sanda ta kai budurcin ta d’akin mijin ta. Za6in bawai d’aya daga cikin bayin ta wanda za su na kwana 6angaran ta aka bata. Gwaggo Munari ce ta za6a mata Ladiyo dan kuwa ta fi yabawa da hankalin ta, sauran kuma wuni za su na yi, idan lokacin bacci yayi ko kuwa Bintu ta sallame su sai su koma 6angaran da aka tanadarwa bayi.

Yarima Barde kuwa duk wannan bikin da ake masa ya na daga na sa 6angaran. Su Yarima Jafar da Khalil tun suna iya jure  shirun da ya mu su har su ma su ka gaji su ka yi na su gurin. Da ya gaji da zaman ne ya watsa ruwa yayinda ya sanya jallabiya, kai tsaye in da ya saba zuwa duk sanda ran sa ya ke 6ace ya nufa, wato lumbun da yake k’yatare da 6angaran matan Sarki. Nan bisa dutse ya kusa raba dare, sai da ya ji idanun sa sun masa nauyi sosai sannan ya tashi a hankali ya nufi 6angaran sa. Ko da ya zo giftawa ta 6angaran da ya san babu shakka nan aka sauki amaryar da aka aura ma sa, sai ya tsinci kan sa ya na mai mummunar fad’uwar gaba. Hakan ya sa shi wucewa da sauri ya na mai ambaton ubangiji. Bakin kofar sa ya tadda dogarai da bayin sa sun yi jugum jugum kasancewar ya mu su hani da biyo shi, ganin sa su ka fara masa kiran lafiya su na mai fad’in

‘’takawa sannu Yarima Barde, lafiyarka dama da hauni, dama da hauni lafiya, salamun salamun’’

Ganin ya zo daf da shiga kofar da za ta sada shi da 6angaran sa, su ka taka masa baya, har ila yau fad’i su ke
‘’gicciye dama Yarima, gicciye salamun’’
Tsayawa Yarima Barde ya yi, ya d'aga mu su hannun alamar baya buk’ata su biyo shi kafin ya sa kai ya shige ciki. Ya bar su waje su na kallan kallo, dan kuwa sun san lamarin auren Yarima Barde kan su zai k’are duk da dai ba su suka kar zuman ba, rataya aka ba su.

Washagari da sassafe jama’ar Fabarusa, Samari da ‘Yan mata har da tsuffin cikin adon su na burgewa su ka yi dandazo kofar fada domin kallan hawan angonci bisa al’ada. Amma Yarima Barde ya yi k’yememe ya ki fitowa ko da kuwa kofar 6angaran sa ne bare a sa ran zai hau. Ko da su Khalil su ka je da numin bashi baki, a bakin k’ofa dogarawa ma su tsaran kofar Yarima Barde su ka fad’a mu su buk’atar Barde na kada a bawa kowa damar isa gare shi. Dan haka sai hakura su ka yi, Magatakarda ne yayi shela ga jama’a cewar Yarima Barde be shirya yin hawan angoncin shi a ranar ba, su yi hakuri sai zuwa ran da ya shirya za a sheda mu su. Da kyar kamar ba su hakura ba su ka watse, dan ba k'aramin cin burin hawan angoncin Yarima Barde su ka yi ba, kasancewa akwai k’auna tsakanin sa da Talakawa, musammam ‘yan mata da samari, Yarima Barde na su.

"Bayan hayaniyar kofar fada ta lafa, jama’a sun watse su Gwaggo Munari da sauran tawagar Sa’ayrasa su ka yiwa iyalan Sarkin Fabarusa sallama, an had’a mu su koma ta arziki sannan su ka d’auki hanyar komawar su gida S’ayrasa, in da su ka bar Bintu tare da bayin ta, wato Ladiyo, Hansai, lantana da Maman Cangwai a sabon Masarauta. Gwaggo Munari ce ta shedawa Iyalan Sarkin Sa'ayrasa irin tarbar da aka mu su da tarin dukiyar da Bintu ta samu. Gimbiya K’amariyya kuwa sai da ta had’a da kwanciyar asibiti. D’aya daga cikin bayin da su ka juyo ne ta isar da sak’on Lantana ga Yarima Nuhu. Sakon na cewa ta aikata komai yanda ya umarce ta, kuma komai ya tafi daidai. Tsabagen dad’in sak’on na ta har kyautar zani da kallabi ya bawa baiwar domin kuwa in har maganar hakan ta ke babu shakka hakin sa ya cimma ruwa.

Kwanci tashi. Bintu ta cika sati guda Masarautar Fabarusa, amma ko da wasa Yarima Barde be ta6a takowa in da ta ke ba bare ma ta san kalar fuskar sa. Gata kuwa ta na sha gurin matan Sarki, musammam Goggon dole da Uwarsoro ,domin kuwannan su burin su ace amaryar Barde daga ta ta ce, Maman Cangwai ce ke saka Bintu a hanya kasancewar ita ta gane manufar su ba lalle alk’airi ba ne. Ita dai ta bi kowa sannu a hankali. Goggon nan kuwa mulki da jin kan ta kad’ai ya fi k’arfin ta, shi Yarima Barde ba gaban ta ya ke ba, bare uwa uba matar sa.


🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) 9

®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.


9⃣

Sidiya ce......✍🏼

Fitowar ta ba da dad’ewa ba Gwaggo Munari ta sanya Bintu wankan dole dan kuwa ba da san ran ta ba. Da taimakon su ladiyo da Hansai Bintu ta fito fes cikin doguwar riga ruwan d'orawa, rigar da Goggon nan ta aiko mata. Material ne mai tsada ke, sai kuma mayafi kore mai turawa da ratsin ruwan d'orawa. Gwaggo Munari ruke da hannun ta domin kuwa ita ta ke gane mata hanya su ka fito, Su Ladiyo biye da su yayinda aka mu su iso zuwa babban zaure in da mata da iyalan Sarki ke jiran isowar su.

Babban zaure ne wanda ya fi k’arfin a k’ira sa da zure sai dai ko d’akin taro, tsawon sa kamu d’ari, fad’in sa kamu hamsin. Haka kuma ko wacce kusurwa na zauren an masa ado da itacen al’ul a bisa ginshishik’an sa. Bayan ga dadduma mai kulliyar jikin damisa da ke shimfid’e tun daga fari har zuwa k’arshen zauren da kuma tintin masu adon jikin damisa da ke baje bisa daddumar, akwai duwatsu wanda aka auna sa’an nan aka yanka su da zarto ciki da baya daidai da juna, aka jera su zagaye cikin zauren tamakar kujerun zama irin na zamani. Haka kuma bangon zauren zane ya ke da tambarin Masarautar Fabarusa.
Cikin zauren su ka tadda  dukkanin iyalan Sarki Abdulrahman tare da y'anuwa da abokan arziki wanda su ka zo domin ta ya su murna. Matan Sarki Abdulrahman uku wanda su ka had’a da Goggon nan (uwar fada), sai ta biyu wacce su ke kira da Goggo ta dole(uwar dole) sai ta ukun wacce ake kira Uwar Soro, wacce itace mai k’arancin shekaru cikin matan sarki. Kowacce hakimce, k’ishingid’e bisa tuntin. Gaban su kuma wani tulu ne wanda aka masa ado da azurfa cike da ruwa mai d’auke da turare da garin lallel.

Haka kuma ‘ya’ya da jikokin sarki da na su wajen daga gefe wanda d’irga su ba k’aramin aiki ba ne kasancewar ‘yay’an sa mata ma su aure da ‘ya’ya sun kai su goma sha takwas, kuma dukkanin su ba su yi k'asa a gwaiwa ba haka su ka zo da sassa da yankunan Jamhuriyar Nijar domin tarbar amaryar d’an uwan na su. Duk da dai ciki akwai mu su bakin cikin lamarin kasancewar ciki d’aya su ke da Yaremi Sadauki. Musammam Yaya Mai Soron Baki, babbar d’iyar Sarki Abdurahman da mai bin mata wato Yaya Jidda wanda su 'ya'yan Goggon nan.

Wajan da aka tanadarwa Bintu gaban  su Goggon nan aka zunar da ita. Tun da ta yi wanka da ruwan nan na Lantana hankalin ta ya ke a tashe, gashi gaban ta sai fad’uwa ya ke, ta na son fad’awa Gwaggo Munari amma ta tsoran za ta yi zatan fad’an da aka mata ne be shige ta ba, dan haka a dole ta hakura da ikon Allah. Maimakon Gwaggo Munari ta zauna gaban ta, sai gani ta yi ta ja gefe daga wajan su Gwaggon nan. Cikin girmamawa ta mik’a gaisuwar ta tare da damk’a amanar Bintu gare su bisa ga al’ada. Goggon nan wacce a ran ta ta yi farin cikin fasa auren d'iyar Sarkin Sa'ayrasa da Sarki Abdulraman yayi, ta kuma yi bakin cikin aurar da aka aurawa Barde a maimakon d'an ta Sadauki, ta fara kar6ar amana ta hanyar saka hannu ta bud’e mayafin Bintu da ke gaban su, tuni Bintu ta yi k’asa da idanun ta cikin fad’uwar gaba. Sai da ta kalli fuskar Bintu na d’an wani lokaci ta na mai yamutsa fuska ta saki mayafin ba tare da ta rufe fuskar gaba d’aya ba. Kana ta ce

‘’ni Munzaratu jikar Sarki Abdulrahman na difa, d’iyar Sarki Abdulmuminu iii na Agadez, matar Sarki Abdulraman ii na Fabarusa, na bud’e fuskar amaryar dan mu, d’iyar Sarkin S’ayrasa, Sarki Sule Inuwa Magaji da zannuwa hamsin, kallabi hansin tare da bayi guda uku’’

Jakadiya ta rangwad’a gud’a, yayinda waje ya d’au sowa. Ita Bintu ta yi k’asa da idanun ta, ji ta ke kamar ta dan ta k’arasa rufe fuskar ta gaba d’aya. Amma me za ta ji? Goggo ta dole ce ta sa hannu ta k’ara yin baya da mayafin Bintu yanda za ta ga fuskar Bintu da kyau, kafin ita ma ta jero sunan ta da nasabobin iyayen ta, ta bud’e fuskar Bintu da silallan gwal. Ita kuwa Uwar Soro da tashi na ta bajintar da dawakai tare da rak’uma ta bud’e fuskar Bintu. Tuni Bintu ta zama mai arziki da kadarori, su Ladiyo cikin ran su sai mamakin baiwa da Allah yayiwa Bintu, su na jin ina ma dai su ne.
Bayan da matan Sarki suka gama budar ka, sai kuma sauran 'yan uwa da abokan arziki, yayye da k'Annan Barde su ma su ka nuna ta su bajimtar.

Bayan an gama ne Jakadiya ta mik’a wa matan Sarki tulu. Matan sarki su ukun nan su ka tsaya bisa kan Bintu su na mai tsiyayo mata ruwan cikin tulun kad’an kad’an bisa kan ta, yayinda Jakadiya ke bada wak’a jama’ar wajan na amsa mata

"Ayyare daure jure
ayyaraye daure jure!
zaman gidan wani tilas ne!
ba kan ki ne aka fara
ba da kan ki ne aka fara ne
da kin ci kuka kin k'oshi
ke yar tsohuwa mai 'yar tulu
Allah ya kar ki watan gobe
Mu ci gumba’’


🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) 8

®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

8⃣

Sidiya ce.....✍🏼

Shiryayyan d’aki mai had’e da 6and'aki aka aje su Ladiyo, su Bintu kuwa d’aya daga cikin d’akunan Goggon nan a matsayin ta na uwar gida aka sauke su kan a gama wankan amarya a mik’a ta ga na ta 6angaran.
Su na shiga masaukin na su ba da jimawa ba, wata baiwa ta sake dawowa d’auke da kaya, gaban Bintu wacce ke zaune bisa gado har lokacin ba ta bud’e fuskarta ba baiwa ta zu6e, ta na mai aje kayan gaban ta, ta ce
‘’ an gaida Gimbiya Fatima, wagga kaya tsaraba ne da ga Goggo nan, ta ce a shedawa Gimbiya Fatima ta sanya su yayinda za ta hito wajan wankan amarya nan ba da jimawa ba’’
‘’Gimbiya Fatima ta amsa, ta na godiya’’
Cewar Gwaggo Munari. Bayan fitar baiwar Gwaggo Munari ta yaye alkyabbar Bintu, sai ga ta ta yi wuri wuri da ido.
‘’Gimbiya yanzun ga ba lokacin tuntuntuni ba ne, kin dai san dalilin da ya sa ki wanga Masarauta da kuma a gurbin wacce ki ka zo, gwara dai ki sake shawara ki nutsu in har ba so ki ke ki rasa ran ki sa’annan ki haddasa yaki da gaba wanda ka iya halaka ta mu Masarauta gaba d’aya’’

Fad’in Gwaggo Munari cikin gazawa da halayyar Bintu dan kuwa idan ba ta yi da gaske ba ko shakka babu asirin su mai tonuwa ne. A sanyaye Bintu ta ce
‘’ina tuba....’’
‘’ba tuban ki mu ke buk’ata ba!’’
Gwaggo Munari ta katse Bintu, kana ta k’ara da
‘’ Aikin ki mu ke buk’ata Gimbiya! Wanda za ki fara yanzu ta hanyar zama Gimbiya ba d’iyar bayi ba. Allah ya mi ki zubi irin na jinin mulki, kowa ya gan ki ya san hakan nan Allah ya yo ki, ba ki gada ba amma Allah ya baki su a halittar ki, Dan haka tak’ama da isa shi na ke so daga gare ki, ki saka a ran ki wannan dama ne da Allah ya baki dan jin dad'in rayuwa da kuma taimako ga Masarautar mu, idan asirin mu ya tonu gaba d’aya farin cik’in masarautar mu ne zai koma ga zubar jini, ina fatan kin fahimce ni?’’
Bintu ta gyad’a kai. Kana Gwaggo Munari ta dafa kafad’ar Bintu ta ce

‘’madallah da d’iya ta gari. Sai ki yi shiri yanzu su Ladiyo za su zo su had'a mi ki ruwan wanka. Hakuri za ki yi na san kin saba yiwa kan ki komai amma daga yau komai yi mi ki za ake yi, ki jure Bintu wata rana sai alkhairi’’
Bintu ta dad’a jinjina kai. Ana hakan kuwa su ka ji an sake turo kofa an shigo. Maimakon Ladiyo da Gwaggo Munari ta ce, Lantana ce baiwar da Yarima Nuhu ya za6a ta musammam domin kular masa da al’amran Bintu ta shigo ta zube gaban su. Gwaggo Munari na mai duban ta tace
‘’Lantana gide ke ce mai shirya ruwan wankan ne? yo to ina sauran? Kar dai sun tsaya kallan kauye mu ka biya ku fa sai mu makara!’’
Lantana waccen ita dama da ka gan ta ka ga zubin munafunci, dan ko magana ka ke da ita haka za ka ga ta na sinsin da idanu sam ba ta bari a ga kwayar idanun ta. Ta kada baki ta ce
‘’ai ga su nan tafe, sauri na yo dama na shirya ruwan wankan kada a makara’’
Jin haka Gwaggo Munari na mai mata nuni da bayan gidan da ke cikin d’akin ta ce
‘’yauwa madalla da ke, maza je ki ga bayan gidan can shirya mata gide’’

Sim sim ta shige bayan gida. Sai da ta fara taran ruwa sannan ta shiga had’a ruwan da turaruka iri iri kamar yanda su ka saba had’a ruwan wankan Gimbiyoyi. Ko da ta zo kan turaren karshe, sai ta faki idanun Gwaggo Munari ta tabbatar hankalin ta na kan su Ladiyo da shigowar su ke nan, ta na mu su bayanin yanda ta ke so su kasance wajan taro. Sannan ta jawo kofar bayi ta rufe. Gefan zanin ta ta kwance, ta dauko wani kullin magani, cikin sauri da azanci ta bud’e maganin ta na mai zazzage shi cikin ruwan wankan Bintu. Tuni wani irin bakin hayaki mai wari ya taso daga ruwan yayi sama, ita kan ta Lantana sai da ja baya ta na mai toshe hancin ta cikin tsoran kada fa su Bintu su ji duk da dai Yarima Nuhu ya tabbatar mata babu wanda zai ji warin bayan ita da ta zuba. Sai da ruwan ya dena kumfa da hayaki sannan ta mayar da sauran kullin maganin cikin zanin ta ta kulle, ta fito hankali kwance kamar ba ta aikata komai ba.

🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) 7

®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

7⃣

Sidiya ce...✍🏼

Jakadiya ta bud’e kofar motar ta in da Bintu ta ke. Bayi mata guda goma shabiyu, wanda su ka kasu gida biyu sahu su ma jere kan sa sunkuye gaban motar su na jiran fitowar Bintu domin taka mata baya. Idan Bintu ta motsa toh dutse ma ya motsa, sai da Gwaggo Munri ta fito sannan ta zagayo gare ta, hannun Bintu ta lalabu cikin alkyabba, sannu a hankali, cikin azanci kai ka ce Gimbiyar ce da gaske ta fito da Bintu. Tuni bayin nan su ka zube gwiwowin su biyu a k’asa cike da girmamawa. Mata da yara masu waka ba su fasa ba. Cewa su ke

‘’Mun nema! An ba mu! Mun k’aru!
Mun nema! An ba mu! Mun k’aru!!’’

Jakadiya kuwa ba ta fasa gud’a ba. Tuni hayaniya da sowar jama’a ya rud’a Bintu, har sai da Gwaggo Munari ta fahimta ganin yanda ta cize waje d’aya ta kasa tafiya. Cikin rad’a Gwaggo Munari ta ce da Bintu

‘’yo to ki ka cize nan Gimbiya kya iya wad’uwa ba ki sani ba, gide rufa mana asiri mu tai, ke kawai ki ta salati, hallo ka da ki kuskura ki kai kallan ki ga jama’a, hakan ka iya rud’a ki, maza soma ambaton Allah’’

Nan da nan Bintu ta tsinci kan ta ta na mai ambaton Ubangiji. Tsakiyar Uwanlenze da Gwaggo Munari, Jakadiya daga baya, biye da ita bayi goma shabiyu ne, su ka kutsa ta hanyar da aka tanada na musammam domin wucewar Gimbiya. Ba su zame koina ba sai cikin fadar Fabarusa.

Kansencewar Masarautar Fabarusa ta yi biyun ta Sa’ayrasa a girma da tsari, ba su Ladiyo ba, hatta Gwaggo Munari sai da ta yi da gaske wajan 6oye shawa’an ta ga Masarautar domin kuwa lokacin da su saka k'afar su a katafariyar fadar Fabarusa, sun ga abin mamakin gaske, wato bayan girman fadar na da ban al’ajabi, kuma yadda aka fasalta ko tsara ginin ta shi ma abin mamaki ne. A tak’aice sai da su ka zamo tankamar k’auyawan da su ka shigo birni. Gini ne irin na gargajiya wanda aka kafa harsashin ginin da manyan duwatsu ma su tsada, wad'an su kamu takwas wasu goma. Tsakanin kowace katanga akwai duwatsu masu tsada wad’anda aka yanka su bisa ga ma’auni san’annan aka dasa itacen al’ul daga gefan su. Tsuntsayen fada iri iri ke shawagi, musammam d’awisu da jin su ne su ka fi yawa.

Sai da su kusta sauro gomasha biyu kan su kai ga shiga cikin gidan Sarki, kowanne da na sa irin adon da kayan k’awa, wanda idan su ka shiga wannan su ka shiga na gaban sa sai su ka ashe na baya ba komai ba ne idan aka had’a sa da na gaban sa. 'Bangarn uwar gidan Sarki Abdulrahman, wacce ake kira Goggon nan aka sauke su. In da aka zaunar da Bintu bisa shimfid’a na musammam da aka ta na dar mata daga tsakiyar falo, yayinda su Ladiyo, Hansai, Lanta da Maman Cangwai su ka yi zaune daga gefe matsayin su na bayin Gimbiya.

Tuni Barori da Bayi su ka shiga kai kawo da hidima domin tarbar baki cikin aminci ta hanyar tabbatar da ba su bawa Masarautar su kunya ba. Kayan marmari na daga ‘ya’yan itace ne, nama na k’arama da babban dabba kai har da ma na d’awisu, su dubulan ne, caccabe, alkaki da nakiya komai bajau sai wanda jama'ar Sa’ayrasa su ka za6a. Gwaggo Munari na mai jinjina kai cikin ran ta take fad’in

‘’ma su abu da abun sa, gaskiya dukiya cikin wanga masarauta ba a cewa komai! D’iyar bayi ke kuwa Allah ya yankewa kakar saka, amre cikin wanga Masarauta shi an baiwa’’

Ciki su ka bud'e su ka ci su ka yi nak. Amma ita ko Bintu ruwa ma kasa sha ta yi bare ta kai ga cin abinci duk da kuwa azababban yunwa ne ya addabi cikin ta. Bayan an tabbatar su huta ne wata baiwa ta zo ta ce da su idan sun shirya za ta kai su ga masauk’in su domin Gimbiya Fatima ta shirya ta sami fitowa zuwa taron wankan amarya wanda za a yi nan ba da jimawa ba.

🐫🐪🐫🐪🐫🐫

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) 6

®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.


Khadija Sidi..✍🏼

6⃣

Ko  da Gimbiya K’amariyya ta koma d'akin ta, sai ta sallami bayin ta gaba d’aya sannan ta kulle d’akin ta haye tsakiyar gado ta na rusa kuka. Bintu kuwa d’akin Hajja Kilishi bayi ke jera kaya da aka d’inka ma ta na alfarma, yayinda Hajja Kilishi ta sa ta gaba sai bayani iri-iri ta ke mata akan kayan da kuma yanda za ta na amfani  da su, da yanda ake son zaman na ta ya kasance  a fadar Fabarusa kasancewar Sarki ya janye makwanin biyun da ya kamata a kai Bintu ga Masarautar Fabarusa.

Bintu da ba cikin hayyacin ta ta ke ba, babu abun da ta gane kawai dai amsa ma ta ‘’um’’ ta ke. Da wuri Hajja Kilishi ta bawa Bintu umarnin kwanciya saboda sammakon da za su yi a washagari. Yanda ta ga rana haka ta ga dare, haka ta kwana cikin zulumi sai da asuba wani bacci mai nauyi ya sace ta.

Ba ta jima ta na bacci ba, Hajja Kilishi ta aiko d’aya daga cikin Bayin da aka bawa Bintu, wato Ladiyo ta tada ita gudun kada su makara.  Nan ta ke tseguntawa Bintu cewar Gimbiya Binta har ta wuce Nigeria makaranta bisa ga umarnin Takawa. Kuka Bintu ta saka ta na mai fad’in

‘’Na shiga uku ni Bintu, wallahi ni Bintu na ke ba Binta ba, d’iyar bayi na ke ba d’iyar Sarki ba, ashe dai ba zan kammala makaranta ta ba, wayyo Inna ki zo ki taimake ni na shiga uku na lalace!’’

Da ladiyo ta ga haka, kawai sai ta fice, jim kad’an sai ga ta dawo biye da ita Hajja Kilishi ce rai 6ace. Tuni ta hau Bintu da fad’a, ta na fad’in

‘’Wai ashe ba ki da tawassali Fatima? Ba ki yarda da k’addara ba? Idan ba ki fasa kuka ba ba ba ki nuna mana ba a isa da ke ba’’

Jin wanna kalame na Hajja Kilishi tuni Bintu ta shiga taitayin ta, sai ajiyar zuciya ta ke kawai. Hajja Kilishi ba ta gushe ba ta cigaba da maganar ta kamar haka

‘’Ki d’au kaddara ki yi fata Allah ya sa hakan shi an alhairi gare ki, yoto ai alkhairin ne ma. Ina ke ladiyo ?’’
Ladiyo ta matso kusa tare da fad’in

‘’Ran ki shi dad’e’’

‘’Maza ku shiga bayan gida ku had’o mata ruwan wankan amare’’

Cewar Hajja Kilishi.
‘’An gama ran ki shi dad’e’’

‘’Ke kuma Hansai maza shirya kayan Gimbiyar ta ku, Ina Maman Cangwai ne? maza ku sheda mata ta ta kawo maganin d’ar nan da lalle domin yiwa amarya wankan lalle’’

Hansai na mai duk’ar da kai ta ce

‘’Ranki shi dad’e ai tuni Maman Cangwai na can rariya, fitowar Bintu kawai ake jira......’’

‘’Bintu ki ka ce!!’’

Hajja Kilishi ta daka ma sa tsawa. Hansai ta zube k’asa jiki na 6ari ta ke fad’in

‘’Tuba na ke ranki shi dad’e, na tuba ran ki shi dad’e ki min rai aradu na tuba’’

‘’Kwarankwatsi ki na rasa ran ki muddi ki ka kuskure asirin Masarautar ga tonu sanadiyar kuskure irin wang, shasha kawai, me an sunan Gimbiyar ga?’’

Hajja Kilishi na magana ne a hasala kamar mai shirin bugun Hansai. Ita kuwa Hansai idanun ta ke kawo ruwa.

‘’Gimbiya Bintu.....’’

‘’Gimbiya Fatima, ban yarda kin kira ta Bintu ko Binta ba!’’

‘’An gama ran ki shi dad’e, godiya na ke’’

Cewar Hansai. Allah Allah ta ke Hajja Kilishi ta sallame ta ko ta sami sarari. Jin Hajja Kilishi ta ce ta yi maza ta idda umarnin da aka ba ta, Hansai ta tashi da sauri ta fice. Kan ace me? Tuni aka shiga hidimar shirya Bintu, sai ga ta ta fito tsaf da ita cikin fararan tufa tun daga sama har k’asa. Hajja Kilishi ce ta d’auko wani dank'areriyar sark’a na gwal tare da yari da warwaro ta ce a sanyawa Bintu na ta gudunmawar kenan. Haka ma Inna Salti ta turowa Bintu goma ta arziki, ciki har da farrar god'iya. Sauran matan Sarkin ma suma ba a bar su baya ma, sai da su ka yi tattaki domin
nuna bacintar su dan kuwa abu na kishiyoyi sai da ya so ya zama gasa.

Rana ba ta k’arya, sai ga shi ana fitar da kayan Bintu zuwa motocin da ke jere domin kai amarya ga Masarautar Fabarusa, yayinda dattijiwar da ta zo amsar amarya, me suna Uwalanze ke zaune ta na jira. Wasu dattijai mata guda biyu, wanda su ke tamkar kakanni wajan su Gimbiya K'amariyya ne bisa ga al’ada su ka zo raka Bintu wajan Sarki domin su yi sallama a matsayin Mahaifin ta, sannan su damk’a ta ga mutan Fabarusa.

Bintu na ji ta na gani su ka sa ta tsakiya, gud’a ke tashi su kuwa tsofi fad’i su ke

‘’Allah Ya ba da sa’ar tafiya Gimbiya Binta, Allah ya sa a dace d’iyar arziki’’

Ba su zame ko ina ba sai turakar Sarki, in da su ka tadda Jakadiya tsaye bakin k’ofa ta na jira. Da isar su ta mu su iso zuwa gaban Sarki da ke daman abun da ta ke jira kenan. Gaban Sarki su ka aje Bintu dan idan aka d'auke dattijiya mai suna Gwaggo Munari cikin su, duk a na su zatan Gimbiya Binta ce. Sai da su ka kai gaisuwar su ga Sarki sannan su ka juya su ka bawa Sarki waje domin su gana da d’iyar sa.

Murya na rawa Bintu ta furta

‘’Barka da safiya ran ka shi dad’e’’

Shiru be iya amsawa ba, tsabagen tausayin Bintu da ya ji ya lullu6e shi, gami da nadamar hukuncin da ya aikata bisa ga san zuciya. Daga bisani ya nisa tare da fad’in

‘’Da wata murya za mu amsa mi ki Fatima? Da wata murya za mu amsa mi ki d’iyar arziki? Da wani baki za mu amsa mi ki wanga d’iya da ke gaban mu? Yau mun yi kad’an mu amsa gaisuwar wagga d’iya, wacca jama’a su ka ku6uta da ga yunwa saboda ita. Sanadiyyar wagga d’iya, mutan Sa’ayrasa na godiya gare mu, mu kuma godiyar mu gare ki ya ke, Allah ya saka mi ki da alkhairi sa’’

Shiru ya yi na d’an wani lokaci sannan ya cigaba

‘’Mungode kwarai hak’ik’a mun yi dana sanin abin da ya wakana a Masarautar mu, hallo mu na fatan hakan ya zama alkhairi a gare ki. Ki tsaya tsayin daka domin tabbatar da rufin asirin mu, shakka babu kin mana abin da ‘ya’yan mu ba su ma na ba. Tashi ki tafi d’iyar arziki, mu na addu’a albarkar Allah ya bi ki duk in da za ki kasance’’

Jiki na rawa, amma Bintu ta kasa tashi ta kuma kasa magana. Jakadiya ce ta lek’o, ganin yanayin da Bintu ta ke ya sa ta yiwa Dattijan nan magana su shigo su tafi da Bintu Sarki ya gama ganawa da ita.

A 6angaran Hajja Kilishi su ka tadda Dattijiwar Fabarusa wato Uwalanze. Nan aka damk'a hannun Bintu gare ta bisa alada da amana. Bintu fuska k’udundune cikin alkyabba kuka har da majina, Uwalanze ta ja hannun ta, biye da su d’aya daga cikin wannan dattijan ne da su ka kai ta ga Sarki, dama kuma ita d’in ce cikin su ta san gaskiyar lamarin wato Gwaggo Munari. Kai tsaye motocin Fabarusa su ka numfa.

Motoci ne na gani na fad’a wanda ke tashe wannan k’arnin. Mota ta farki cike fal da dogaran Fabarusa, sai ta biyu wacce ke rufe ruf da bakin gilashi, ita ce motar da su Yarima Barde ke ciki. A ta ukun Bintu ke zaune tsakiyar Uwalanze da Gwaggo Munari. Sai ta hud'in kuma bayin da aka bawa Bintu ne, wanda idan ka d'auke Maman Cangwi ko wacce daga cikin su tafe ta ke da na ta kullalliyar akan Bintu. Mota ta biyar ma dogaran Fabarusa ne ciki. Nan su ka d'auki hanyar Fabarusa.

A  hankali Bintu ta ji ana ta6a kafad'ar ta, maimakon ta tashi sai ma dad'a lumshe idanu ta yi ta na mai murmushi, kasancewar mafarkin da ta ke mai dad'i, wai ga ta a makarantar su, tare da Aisar su na zantawa ya sa ta ji sam ba ta so ta farka. Gwaggo Munari ce ta katse mata jin dad'i ta hanyar jijjaga kafad'ar ta, wannan karan da d'an karfi domin kuwa sun jima da isa Masarautar Fabarusa, yanzun haka kofar fada su ke, Uwalanze har ta fice daga motar amma Bintu na nan ta na baccin asara.

A firgice Bintu ta tashi jin jijjigar ta wuce hankali, ga busar algaita da ke tashi, har da hayaniya da wak'e dake  tashi daga bakin mutan Fabarusa da su ka cika kofar fada domin ganin isowar amaryar Yerima Barde.

Ganin alamar Bintu ta tashi, Gwaggo Munari ta shiga gyara ma ta alkyabba yanda fuskar ta zai rufu da kyau, ta na fad'in

"Ko ke fa Gimbiya d'iyar Sarki mai dole, ai ke kuwa bacci be same ki ba"

Kalmar nan ta Gimbiya da jama'a ke kiran Bintu da shi sam ba ya mata dad'i, gani ta ke tamkar ana raina mata iyayen ta, ya ga wanda su ka haife ta amma fin k'arfi zai sa a raba ta da su? In dai haka zama Gimbiya ya ke Allah wadar da irin na Sa'ayrasa.

Ta na kan wannan tunani ne gilashin motar ya sauka, yayinda Jakadiyar Fabarusa ta bayyana a gare su, kana ta ce

"Gide mutan Fabarusa, na cikin gari hallo da na fada, kwan mu da kwarkwatar mu, mun hito domin tarbar amaryar zaki, Yariman mu abin alfaharin mu. Mu na neman alfarmar bayyanar wagga Gimbiya ta Sa'ayarasa, da ta kasance Gimbiyar Fabarusa da ga ranar jiya har illa MashaAllahu"

Gwaggo Munari na mai murmushi ta amsa mata da

"Gimbiyar ta mu, wacce ta kasance fure a gare mu, wacce babu shakka za ta wadata ku da kyawu gami da kamshi da ke tattare da ita, Gimbiya Fatima ta Sa'ayrasa ta amsa kiran mutan Fabarusa"

Jakadiya ta rangwad'a gud'a, tuni waje ya kaure da hayaniya,yayinda mata da yara su ka hau wak'a su na tafi, fad'i su ke

"Mun nema! An ba mu! Mun k'aru!
Mun nema!  An ba mu! Mun k'aru!"
🐪🐫🐪🐫🐪🐫

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) 4-5

: ®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

4⃣

Bayan sarkin Fabarusa ya yiwa Sarkin S’ayrasa bankwana, ya d’au hanya tare da tawagar sa. Haka d’aya bayan d’aya taro ya shiga watsewa. Tawagar shugaban k’asa ma tuni su ka d’auki hanya dan tadda su Aisar.

Sarkin Sa’ayrasa na komawa turakar sa Jakadiya ta zo ma sa da buk’atar iyalan sa na ganawa da shi. Ganin magariba ta gabato ya ce su maza su iso gare shi kada ya rasa sallah.

Hajja Kilishi, Inna Salti, Gimbiya Binta da kuma Gimbiya K’amariyya ne zaune gaban sarki, sai kuma Jakadiya da Bintu can gefe nesa da su. Jikin Bintu har karkarwa yake, fatan ta Allah ya sa Sarki ya duba lamarin ta hanya warware auren masifar da aka d’aura mata.
Ya na mai kallan Gimbiya K’amariyya ya ce

‘’ke mu ke sauraro’’

Maimakon ta bashi amsa sai ta kai kallan ta ga Inna Salti, cikin idanun ta ta na mata magiyar ta taimaka ta shedawa sarki. Inna Salti da ta gane halin da K’amariyyar ke ciki ta ce

‘’Allah shi ja da ran Takawa, batun amren da aka d’aura ne, wanda aka d’aura amren da shi, shi ke neman amren Kamariyya’’

‘’dama akwai wanda ya zo ya same mu da batun amren d’iyar mu? Ba mu san da wanga Magana ba’’

Fad’in Sarki Sule. Inna Salti na mai kame kame ta ce

‘’eh dama ba su zo din ba, kasancewar da akwai rashin jituwa tsakanin Masarautar ta Fabarusa da ta mu, hakan shi ya kawo jinkiri Allah ya taimaki Takawa’’

Sarki Sule na mai gyad’a kai cikin nuna 6acin rai ya ce

‘’ki nufin d’iyar mu ta na sauraran wani ba tare da sanin mu ba?’’

‘’ta yi kuskure, ayi mata afuwa’’

Cewar Hajja Kilishi, da ita kad'ai  ke iya bawa Sarki hakuri idan ya na cikin yanayin 6acin rai. Shiru ne ya biyo baya, kafin daga bisani Sarki Sule ya ce

‘’a shedawa wanda d’iyar mu ta ke saurara a bayan idon mu, ya zo nan da kwana biyu dal mu na so mu gana da shi’’

‘’shi ne Yarimar da aka d’aurawa amre da d’iyar bayi Allah ya huci zuciyar babban bijimi’’

Cewar Inna Salti a hankali kamar wacce ke tsoran maganar. Sarki na duban Gimbiya K’amariyya ya dad’a tambayar

‘’ku na nufin Badde na Fabarusa?’’

‘’Badde kuwa Allah ya k’ara ma ka lafiya’’

Ga mamakin su sai gani su ka yi Sarki ya murmusa, kafin ya k’ara da

"shin kin san ita d’iyar bayi a matsayinwa aka d’aura mata Badde?’’

Inna Salti wacce ta fara dana sanin furta maganar ta ce

" a matsayin Binta, Allah ja da ran ka’’

‘’wacece Binta?’’

Tambayar Sarkin Sule da ya sa kowani mahalukin da ke wajan sai da ya sha jinin jikin shi. Da kyar Inna Salti ta yi k’arfin halin furta

‘’d'iyar babban bijimi ce’’

Cike da 6acin rai ya ce

‘’ita Kamariyya da aka amrer da d’iyar bayi a matsayin kaunar ta, kuma ta zo mana da zancen alakarta da wanda aka d'aura din, ya ta ke so mu yi ma ta?’’

Shiru babu wanda ya iya furta komai. Idanun sa bisa silin yace

‘’an bar mu muna jira, ke mu ke sauraro K’amariyya!’’

Murya na rawa ta ce

‘’dama tin da haka abin ya kasance, na ke so a warware matsalar ta hanyar raba amren …….’’

‘’yashasheshshen zance!’’

Sarki Sule ya katse ta ta hanyar daka mata tsawa, tuni jikin K’amariyya da Binta ya hau k’yarma tsabagen firgici, kowa sai da ya sha jinin jikin sa,  Jakadiya ta durkusa ta na fad’in

‘’tuba mu ke ran Babban biji ya dad’a, Allah huci zuciyar Babban Biji, lafiya salamun’’

Sarki kuwa be gushe b ya cigaba

‘’mun biye mu ku mun bi san zuciya mun aikata ha’inci, hakik’a Sarki Abdulrahman ya kasanse mai zurfin tunani, mu kuma mun kasance daga cikin ma’abota san zuciya, fatan mu shi ne gyara wanga kuskure da mu ka aikata bisa san zuciya ba tare da 6ata dangantakar arziki da mu ka kulla a wanga rana ta yau ba’’

Kallan sa ya mayar ga Bintu, kana ya ce

‘’ina Kilishi?’’

‘’ran Takawa ya jima, gani kusa gaban ka’’

Cewar Hajja Kilishi.

‘’wagga d’iya ta arziki (yayi nuni ga Bintu) ta ma na abun da jinin mu basu ma na ba, sanadiyar ta yunwa ta kau a masarautar mu, idan ba mu maishe ta d’iya ba, ko shakka babu mu na daga cikin wanada ake kira butulu, wagga d’iya d’iyar mu ce, ni Sule na kira wagga d’iya da d’iya a gare mu, maza a shirya d’iyar arziki, idan an wayi gari ta bi tawagar masarautar Fabarusa dan kuwa jinkirin makwannin biyun ka iya zama barazana a gare mu, da zafi zafi akan bugi karfe…mun gama Magana’’

Ya na dasa aya ya tashi cike da Sarauta yayi shigewar shi daga ciki, ya na jiyo koken Gimbiya K’amariyya da Gimbiya Binta amma ya mu su kunne uwar shegu duk da kuwa har ran sa ya ke jin abun.

Ita kan ta Bintu jin gobe gobe za a wuce da ita hankalin  ta ya dad'a tashi, ta ma kasa motsawa daga in da ta ke, ta nemi kuka ta rasa.

Gimbiya K’amariyya kuwa wacce har shid’ewa ta ke tsabagen kuka da ya ci karfin ta, tuni ta sake fad’uwa sumammiya a karo na biyu. Nan waje ya sake kaurewa da salatin su Hajja Kilishi da Jakadiya. Dan kok’ari har da Bintu cikin kawo d’oki ta hanyar ciro mayafin ta, ta shiga yiwa Gimbiya K’amariyya fifita, yayin da Inna Salti ke yayyafa mata ruwa.

Wani k’akk’arfar ajiyar zuciya ta saki, alamar ta farfad’o, amma idanun ta lumshe ta kasa bud’e su, hawaye ke gudana bisa kuncin ta. Sai fa a sannan Gimbiya Binta ta ankare da Bintu da ke sunkuye bisa kan Didin na ta, sai fifita ta ke ma ta, ai kuwa ta daddage ji kake tas! Ta sauke yatsun ta biyar bisa kuncin Bintu sai da ta ga wuta a idanun ta. Hannun ta biyu bisa kuncin ta ta ke duban Gimbiya Binta, hakan ne ya dad’a k'ular da ita, ta sake d’aga hannu da niyar kai mata wani marin caraf Inna Salti ta ruke hannun ta, ta na mai fad’in

‘’kul kar ki kuskura ki sake! Kin san kuwa matar Yeriman Fabarusa ki ka d’aga hannu ki mara? Ina hankalin ki ya tafi?’’

Jin haka Gimbiya Binta kamar ta yi hauka, fad’i ta ke

‘’d’iyar bayi na mara, d’iyar bayi wacce na saba takawa ita na mara, babu wata matar Yariman Fabarusa da ta wuce Didi, duk makirci da munahunci wanga wulak’antacciyar Baiwa arudu ya k’are bisa kan ta! Ku ma mu zuba ni da ke ina mai tabbatar mi ki alkiyamar ki ta zo dan kuwa da ki tafi zuwa Fabarusa a gurbin Didi gwamma ki je ki kashe kan ki, dan kuwa masifa da balak’I ya na nan an tanadar mi ki, kuma shi za ki riska, sai dai uwar ki ta haifi wani…..’’

Ta juya fuuuu ta fice gudun kar Bintu ta ga hawayen ta, dan kuwa su ke sauka d’aya bayan d’aya tsabagen bakin ciki da takaici. Hajja Kilishi shi ce ta ja Bintu zuwa turakar ta dan neman yanda za a yi idanun Bintu da ya kumbura da shatin yatsun Gimbiya Binta ya baje, bayan Inna Salti ta bata baki bisa ga lamarin Gimbiya Binta da kuma mata alk’awarin irin haka ba mai sake faruwa ba ne. Nan su ka bar Inna Salti ta na rarrashin Gimbiya K’amariyya, domin kuwa bakin alk’alami ya bushe tuni.

🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
[

: ®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

5⃣

Da daddare bayan an idda sallar isha’i, Yarima Jafar da Yarima Barde zaune a falo sun yi jigum kamar wanda aka yiwa mutuwa, Khalil na daga d’aka ya na waya da matar sa.

Babban falo ne mai d'auke da k'ayataccun kujeru na sarauta, masauki ne da dama a ka tanada na musammam domin saukar bak'i na alfarma irin su Barde.

Tun da su ka isa ga masauki Barde ke zaune nan falon, sallah kad'ai ke iya sawa ya motsa. Shigar sa na d'aurin aure ke jikin sa, sai dai ya cire babbar riga da rawani, sumar kan sa kwance lub lub bisa kan sa.

'Daya daga cikin dogarawa da ke ciran kofa ne ya shigo ya zube gaban Yerima Barde, kana ya ce

‘’ran Yarima ya dad’e, Gimbiya K’amariyar d’iyar Mai martaba Sarki Sule na S’ayrasa ce me neman iso gare ka’’

Jin sunan K’amariyya tuni kafad’a Barde ta tasa, yayinda jijiyoyin wuyar sa su ka bayyana. Amma ya kasa furta komai. Yarima Jafar ne ya ce

‘’ka iso da ita gare shi’’

Dogari na mai fad’in

‘’an gama ran Yarima Ja’afar ya dad’e’’

Ya tashi da sauri ya fice. Yarima Ja’afar ma tashi yayi, ya d’an dafa kafad’ar Yarima Barde sa’annan ya shige ciki. Shigar sa ke da wuya Dogari ya shigo biye da shi Gimbiya K’amariyya ce. Sai da ya kawo ta gaban Yarima Barde sannan ya juya ya koma waje in da bayan Gimbiya K’amariyya ke tsumayin ta.

Tin shigowar ta ya kafa mata ido, har ta iso gare shi sanye cikin atamfa koriya wanda ta rufe da farar alkyabba ta alfarma. Duk tashin hankalin da ta ke ciki da kuma wanda Yarima Barde ke ciki be hana shi ganin kyauwun Gimbiya K’amariyya ba. Ga wani k’amshi mai saka kwanciyar hankali da ya kasa gane kan sa ke tashi daga jikin ta sa’in da ta zaune gaban shi. Yayi kok’ak’arin sanya kwayan idanun sa cikin na ta, amma hakan ya gagara kasancewar ta yi k’asa da na ta idanun.

‘’K’mariyya…..’’

Ta ji murya mai d’auke da tarin kwarjini ta daki kunnan ta, wanda tun da aka d’aura masa aure da Bintu, kwakkwarar kalma d’aya be fito daga bakin sa ba sai a yanzu da ya ga K’amariyya zaune gaban sa.

‘’K’amariyya’’

Ya sake kiran sunan ta a karo na biyu, maimakon ta amsa, kawai sai ta sa ma sa kuka, ya rasa yanda zai yi da ita dan kuwa Barde sam be iya rarrashi ba. Ta d’au lokaci mai tsayi ta na rera kuka gaban sa, tin ya na iya ba ta baki, har ya mata shiru dan kuwa shi dama Magana wahala ta ke masa. Sai da ta yi shiru dan kan ta, sannan ya dube ta, kana ya ce

‘’ban san kud’irin mahaifina ba, sai bayan da bakin alk’alami ya bushe, sai da aka d’aura min amre da kauna gun ki Fatima….’’

Jin haka Gimbiya K’amariyya ta kai duban ta gare shi, ta ga ya k’ara ma ta kyau da kwarjini na kwaran gaske, wai kuma an d’aura ma sa Bintu! Bintu dai d’iyar bayi! Ji ta yi kamar ta bud’e baki ta fad’a masa gaskiya komai ta fanjama fanjam, tunawa da ta yi da na ta Mahaifin ya sa ta a dole ta na ji ta na gani ta yi shiru, babu mamaki shi ya na da wani shiri ne na daban. Murya na rawa ta ce

‘’ina cikin damuwa Yarima, ina mafita?’’

Kallan ta yake na wasu dak’ikai, kafin daga bisani ya saki ajiyar zuciya mai karfi gami da sauke kafad’a, kana ya ce

‘’Allah shi ne mafita, shi za mu kai kukan mu gare shi, hallo bana yiwa Mahaifina musu, ban ta6a ba K’amariyya shi ya sa ma ki gaya aiwatar da wanga lamari ba tare da ya tuntu6e niba, yanzu ban da tsumi hallo ba dabara, amma ina so ki sani ina son ki, kwaran gaske’’

Cikin hawaye K’amariyya ta ce

"me zai hana ka sanar da Mahaifin ka gaskiya kamar yanda na sanar da nawa Mahaifin?’’

‘’ban da wannan ikon K’amariyya, da ina da shi da tuni na aiwatar da hakan’’

Cewar Yarima Barde ya na amai girgiza kai. Nan Gimbiya K’amariyya ta fusata, ta tashi da sauri za ta fita. Yarima Barde ma tashin ya yi, ya dakatar da ita ta hanyar fad’in

‘’kar ki yi fushi K’amariyya, kunar za ta min yawa, badan wacce aka d’aura min jinin ki ba ce kuma kauna gun ki da na ce duk duniya babu wacce na tsana face ita, sam ba za ta sami kulawa bare wani abu wai soyayya daga gare ni ba saboda soyayyar ki, hallo babu yanda zan yi dole haka zan zauna da ita har Allah ya kawo karshen zaman, dan darajar Mahaifan mu da Masarautun mu’’

Kallan sa ta ke yayinda hawaye ke gudana daga idanun ta, a hankali ta furta
‘’ina ma ka fatan alkhairi Yarima Badde’’

Sannan ta juya a hankali ta na ficewa. Tsayawa yayi ya na kallan ta yayinda ta ke ficewa daga rayuwar sa, idanun sa sun yi jajur, ji yayi k’afafun sa sun kasa d’aukar gangan jikin sa, a hankali ya zauna zuciyar sa cike da tunanin yanda rayuwar sa ta sauya a wuni d’aya. Shi ba mutum ba ne mai san mata, mata ne ma ke san sa da bibiyan sa. Tin da Allah ya had’a shi da Gimbiya K’amariyya, ita ce mace ta fari da ya ji ya na kauna zai kuma iya aura. Amma yau gashi an ma sa Katanga da ita ta hanyar aura ma sa kanwar ta. Yatsun sa ya tusa cikin sumar kan sa sanadiyar sarawa da ya ji kan sa na yi, ya na fad’in

‘’lahaula walakuwata illa billah!’’


🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2)

[8/14, 9:37 PM] Salma: FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

®

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

💌 SAK'ON NA MASOYA NE🤗

Ina mai neman afuwa kan jinkiri da aka samu na cigaban wanga littafi, Sidiya mai yawan hidama ce, da fatan za a cigaba da mata uzuri. Ina Godiya da kulawar ku. Sidiya ce ke mu ku fata na alkhairi🤝


WAIWAYE

Daga cikin Masallaci aka fara abinda ya had’a jama’a a wannan masarauta, wato d’aurin aure, in da aka umarci waliyin Ango da Amarya su matso kusa. Waziri ne ya fito daga 6angaran Sa’ayrasa, Fabarusa kuma Sarki Abdulrahaman ne ya nuna kan sa a matsayin waliyi.

Daga waje Khalil ne ke ta yiwa  Yarima Barde hira, amma shi ina hankalinsa na ga Gimbiya K'amariyya, Allah Allah ya ke a shafa fatiha ya tafi garera don jin soyayyar ta ya ke har ransa, bare kuma yau gabar da ke tsakanin Masarautasu za ta kau, za su yi soyayyarsu a zahirance ba tare da wani shakku ba. Jin an shafa fatiha Yarima Barde ya tashi ya na mai fad’in.
‘’Alhamdulillah tunda an amra sai ku tashi mu tafi ko?’’

Har Khalil da Jafar sun tashi, tuni su ka tsaya cak jin marok’a na fad’in

‘’An d’aura auren *Yarima Abubakar BARDE*  tare da *Gimbiya Fatima* akan sadaki (50000 CFA)"
Yarima Barde da sam bai lura da abinda su ka ji ba tsabagen hankalinsa ba ya wajan, a hasale ya kai kallonsa ga abokannasa ya na mai fad’in
‘’Me ku ke jira ne? Mu tafi, Allah Allah na ke na gana da Gimbiyata.’’
Su kuwa marok’a ba su fasa shela ba. Khalil ne yayi k’arfin hali ya ce
‘’Da ma kai ne Barde?’’
Cikin rashin fahimta Barde ya ce
‘’Ni ne wa?’’
‘’Angon da aka amrawa amren.’’
Jafar ya bashi amsa a tak’aice. Kai Yarima Barde ya girgiza cike da murmushin irin ban son rainin hankali fa. Khalil ya ce
‘’Saurara ka ji Barde’’
Nan kuwa muryar wani marok’i da ya zo giftawa ta dafda su ya doki kunnan Barde, fad’i ya ke
‘’An amra auren Yarima Abubakar Barde da Gimbiya Fatima....’’
Nan ya ya tsaya cak tamkar wanda aka zarewa rai, su kansu abokannasa sun girgiza kwaran gaske.

Daga cikin masallaci, ana gama d'aurin auren, inda kowa ya ke mamakin sauyin al’amura da aka samu, musammam jama’ar Sa'ayrasa, shi kuwa Aisar tunanin hanyar fita daga cikin jama’a yake, domin zuwa neman Bintu ba tare da Junaidu ya ankare ba. Bayin Sa'ayrasa ne d’auke da farantin goro da alawa, su ke bin kusirwa kusirwa in da suke mik’a farin tin jama’a na d'iba san ran su.
Bawan da ya zo kusurwar da su Aisar su ke, Aisar ya fara mik’awa, in da ya girgiza masa kai alamar ba ya buk'ata, har bawan zai wuce, nan idanun Aisar su ka sauka bisa yatsun bawan, me zai gani? Zobensa da ya bawa Bintu ne cikin yatsun na shi, bai ankara ba sai ji yayi Aisar ya damk’o hannunshi, a tsorace bawa ya saki farantin hannun sa dan ko shakka babu ya san tawagar shugaban k’asa ne gabansa.Hakan ya dawo da hankalinsu Junaidu da sauran ‘yan tawagar garesu. Aisar na mai duban idanun bawan ya furta
‘’Ina ka sami wagga zo6en? Menene dangantakarka da mai zo6en? Ina Bintu d’iyar bayi?’’

Babban gida kuwa 6angaran Jakadiya, Bintu na zaune tare da su Jakadiya sai ga Gimbiya K’amariyya ta shigo, ta yi kyau kwarai cikin jajayen kaya, ta d’aura alkyabba ruwan zuma bisa kayan, ga bayi nan biye da ita. Ta zo kar6ar mabudin wajan aje baki na musammam domin kar6ar Yarima Barde.

Ta na zaune ta na jiran Jakadiya ta shiga ciki dan d’auko mata mabud'in, su ka ji an shigo 6angaren Jakadiya an gud’a. Tuni hanjin cikin Bintu ya kad’a don kuwa ta san ta faru ta k’are an yiwa mai dami d’aya sata, aure dai an aura. Tuni ta fashe da kukan da dama ya tsaya k’asan mak’ogaran ta.
Jakadiya ta fito d’auke da mabud’i, yayinda Ladiyo ta shigo jiki na rawa, sai tafa hannu ta ke cikin salati da sallallami. Jakadiya ce ta tambaya ko lafiya, yayin da hankalin kowa ya koma gareta.
Cike da ladabi Ladiyo ta durk’usa gaban Jakadiya ta na mai fad’in
‘’Yau na ga lafiyar Allah Maigari gauro talaka da mata hud’u.’’

Cikin k’aguwa Gimbiya K’amariyya ta ce
‘’Me ya faru ne Ladiyo?’’

‘’Wato Allah shi taimaki Gimbiya, ji da gani dai ba ya k’arewa sai randa kurman bebe ya makance, Sarki Abdulraman na Fabarusa cike ya ke da abin mamaki, wani lamari sai shi.....’’
‘’Yo to wani abin mamaki? Ya ce ya fasa ne?’’
Jakadiya ta tambaya cikin rashin fahimta. Kana Ladiyo ta ce

‘’Eh to ya fa fasa be kuma fasa ba, da ya tashi yin bazata, sai ya amrawa d'ansa Barde Bintu.....’’
Hakan yayi daidai da ihun da Gimbiya K’amariyya ta kurma ta na mai zubewa k’asa sumammiya. Nan da nan aka yi kanta. Bintu kuwa yanda maganar ya doki kunnenta ta tabbatar ta zama kurma, don kuwa ba ta jin hayaniyar da ake gabanta
‘’Ya amra ma d’an sa Barde Bintu....’’
Maganar da ke ihu jikin kunnenta kenan.









®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE! (2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

1⃣

Tuni waje ya kaure da salati da salallamin bayi, Jakadiya ce ta sa aka yi maza aka shigar da K’amariyya daga cikin d’aki gudun gulman da ta san tabbas sai ta yad’u daga bakin bayin da ke wajan. Bintu kuwa ta ma kasa gane komai, kukan ta kawai ta ke, aure dai an d’aura mata, ko ta na so ko ba ta so tafiya ne dole a tafi da ita. Gashi a rasa wanda za a d’aura mata sai saurayin Gimbiya K’amariyya, Yerima Barde na Fabarusa! Hannu biyu Bintu ta d’aura bisa kan ta ta na mai fad’in

‘’Wayyo ni Bintu alk’iyama ta ta zo’’

Daga cik’in uwar d’aka, bayan an kori duka bayin da ke b’angaran Jakadiya, Hajja Kilishi da Inna Salti wanda Jakadiya ta aika Ladiyo da Kyallu su sheda ma su abun da ke faruwa ne su ka shigo d’aya na bin bayan d’aya, biye da su Gimbiya Binta ce, wacce ita ma labari tuni ya je mata.
Jakadiya ta umarci  bayin da su ka taka mata baya su yi jiran ta waje. Bayan an watsa ma Gimbiya K’amariyya ruwa, da rokan Allah ta farfad’o ta na mai bin su da kallo kamar lokacin ta fara ganin fuskokinsu. Kanta bisa kan cinyar Inna Salti, Jakadiya zaune gaban ta sai kuma Gimbiya Binta wacce ta dad’e da gigicewa da jin lamarin da ya faru, in ban da kuka babu abinda ta ke don gani ta ke duk laifin Bintu ne ko shakka babu ita da uwarta ne su ka sa musu hannu wannan balk'in ya fad’a kan ‘yar uwarta.

Ko da idanun Gimbiya K’amariyya ya sauka kan Gimbiya Binta, ita ma d’in ta fashe da kuka don sai a sannan ne ta dawo cikin hayyacinta sosai. Cike da damuwa Hajja Kilishi ke tambayar

‘’Menene ne? Gide menene ke faruwa? Tun dazu fa nake tambayar ki Binta amma amsa ta gagara daga gareki, yanzu kuma mun samu ta farfad’o maimakon a sami sauki ina, kun maishe da gida kamar wajan makoki! Shin ba kwa gudun abinda zai je ya dawo? Kun fa san gidan ga cike yake  da baki da kyar na sami hitowa daga cikin jama’a, ko rufa mana asiri ku sheda mana abun da ke faruwa.’’

Cikin kuka muryarta dak’yar ya ke fita, Gimbiya K’amariyya ta amsawa Hajja Kilishi, ta na mai fad’in

‘’Na shiga uku Hajja, Inna Salti na shiga uku, na d’au wuk’a na dab’a ma kaina, Allah Ya nuna min ikonSa, Barde…..Yarima Barde na Fabarusa……’’

Kuka ya ci k’arfinta, ta kasa k’arasawa sai shasshek’a ta ke. Cikin rashin fahimta Inna Salti ta ce

‘’Barde? Me ya faru da Barde na Fabarusa?’’

‘’Ni kam ta dad’a sa kai na cikin duhu, jakadiya wagga yarinya ba gamo ta yi ba kuwa?’’

Cewar Hajja Kilishi cike da damuwa.

‘’Yarima Barde da Didi masoya ne, shi ne dalilin ta na k’in amincewa ta auri sarkin Fabarusa wanda yake mahaifi a gareshi.’’

Gimbiya Binta ce ta amsa ma su.

‘’Kayya! Kai wagga lamari da me yayi kama! Kun ga irin ta ko? Gashi dai an cuci d’iyar mutane kin kuma cuci kanki K’amariyya, anyi gudun gara an tadda zago! Jakadiya dai ga irinta nan dai kin gani don kuwa wagga kulli ke da wagga d’iya ku ka kulla.’’

Fad’in Inna Salti ta na mai nuna matuk’ar b’acin rai.

Jakadiya da tunda aka fara maganar ta sha jinin jikin ta, jikinta ya yi sanyi kamar wacca aka tsunduma cikin ruwan sanyi cewa ta yi

‘’Uhum Allah shi ja da ran ki, yo to ni me zance? Ni ina naga ta ce wa? ‘’

Cikin kuka don kuwa idanunta sun rufe K’amariyya ta furta

‘’Don Allah ku taimaka a warware wanga lamari, don Mai Sama, kwarankwatsa zan iya rasa rayuwata, dan Allah ayi maza a shedawa takawa kafin na rasa raina, Ammu ki taimaka min…..’’

Kai Hajja Kilishi ta jinjina kafin ta ce

‘’Gide Takawa zai saurari wanga azzance kuwa Jakadiya? Yanzun ga ya na can wajan liyafar d’aurin amren nan......’’

Kafin Jakadiya ta amsa Gimbiya Binta ta yi saurin taran numfashin ta ta hanyar fad’in

‘’Ku taimaka tun kafin a makara, dan kuwa ba Sidi ba ko ni ma ina tara muddin ba a warware wanga
amre ba, ya d’iyar bayi za ta amri mutum kamar Barde, dan Allah Jakadiya ki sama mana mafita tun kan na had’iyi zuciya na mutu dan kuwa ciwon da na ke ji ya ma fi na Didi’’

‘’Makara kam an riga an makara, saidai fa a jira bayan komai ya lafa a yiwa Takawa magana watakil shi bai zai rasa dabara ba.’’

Cewar Hajja Kilishi yayin da tashi tsaye jiki sanyaye, tak’ara da fadin.

‘’Kunsan mu na da baki, duk abinda za ku yi kada ku manta da martabar Takawa, ku kula ku kame kanku kada ku jawo mana abun da zai halaka yankin ga gaba d'aya’’

Ta na gama Magana ta juya abun ta ta fice, ta bar Inna Salti tare da Jakadiya cikin al’ajabi. Gimbiya Kamariyya gani ta ke sam Hajja Kilishi ba ta damu ba saboda ita dama ba ta ta6a haihuwa ba shi ya sa sam ba ta damu da lamarinsu ba. Ita kuwa Gimbiya Binta abinda ya tsaya mata a rai bai wuce na ta na murnar raba Bintu da masoyin a Aisar, sai gashi ta zama matar wanda har ta gama rayuwar ta a doran k’asa ba za ta sami kamar shi ba, abun takaici ta yiwa yar uwarta asarar masoyi, duk akan wanda sam be ma san ta nayi ba.



🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
[8/14, 9:37 PM] Salma: ®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

2⃣

Daga cikin masallacin Sa’ayrasa, ko da bawa ya tsinci kansa gaban Aisar, hannunsa damke cikin na sa yayinda yake jero masa tambayar da shi kansa bai ta6a jin ko da makamancin sunan ba a matsayinsa na bawan barga da kwananan ya dawo cikin sawun bayin da ke kula da lambu. Zufa ne ya shiga keto masa, cikin kame-kame da in’ina ya ce

‘’Eye? Na’am lillahi warasulihi wanga zoben tsintarsa na ka yi, idan kuwa na yi karya aratta kashe ni….’’

Maimaikon Aisar ya saki bawa sai dad’a damke hannu bawa yayi. Cikin neman d’auki bawa ya kai dubansa ga sauran yan tawagar na shugaban k’asa ya na mai neman d’oki. Hakan yasa Junaidu tausaya ma bawan duk da ko shakka babu ya san zoben hannun bawa mallakin d’an uwansa ne. Kana ya na mai shiga tsakanin bawa da Aisar ta hanyar ciro hannun Aisar daga cikin na bawa yayinda yayiwa bawa nuni da ya ciro zoben, nan da nan bawa ya ciro zoben, ya mik'awa Junaidu kai durkushe ya na mai fad’in

‘’Tuba na ke, aradun Allah tsinta na kai, ku min rai……’’

Nan bawa ya fashe da kuka, wanda hakan ba k’aramin dad’a kular da Aisar ya yi ba, ji yake kamar ya shek’eshi har sai ya matso gaskiya daga bakin bawan.

‘’Ka ga ba kuka za ka yi ba, babu abun da zai ma muddin ka fad’a masa gaskiya, shin in aka sami wanga zoben?’’

Cewar Junaidu ya na mai kok’arin saka idanunsa cikin na Bawa don gano inda bawa ya dosa. Shi kuwa bawa ya gama rikicewa sai rantse rantse kawai yake, fad’i yake

‘’Tsinta na ka yi, kwankwasi tsinta na ka yi a lambu, aradu tsinta na ka yi.’’

Jin an furta
‘’Ko shakka babu gaskiya ya ka fad’i, don na shedi wanga bawa mai gaskiya ne.’’

Gaba d’aya hankalinsu ya koma ga mai maganar. Sanye ya yake cikin bakar jamfa wanda aka masa ado da bakin zare, idan ka d’auke rawaninsa da yake fari komai na jikinsa bak'i ya sanya, kai kace wani taron bakin ciki ya halarta, ko da shike a nasa 6angaran hakan ta ke. Kallo d’aya Aisar ya masa ya d’auke kai ya na fad’in

'’A matsayinka na wa za mu k’ar6i shedanka?’’

‘’A matsayinsa na Yarima Nuhun Sa’ayrsa ranka shi dad’e.’’

Fad’in bawan da ke tafe da Yarima Nuhu kenan, ganin idan ba a yi dagaske ba yanda ran Yarima Nuhu ya ke a dak’ule komai mai  afkuwa ne. Jin haka Junaidu ya bawa Yarima Nuhu hannu suka gaisa haka sauran yan tawagar amma ban da Aisar wanda idan ransa yayi dubu ya 6aci, don haka a kusa ya ke. Sanin hakan ne ya sa Junaidu yin saurin yiwa Yarima Nuhu bayani, ya na mai nuna ma sa zoben. Ganin zoben da kuma jin wanda Aisar ya ke tambaya Yerima Nuhu ya san ko shakka babu Bintunsa ta arziki a ke nema, zoben nan shine zoben da ya kar6a daga hannunta ya wulgar. Wato wannan shi ne Aisar d’in da yake soyayya da Bintunsa….

Bawan nan dai da ke tafe da Yarima Nuhu ne cike da ladabi ya furta

‘’A hakik’anin gaskiya wanga bawa ada bawan barga ne, be dad’e da dawowa sahun bayinmu masu kula da lambu ba, saboda haka ina mai tabbatar maka ba zai san wagga d’iyar bayi da ku ke magana akai ba, dan yanda alama ya nuna ko shakka babu ta na daga cikin bayin cikin babban gida tun da har aka iya tsintar zoben hannunta cikin lambu, haka nima da na ke bawan kofar gabas, ba mai yiyuwa ba ne na santa, domin kuwa ba mu da wata alak’a da zai had’amu da bayin cikin babban gida’’

‘’Shin ina za mu sami wagga d’iya?’’

Aisar ya tambaya ya na mai fatan samin mafita daga bakin bawa. Nan take bawa ya masa alk’awarin tayashi cigiyar Bintu nan ba da dad’ewa ba, sannan su ka sallami wannan bawa da zoben Bintu ke gareshi. Yarima Nuhu ya shaida mu su abinda ya kawo shi gare su, wato sheda ma su ana buk’atar su d’akin taro. Ya na gama shaida mu su yayi gaba dan kuwa yanzun da ya gane Aisar shi an samrayin da ya kwace zuciyar Bintu ya fi ma sa d’aci akan auren da aka d’aurawa Bintu a yau, dan wannan ya san ba mai d’orewa ba ne musammam idan aka yi la'akari da wanda aka d’aura mata.

Dakyar Junaidu ya lalla6i Aisar, sai da ya masa tuni da ba fa su kad’ai ba ne, akwai manya cikinsu, sun zo d’aurin aure ne bisa wakilcin shugaban k’asa ba wai hakan nan bak’akatan su ka zo ba, sannan ya samu ya d’an shawo kansa, ta hanyar  masa alk’awarin bayan komai ya lafa Junaidu da kansa zai tsaya har sai sun samo Bintu kafin su juya gida, ko da kuwa hakan ya na nufin raba tafiya da tawagar ta su. Da wannan su ka yi tattaki zuwa d’akin taro ba tare da sun bari manya daga cikinsu sun fahimci abinda ke faruwa ba.

Yarima Barde kuwa da  dabara Yarima Jafar da Khalil su ka ja shi mota, gaba d’aya ya zame mu su tamkar mutum mutumi, ya d’auke mu su wuta. Cikin mota sai da su ka d’au kusan rabin awa babu wanda ya iya furta komai.

Dogarin Masarautar Fabarusa ya zo ya buga musu kofa, nan ya zube ya na mai sheda mu su umarnin Sarki Abdulrahman na a ma su iso gareshi.

‘’Su na cikin masallacin ne?’’

Yarima Jafar ya tambaya, in da Dogari ya ba shi amsa da

‘’A'a, sun wuce ga d’akin taron masarauta tunda jimawa, Yarima kad’ai ake tsimayi ranka shi dad’e.’’

‘’Mu na nan tafe.’’

Cewar Khalil, yayinda Dogari ya tashi da sauri ya na fad’in

‘’A iso lafiya.’’

Yarima Jafar na duban Yarima Barde ya ce

‘’Ka bawa zuciyarka hakuri mu amsa kiran Mai Martaba’’

Ko kallonsa be yi ba bare ma ya nuna alamar ya san da shi ake, kamar an aje dutse. Ganin haka Khali ya ce da Yarima Jafar.

‘’Ka san halin Barde a sama ya ke, ina zaifi mu lalla6a mu je a dai ga fuskarshi, in ya so sai mu nemi izinin tafiya ta hanyar ba da uzirinmu ga Mai Martaba.’’

Da wannan shawara su ka fito daga motar, amma Yarima Barde fitowa ta ma sa wuya, sai da Yarima Jafar ya ma sa tuni akan wanda ya sa a yi kiransa sannan ya fito cike da k’asaita, dama shi idan ransa ya 6aci nan fa sarautar ta sa ke bunk’asa. Ko da dogarawan da ke tsimayinsu su ka ga fitowarsa tuni su ka rufa musu baya, zuwa d’akin taro, kai kace Sarki Abdulrahman na Fabarusa ne da kansa ke tafe.

🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

: ®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

3⃣

Dakin taron ya cika fal da jama’a, tawagar Aisar da shigowar su ke nan, na su 6angaran na shugaban k’asa su ka zauna. Haka ma hakiman Sa’ayra da Fabarusa, Agadez, Diffa da sauran Hakiman yanki da sassa na jamhuriyar Nijar wajan su na musammam su ka zauna. Haka kuma yankin Sarakuna wanda Sarkin Sa’ayrasa mai gayya mai taro ya hakimce, kusa da shi kuma Sarkin Fabarusa ne zaune cikin aminci. Hakan ba k’aramin farantawa jama’a rai yayi ba, wai ashe dai akwai ranar k’arshen gaba tsakanin Sa’ayrasa da Fabarusa? Shin dama akwai rana irin ta yau da za a ga Sarakunan wanga yanki zaune cikin aminci?

Busa na alkgaita ke tashi daga waje, jama’ar Sa’ayrasa kwan su da kwarkwatar su sun yi dandazo cikin d’akin taro, murna gun su ba a cewa komai domin kuwa a yau yunwa zai kau a k’asar su. Ganin shigowar su Yarima Barde tuni dogarai su ka hau yiwa ango kirari. Shi kuwa  Yarima Barde sam ba cikin hayyacin sa ya ke ba, amma in aka  d’auke Yarima Jafar da Khalil wanda dama sun san halin da abokin na su ya ke ciki babu wanda zai kalle shi ya ce ya na cikin wani hali, sai dai ma ayi tsammanin tsabar sarauta da miskilanci ne yake d’ibar sa.

Sai kuma Mai martaba Sarki Abdulmalik na Fabarusa, wanda kallo d’aya ya yiwa d’an na sa Yarima Barde bayan ya kai gaisuwar sa ga Mai martaba Sarki Sule na Sa’ayrasa, ya gane halin da ya ke ciki, kasancewar wajan mahaifin na shi ya yo gadan kafiya, cijewa da kuma yin burus kamar be san abun da ke faruwa da shi ba, amma in aka tona cikin zuciyar su, Allah kad’ai ya san tafasar da ta ke. Murmushi Mahaifin na sa yayi, cikin ran sa kuwa yacewa ya yi

"d’an mu  Abubakar, alkhairi ne mu ka kulla ma ka ba sharri ba, nan gaba za ka gode ma na kwaran gwaske’’

Ganin Yarima Barde durk'ushe gaban Sarki Sule, haka ma abokan na sa biyu, hannun su na dama dunkule suna mai jinjina ga Sarki Sule, fadawan Sa'ayrasa su ka amsa ma su da

"Jinjine dama lafiya alher, gaishe ka Yarima Badde, an gaishe ku samari"

Sarkin Sa’ayrasa kuwa cikin nuna ya amsa gaisuwar ta su shi ma ya dan daga na shi hannun daman a dunk'ule. Yarima Barde ya shiga ran sa saboda kamala da kwarji na sa, ji ya ke ina ma ina ma, ina sirikin na sa ne na gaske, da ya san haka Sarkin Fabarusa zai aikata, da ya bayar da d’iyar sa ko da kuwa ba a san ran ta ba ne.

Ko da Yarima Barde ya had’a ido da Mahaifin na sa, sai ya yi saurin saukar da na sa idanun. Duk wannan abun da ke faruwa a kan idanun yayan Barde, wato Yarima Sadauki na Fabarusa wanda tun da ya ji abun da mahaifin na su ya aikata bisa ga auran da ya d'aura ya k'ara jin tsanar Barde ya dad'u a kirjin sa. Domin kuwa shi ya kamata Sarki ya d'aurawa aure shi da ya ke babban d'an sa ba k'anin sa, hakan da yayi shi ya nuna k'arara Sarki Abdulraman ya fi kaunar Barde, ya kuma fi fifita shi akan Sadauki. Hakan ne kuma Yarima Sadauki ba zai lamun ta, dan ya san ba k'aramin girma aka zubar ma sa ba a idanun jama'a, dole kuma ya d'au Mataki. Idanun sa kan Barde, cike da tsana ya ke duban sa yayin da aka yiwa su Barde nuni ga na su wajan zaman, wato kusa da Yarima Sadauki da abokan sa su ka zauna.

Tun shigowar su Yarima Barde idanun Yarima Nuhu ke kan sa, ji yake kamar ya je ya sheda ma sa wacece Bintu in ya so kowa ma ya rasa. Haka ma Aisar wanda ya san burin Bintu na ganin Yarima Barde ko da sau d’aya ne a rayuwar ta, wai ta rasa wanda za ta kira mai kyawun duniya sai wanga buzu! Cewar Aisar cikin ran sa yayinda wani bakin kishi ya ta so ya mamaye ran sa, shi dai fatan sa Allah ya sa ya sami damar ganin Bintu tin ka a tafi da ita cikin bayin da za su raka gimbiya Binta Fabarusa, ko dan Yarima Barde dole ya d’auke ta, sam jinin su be had’u ba, dan haka Bintun shi ba za ta yiwa matar Barde bauta ba, ko da kuwa duka dukiyar sa za a buk’ata domin mallaka ma sa Bintu, a shirye ya ke ya rasa komai.

Bayan an sami nutsuwa ne aka bud’e taro da addua’a, sannan aka shiga abun da ya tara su a wajan. Su Yarima Jafar sun so su nemi izinin tafiya, amma hakan be samu ba, sai hakura su ka yi su ka zauna kamar gumaka, ba um ba um um, ga abokan Yarima Sadauki da shi kan shi Yarima Sadauki sai harbin iska su ke. Barde kam duk be san ana yi ba.

Sarkin fabarusa ne ya fara jawabi, ya mai nuna farin cikin sa na kulla aminta da auratayya wacce ta kawo k’arshen gaba tsakanin Masarautar ta su biyu. Bayan haka ya gabatar da takardar shedar sun bayar da bashin da masarautar Sa’ayrasa su ka buk’ata, ya kuma ce tun da an zama d’aya, sa iya biya a tsanake sannu a hankali ba tare da tashin hankali ba.

Nan waje ya kaure da ihu da sowa na jama’a, kowa na nuna jin dad’in sa da kuma alfahari da halin girma irin na sarkin Fabarusa. Dogarawan Fabarusa su ka shiga jera kirari ga Sarkin Su, fad'i su ke

"Lafiya Sarkin yakin Sarkin musulmi
Lafiya maida garin wani kango
Lafiya Barden mahadi
Lafiya Sukukun bakaka
Lafiya Darzaza amalen sarakuna
Lafiya ba hau da wani ba sauke wani
Lafiya hana kangara
Lafiya Sakaka babban bako
Lafiya Bango madafar bayi
Lafiya hadarin kasa maganin mai kabido
Lafiya kwankwason jimina mai wuyar shafawa. Lafiya adali, lafiya salamun, salamun salamun"


Jikin sarkin Sa’ayrasa ba k’aramin sanyi yayi ba. Sai da waje ya lafa sannan Sarki Abdulraman ya k’are jawabin na sa da adduar zaman lafiya tsakanin Masarautar da kuma fatan Allah ya bawa shugaban k’asa lafiya.

Sai da sarkin Sa’ayrasa ya sa hannu a takardar ta hanyar amfani da hatimin masarautar ta sa, yayi na sa jawabin na nuna farin ciki da godiya ga masarautar Fabarusa, sannan kuma ya yaba da halin dattako na Sarki Abdulrahman dan har ga Allah ya bashi mamaki matuk’a. ya k’are jawabin na sa tare da fatan alkhairi tsakanin Masarautar biyu. Cikin ran sa ya na alhinin aurar da d’iyar bayin da yayi maimakon d’iyar sa, maimakon ya kawo k’arshen gaba, gudunmawar dad’a k’arfafa gaba yayi muddin sarkin Fabarusa ya fahimci yanda ya haince shi saboda san zuciya.

Daga tawagar shugaban k’asa Kwaminishinan da yayi jawabi ne ya mik’a gaisuwar shugaban k’asa tare da gudunmawar sa na buhuhunan hatsi, shinkafa da dabino ga masarautar ta Sa’ayrsa, wanda sam kyautar ta shi ba burge su ta yi ba, a fad’ar su sai da yunwa ta ci ta cinye su har su ka kai ga neman taimako gun abokan gaba sannan zai wani kawo musu gudunmawar sa na bogi. Kafin  kwaminishna ya k’are jawabin sa, wayar Junaidu ta d’au k’ara, ko da ya amsa kiran tuni fuskar sa ta canza, cikin dabara ba tare da ya bari an san halin da ake ciki ba ya ja Aisar su ka yi waje.

A cikin mota ya ke sheda masa ai jikin Shugaban kasa ya dad’a tashi kiran da aka masa kenan, su za su fara yin gaba in ya so sauran tawagar za biyo su a baya gudun kada a d’aga hankalin jama’a. Aisar ya na ji ya na gani haka su ka bar yankin Sa’ayrasa, ya na mai kudirin dawowa da sun sami kan Shugaban k’asa.

Daga d’akin taro kuwa tawagar shugaban k’asa sai neman su Aisar su ka yi su ka rasa, bayan sun kira su ne su ke sheda mu su ai sun yi gaba saboda wani uziri da ya taso, duk da dai ba du sheda mu su ainihin abun da ke faruwa ba, sai da jikin su yayi sanyi matuk’a.

An kamala taro yayinda aka ci aka sha, dan kuwa yau take salla a masarautar Sa’ayrasa. Yarima Jafar ne ya nemi a kai su ga masaukin su da ke su dama nan Sa’ayrasa za su kwana su da tawagar Yarima Sadauki. Amma bakin ciki da kuma Allah Allah da ya ke ya bud'e ido ya gan sa a Fabarusa domin shedawa Mahaifiyar sa cin fuskar da aka masa ya sa Yarima Sadauki fasa kwana, nan ta ke ya juya shi da tawagar sa ba tare da sun jira Sarki ba. Su Yarima Barde kuwa da wasu dogarawa aka had’a su domin kai su masaukin su.

🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪H