®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
💌 SAK'ON NA MASOYA NE🤗
Ina godiya da babban murya ga masoyan Bintu d'iyar bayi, na gida Nigeria da kuma mak'ota Nijar. Ina alfahari da ku.
Sidiya ce ke mu ku fata na alkhairi🤝
2⃣7⃣
Daga cikin Masallaci aka fara abinda ya had’a jama’a a wannan masarauta, wato d’aurin aure, in da aka umarci waliyin Ango da Amarya su matso kusa. Waziri ne ya fito daga 6angaran Sa’ayrasa, Fabarusa kuma Sarki Abdulrahaman ne ya nuna kan sa a matsayin waliyi.
Daga waje Khalil ne ke ta yiwa Yarima Barde hira, amma shi ina hankalinsa na ga Gimbiya K'amariyya, Allah Allah ya ke a shafa fatiha ya tafi garera don jin soyayyar ta ya ke har ransa, bare kuma yau gabar da ke tsakanin Masarautasu za ta kau, za su yi soyayyarsu a zahirance ba tare da wani shakku ba. Jin an shafa fatiha Yarima Barde ya tashi ya na mai fad’in.
‘’Alhamdulillah tunda an amra sai ku tashi mu tafi ko?’’
Har Khalil da Jafar sun tashi, tuni su ka tsaya cak jin marok’a na fad’in
‘’An d’aura auren *Yarima Abubakar BARDE* tare da *Gimbiya Fatima* akan sadaki (50000 CFA)"
Yarima Barde da sam bai lura da abinda su ka ji ba tsabagen hankalinsa ba ya wajan, a hasale ya kai kallonsa ga abokannasa ya na mai fad’in
‘’Me ku ke jira ne? Mu tafi, Allah Allah na ke na gana da Gimbiyata.’’
Su kuwa marok’a ba su fasa shela ba. Khalil ne yayi k’arfin hali ya ce
‘’Da ma kai ne Barde?’’
Cikin rashin fahimta Barde ya ce
‘’Ni ne wa?’’
‘’Angon da aka amrawa amren.’’
Jafar ya bashi amsa a tak’aice. Kai Yarima Barde ya girgiza cike da murmushin irin ban son rainin hankali fa. Khalil ya ce
‘’Saurara ka ji Barde’’
Nan kuwa muryar wani marok’i da ya zo giftawa ta dafda su ya doki kunnan Barde, fad’i ya ke
‘’An amra auren Yarima Abubakar Barde da Gimbiya Fatima....’’
Nan ya ya tsaya cak tamkar wanda aka zarewa rai, su kansu abokannasa sun girgiza kwaran gaske.
Daga cikin masallaci, ana gama d'aurin auren, inda kowa ya ke mamakin sauyin al’amura da aka samu, musammam jama’ar Sa'ayrasa, shi kuwa Aisar tunanin hanyar fita daga cikin jama’a yake, domin zuwa neman Bintu ba tare da Junaidu ya ankare ba. Bayin Sa'ayrasa ne d’auke da farantin goro da alawa, su ke bin kusirwa kusirwa in da suke mik’a farin tin jama’a na d'iba san ran su.
Bawan da ya zo kusurwar da su Aisar su ke, Aisar ya fara mik’awa, in da ya girgiza masa kai alamar ba ya buk'ata, har bawan zai wuce, nan idanun Aisar su ka sauka bisa yatsun bawan, me zai gani? Zobensa da ya bawa Bintu ne cikin yatsun na shi, bai ankara ba sai ji yayi Aisar ya damk’o hannunshi, a tsorace bawa ya saki farantin hannun sa dan ko shakka babu ya san tawagar shugaban k’asa ne gabansa.Hakan ya dawo da hankalinsu Junaidu da sauran ‘yan tawagar garesu. Aisar na mai duban idanun bawan ya furta
‘’Ina ka sami wagga zo6en? Menene dangantakarka da mai zo6en? Ina Bintu d’iyar bayi?’’
Babban gida kuwa 6angaran Jakadiya, Bintu na zaune tare da su Jakadiya sai ga Gimbiya K’amariyya ta shigo, ta yi kyau kwarai cikin jajayen kaya, ta d’aura alkyabba ruwan zuma bisa kayan, ga bayi nan biye da ita. Ta zo kar6ar mabudin wajan aje baki na musammam domin kar6ar Yarima Barde.
Ta na zaune ta na jiran Jakadiya ta shiga ciki dan d’auko mata mabud'in, su ka ji an shigo 6angaren Jakadiya an gud’a. Tuni hanjin cikin Bintu ya kad’a don kuwa ta san ta faru ta k’are an yiwa mai dami d’aya sata, aure dai an aura. Tuni ta fashe da kukan da dama ya tsaya k’asan mak’ogaran ta.
Jakadiya ta fito d’auke da mabud’i, yayinda Ladiyo ta shigo jiki na rawa, sai tafa hannu ta ke cikin salati da sallallami. Jakadiya ce ta tambaya ko lafiya, yayin da hankalin kowa ya koma gareta.
Cike da ladabi Ladiyo ta durk’usa gaban Jakadiya ta na mai fad’in
‘’Yau na ga lafiyar Allah Maigari gauro talaka da mata hud’u.’’
Cikin k’aguwa Gimbiya K’amariyya ta ce
‘’Me ya faru ne Ladiyo?’’
‘’Wato Allah shi taimaki Gimbiya, ji da gani dai ba ya k’arewa sai randa kurman bebe ya makance, Sarki Abdulraman na Fabarusa cike ya ke da abin mamaki, wani lamari sai shi.....’’
‘’Yo to wani abin mamaki? Ya ce ya fasa ne?’’
Jakadiya ta tambaya cikin rashin fahimta. Kana Ladiyo ta ce
‘’Eh to ya fa fasa be kuma fasa ba, da ya tashi yin bazata, sai ya amrawa d'ansa Barde Bintu.....’’
Hakan yayi daidai da ihun da Gimbiya K’amariyya ta kurma ta na mai zubewa k’asa sumammiya. Nan da nan aka yi kanta. Bintu kuwa yanda maganar ya doki kunnenta ta tabbatar ta zama kurma, don kuwa ba ta jin hayaniyar da ake gabanta
‘’Ya amra ma d’an sa Barde Bintu....’’
Maganar da ke ihu jikin kunnenta kenan.
Tammat Bihamdillah
Nan na kawo k’arshen Bintu d’yar bayi ce kashi na farkon, sai a dakace ni zuwa bayan sallah da rai da lafiya. Ina mai mu ku fatan yin azumi cikin k'oshin lafiya. Dan Allah ku saka kawuna marigayi Alhaji Aliyu Abdullahi Sidi (A.A Sidi) cikin addu’a, Allah ya ji kan sa da rahama.
Allah ya sada mu da alkhairin sa. Sidiya ce ke mu ku fatan alkhairi.
HASKE
Sa'ayrasa
S anah
Ay aisha
Ra shida
Saƙlma
Fabarusa
FA=Fatima/Farida
B=Batool
R=Rufaida
U=Ummuabdoul
S=Sidiya
A=Asma'u/Bingel.
Monsieur Malam
École Makaranta
Madame Malama
Ciseaux Almakashi
Gide Ke
Hallo Kuma/ haka zalika
Rariya Waje
Aratta kashe ni
Kwankwatsi
Aradu Rantsuwa
Kwana Bacci
Amre. Aure
Wagga/wanga Wannan
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
No comments:
Post a Comment