®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
©Khadija Sidi.....✍🏼
0⃣8⃣
Tin da Iya Dije ta fara jawabi idanun Aisar da ya k’ada yayi jajur ke bisa fuskar Bintu, wacce ke zaune kusa da Iya Dije kan ta sunkuye. Zaune su ke offishin Malam Hashim, dan kuwa gari na wayewa ko taron d’alibai(Asembly) ba a yi ba Iya Dije ta ja Buntu zuwa ofishin, ta na cikin masa jawabi ne Aisar ya shigo sanye da wannan shigar na sa da ya saba, wato (suite) amma wannan karan ruwan k’asa ya saka.
Shigowar Aisar babu alamar da Malam Hashim be yiwa Iya Dije na ta yi shiru ba,
amma ina ta kasa d’aukan haske. Hankalin sa ba k’aramin tashi yayi ba ganin Asar ya tashi tsaye a fusace ya na mai maimata ‘’ta saka Ciseaux (Almakashi) ta yanke sumar Bintu!’’ shima Malam Hashim d’in tashi yayi, ya na yiwa Iya Dije alama da ido na ta rufa asiri ya ce "Ciseaux kuwa uwa Iya Diya?’’
Ita kuwa Iya Dije amsawa ta yi "kwankwatsi ma kuwa, ba mai bi na bashin rantsuwa, ai ga d’iyar nanniya(ai ga yarinyar nan), gani ya kori ji’’ kan Bintu ta ankara iya dije ta ja dan hijabin jikin ta, sai ga daga hijabin har kallabin na ta hannun Iya Dije, dan kunya kamar k’asa ta tsage ta rufe, musammam yanda rabin gashin na ta ya sauka har gadan baya, rabi ya tsaya iya wuya. Ta so yanke sauran dan ta daidai ta su amma sammakon da Iya Dije ta doka mata ya sa ba ta sami dama ba.
Cike da tausayi Aisar ya ke duban ta, ji yake kamar ya ruke ta ya kwashe mata gaba d’aya damuwar ya mayar zuwa kan shi. Gashi saboda shi an wulak’an ta ta, har aka mata cin zarafi ta hanyar yanke mata suma. Malam Hashim kuwa duban sa ga Aisar ya ke, in da zuciyar sa ke jaddada masa lalle watan rufe wannan makaran ta tasu ce ta tsaya...
"Bintu....’’ ya kira sunan ta cikin wani yanayi ya na mai sassauta kullin nakatayal (Neck-tie) din wuyar sa, dan ji yake kamar numfashi ba ya isar sa tsabagen 6acin rai. Hatta Iya Dije da Malam Hashim sai da su ka kai kallan su ga Aisar, ita kuwa Bintu kasa d’aga ido ta kalle shi ta yi. Malam Hashim ya gyara murya ganin yanayin 6acin ran da Aisar ya shiga ya ce "Ina Iya Dije, zai fi kyau ku d’an ba mu hili (fili) mu zanta da Malam Aisar’’ ta na mai mik’awa Bintu kallabi da hijabin ta, ta ce ‘’ye to ai sai mu fita rariya (sai mu fita waje), Bintu mu tahi ko?’’
Da saurin ta, ta karb’a ta d’aura kallabin kafin ta sanya hijabin na ta, Iya Dije a gaba ta na biye da ita, idanun Aisar kan Bintu har su ka fita. Shiru ne ya biyo baya na wani d’an mintina, kafin Malam Hashim ya d’aure ya ce ‘’na san abun da ke ran ka, amma ina mai tabbatar ma ka makamancin haka be ta6a faruwa a wanga École ba, wanga da ya faru ma tsautsayi ne Monsieur Aisar (Malam Aisar)’’
‘’ka na nufin baka san d’aliban ka su na aje makami a tare da su ba Monsieur (Malam)? Ai na zaci k’aida ne hukumar makaranta ta na bibiyan d’akin d’alibai lokaci lokaci dan binciken kayan su domin gudun irin haka? Me ke faruwa a wanga École ? (me ke faruwa a makarantar nan?) Shin me ku ke yi da har irin haka ka iya faru? Ya ilahi da ta kashe d’iyar mutane fa!!!’’ fad’in Aisar wanda tun da ya fara maganar kansa ke kallan silin. Malam Hashim kuwa zufa ne ya lullub’e shi kana ya ce ‘’lillahi warasulihi Monsieur (Malam) abin ga da ya faru tsautsayi nai, na kuma yi maka alkawarin duk matakin da za ka d’auka daidai ta (daidai ne), amma kar ya shafi wanga École(Makaranta) ’’
Sai a sannan Aisar ya mayar da kallan sa ga Malam Hashim, kana ya ce ‘’wannan laifi ne da ba zan iya d’auke ido akai ba, kasan k’asar mu ta Nijar k’asa ce da ke san jama’ar cikin ta, mai daraja dukkan abu mai numfashin da ke cikin ta, a matsayi na na d’an k’asa mai kishin k’asan ga, na ga irin haka na d’auke kai tabbas na ci amanar k’asa ta’’. Jin haka hankalin Malam Hashim ne ya tashi. Sai gashi ya taso ya zo gaban Aisar ya na mai ruk’o hannun sa ya ce "wanga École (makaranta) ta kunshi d’alibai daga kowani sassa da yankunan jamhuriyar Nijar, ruhe (rufe) ta ba k’aramin asara ba ce ga k’asar ga, kai ka sani k’asar mu na buk’atar makarantu ma su inganci irin Sovereign.......’’
"ka na nufin ita kad’ai ta École mai inganci a wanga k’asa ta mu? (ita kad’ai ce makaranta mai inganci a wanga k’asa ta mu?) Kada fa ka nemi ka zagi k’asa ta Monsieur Hashim!’’ Aisar ya katse shi cike da nuna 6acin rai. Cikin sauri Malam Hashim ya girgiza kai ya ce ‘’ba haka na ke nufi ba Monsieur Aisar, yo to na fad’i haka ban yi ma k’asa ta adalci ba, aradu ma kuwa, École (Makaranta) kuwa masu inganci mu ke da su a k’asar mu, amma ruheta kan iya jawo asarar d’aya daga cikin su, sabida Allahu da manzan sa wanga batu ka duba, duk hukunci da za yiwa wannan d’alibar ka mata ita ta jawa kan ta, yo mi zan ce zanin aro ya toye? amma kada laifin wani ya shafi wani’’
Bayan nazari na wani d’an lokaci Aisar ya ce "ko wani hukumci ka ce Monsieur Hashim?’’ Malam Hashim ya jinjina kai kafin ya ce ‘’ko wani hukunci muddin ba zai shafi wanga École ba, ba zai kuma shafi jarabawar gama sakandiri da d’iyar ta ke rubutawa ba....’’ wani irin kallo Aisar ya watsa masa jin maganar ta sa. Da sauri Malam Hashim ya ce ‘’ba dan d’yar ba Monsieur Aisar, dan cigban k’asar mu, ka ga idan ya shafi jarabawar hallau ya shafi cigaban k’asa ta fannin karatu, k’ak’a ka gani?’’
Tashi yayi ya na bai gyara nakatayal(neck-tie) d’in sa, sannan ya ce ‘’na fahimce ka, zan mata hukunci daidai da yanda ta aikatawa yar uwar ta’’ ya na gama magana ya fice in da ya bar Malam Hashim ya na mai zubewa bisa kujera yayinda ya ke goga zufan da shi kan sa be san ya tsefo masa haka da yawan gaske ba. A waje Aisar ya tadda Bintu da Iya Dije tsaye suna jiran tsammani, be iya kallan in da Bintu ta ke ba tsabagen haushin kan sa da ya ke ji akan abun da ya jawo mata. Kana ya dubi Iya Dije ya ce ‘’ko zan iya samin Ciseaux da sabuwar reza gun ki Iya Dije?’’ Cikin fad’uwar gaba Bintu ta d’ago kai ta na mai duban Malam Aisar, sai a sannan ta lura da yanayin shi da ya canza gaba d’aya, ya zama kamar ba shi ba tsabar 6acin rai. Murya a sanyaye ta ce ‘’dan mai sama Monsieur (Malam) ayi hakuri a bar maganar ga, yo to menene dan an aske gashin niya?(menene dan an aske gashi na), in dai dan niya ne arudu na gafarce ta’’
Kallan ta Aisar yayi ba tare da ya tanka mata ba ya sake maimaitawa Iya Dije tambayar, ganin haka Bintu ta sawa bakin ta sakata, in da Iya Dije ta amsa da ta na da su duka, ya ce to ta kawo masa filin taron d’alibai(assembly ground) yanzu ba tare da 6ata lokaci ba. Ya wuce ya bar Bintu da bin bayan sa da ido. Ita kuwa Iya Dije jiki na b’ari ta nufi 6angaran su dan d’auko sak’on Aisar.
A wajan taron d’alibai(assembly), d’alibai da malamai babu wanda be hallara wajan ba, filin ya cika mak’il. Bayan sun yi abin da su ka sabayi kullum, wato na daga al’adar makarantar ne aka bawa Aisar filin. Gannin shi gaban su d’alibai su ka yi tsit, ita kuwa Marry zawo ne kad’ai be zubo mata ba, musammam ganin Iya Dije tsaye kusa da Aisar hannun ta ruke da almakashi. Kamar saukar aradu haka ta ji sunan ta bakin Aisar, bayan ya kira Bintu. Nan da nan d’alibai su ka shiga bud’a mata hanya, da kyar ta ke iya d’aga k’afa ta na takawa saboda tsabagen nauyin da k’afar ta yi mata, har ta kai ga Aisar da tun fitowar ta ya ke mata kallan hadarin kaji.
Jin umarnin da Aisar ya bata na da ta juya ta tsugunna bisa gwiwowin ta gaban d’alibai ya sa ta matsawa kusa da Aisar ta na magana a hankali dan kar a ji abun da za ta ce tace ‘’dan Allah Monsieur (malam) ka taimaka kada su raina ni’’ wani irin tsawa ya daka mata ya na mai fad’in ‘’matsa min daga nan in ba haka ba ina kishe ki a nanniya!(in ba haka ba ina dukan ki a nan)’’ da saurin ta ta ja baya, ba ta san sanda ta zube k’asa ba jiki na 6ari. Ba tare da wani dogon bayani ba, haka ma d’alibai ba sa buk’ata dan kuwa gaban su aka yi komai dan haka Ciseaux din hannun Iya Dije ya kar6a ya na mai mik’awa Bintu ya ce ‘’kyarbi ki mata abin da ta mi ki jiya!’’
Hannun Bintu na rawa amma ta kasa d’aga su ta kar6a, cikin magiya ba tare da ta iya furta wani abu ba ta ke kallan Aisar ta na mai girgiza masa kai. Ga mamakin kowa sai jin Aisar cikin rarrashi ya ce da Bintu ‘’kar6ar wanga Ciseaux tare da yiwa wanga azzalumar aski shi ne hukunci mahi(mafi) sauki a gare ta, idan ba haka ba barin wanga École nan har abada ba tare da ta gama jarabawar ta ba ya kamata, za6in na ki ne’’ jin haka tuni waje ya kaure da hayaniya d’alibai, masu tausayin Mary da masu Allah shi k’ara wanda su suka fi yawa, in da yan aji shida kuwa idan ran su yayi dubu ya 6aci, dama duk ajin Mary aka fi tsoro, ita ce mai kankaro mu su girman yau ga ta tsugunne gaban kowa kuma a wulk’ance, tsabagen d’ibar albarka ace yar aji uku ce za ta mata aski! Gaskiya sun zube ba nauyi. Sai ga hawaye sha6e sha6e a fuskar Mary.
Tuni zufa ya fara kyetowa wa Bintu, musammam da ta kai kallan ta ga Malam Hashim ya gyad’a mata kai dan kuwa dai ba kukan sa ba uwar kishiya ta mutu. Wata malama ce wacce dama ta dad’e da tsanar Mary ta k’araso kusa da su ta na mai fad’in ‘’ Monsieur ba ka san halin wanga d’ya ba ne (wannan yarinyar ba ne), in aka biya ta za mu shekara nanniya ba tare da an samu abun da ake so ba, bari kawai ni na taimaka mata da zab’in’’ ta na magana ne in da ta ke aikawa Marry da sako murmushin yayinda ta sa hannu ta cizge kallabin Mary, Mary ta yi saurin d’aura hannayen ta bisa kan ta domin 6oye cinyayyen gashin ta, ai ganin gashin sai ga d’alibai na darawa.
Muryar Mary na rawa ta ‘’in ki na yiwa Allahu ki yi hakuri Madame , kwankwatsi (rantsuwa) na tuba, dan Allah kada ki yanke min suma ta’’ cike da mamaki ta ce ‘’yo ba ki so a yanke na ki shine ki yanke na wata, aradu kwal kwabo zan mi ki ma kuwa, Iya Dije ruk’e min hannun ta’’ ganin Iya Dije ta yo kan ta, ta saurin sauke hannayen ta k’asa, ta na ji ta na gani Malama ta sai ta almakashi bisa d’an gunjin ta, ta daidaici rabin gashin cikin hikimar raba kan gida biyu, ta fara cire na sama sama. Dake Malamar ma ta na fama da mugun ta, sai da ta karb’i sabuwar rezar hannun Iya Dije, ta kwashe rabin gashin Mary tas sannan hankalin ta ya kwanta.
Fuskar Mary ba k’aramin muni ta yi ba da kai rabi kwakwaido rabi kwal kabo, ko da yake dama yaya bare sarki ya aiko. Dan kunya da takaici ta kasa ko da motsi bare ta iya d’aga idanun ta ta kalli jama’a, d’alibai ba su fasa ihu da sowa ba, musammam da malamar ta ce ayiwa Marry ihu, su ka d’auka ‘’ihu dube ta kwakwaido da kwal kabo’’ Malam Hashim ne ya matso gaba, in da ya kira Shedigyal da Sikanti, ya had’a har maryam ya kwace kallabin muk’amin su, ya kuma jaddada hukunci mai tsanani ga duk d’alibar da aka k’ara kamawa da makami ba tare da kwakkwaran daliliba, ko da kuwa reza ne.
Farin ciki gun d’alibai be musaltuwa, dan kuwa kurace ta mutu, sun huta. Gimbiya kuwa tuni ta sha jinin jikin ta ganin yanda Aisar yayi ruwa yayi tsaki bisa ga lamarin, batun akwai wani abu tsakanin Bintu d’iyar bayi da Malam Aisar tun daga wajan ya fara shawagi tsakanin d’alibai. Har aka sallame su Mary ba ta iya tashi daga tsugunnan da ta yi ba, sai da yan aji shida su tada ita, nan ta saki kukan da dama ya tsaya k’ark’ashin mak’oshin ta, ba ta ta6a jin ta tsani kan ta ba kamar ranar ba. Ko da ya ke ba ita kad’ai ba duka yan aji shidan ma hakan ta ke. Sauran d’aliban kuwa yau ta ke sallah, dan kuwa abin da aka yiwa Bintu gaba ta kai dan sun sami sakewa da wa tayawa, a ranar Bintu ta yi farin jini sai san barka ake yi mata, hatta Gimbiya a ranar sai da ta sarara mata.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
No comments:
Post a Comment