Tuesday, 19 September 2017

Bintu ɗiyar bayi ce 3

®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

©Khadija Sidi.....✍🏼

0⃣3⃣

Tausayin ta ne ya lullu6e shi,dan daga ganin yanayin ta ka san fararriya ce.
‘’zauna ina ki jira ina zuwa’’

Ya fad'a a sanyaye,kafin ya juya ya fita ba tare da ya jira ta amsa masa ba,dama ko ya jira in ma ba amsawa za ta yi ba. Cike da da kunya da takaicin yanayin da ya gan ta, ta koma ta zauna, gaba d’aya ji ta yi ta tsani kan ta,kan ta ta kifa bisa teburi. Jim ka d’an ta ji muryar d’aya daga cikin masu kula da d’akin kwanan dalibai,wacce su ke kira iya Dije,ta na fad’in
‘’wacece ne? d’ago kan ki na gan ki’’
Bintu ta d’ago kan ta a hankali ta dube ta. Ganin fuskar Bintu ga idanun nan na ta ya yi jajur dan kuka Iya Dije ta ce
‘’aw Bintu da ke ce?yo menene na kukan har haka? Ai girma ne ya zo,maza ungo wannan zanin ki d'aura mu je ki gyara kan ki’’
Ta mik’a mata zani,hannun Bintu na rawa ta kar6a da saurin ta. Ta tashi a hankali ta d’aura zanin ta na mai bin kujerer da ta 6’ata da kallo.
‘’kar ki wani damu da wannan, Shatu na nan tafe za ta gyara,ke dai mu je ki fara gyarawa tukun’’
Fad’in Iya Mairo yayinda ta d’auki jakar Bintu ta wuce gaba,Bintu na biye da ita. D’akin kwanan d’alibai su ka wuce, d’akin su Bintu ta zauna ta yi jiran ta bayan ta koya mata yanda za ta yi ta gyara kan ta. Sai da ta yi wanka ta shirya sannan ta wanke kayana da zanin da Iya Dije ta bata.
Bayan ta gama ne ta je ta sami Iye Dije zaune ta na jiran ta. Kamar wacce ta yi laifi ta d’an ra6e daga gefe,kan ta sunkuye ta ce
‘’Iya Dije na gode da kulawar ki,wallahi ba da sani na ba ne,ban ta6’a ganin irin haka ba’’
Murmushi Iya dije ta yi jin maganar Bintu,kana ta dafa kafad’ar ta tana mai fa’d’in
‘’Yaro dai Yaro ne,dama kowa akwai ranar da ya ke farawa,kuma kowace cikakkiyar budurwa ta na yi,auta ta ma ba ta dad’e da farawa ba’’
Da sauri Bintu ta d’ago kan ta ta ce "Allah? ita ma ta yi kuka?’’
‘’ah ah’’
Iya Dije ta amsa mata,sannan ta k'ara da
‘’da ke ta tashi cikin mata kuma ta na zuwa islamiya toh ta san komai,kawai dai ta shiga damuwa na rashin sabo,da fatan ki na dai zuwa islamiya a masarautar ku’’
Bintu na mai girgiza kai ta ce
‘’ah ah makarantar allo na ke zuwa,shi ma kuma sai idan babu aiki sosai a fada,da aka sani wannan makarantar ma sai na dena zuwa gaba d’aya’’
Iya Dije ta ce
"assha ai makarantar islama na da muhimmanci ga rayuwar d’iya mace, kin ga da kina zuwa da yanzu kin san  duka hukunce hukunce da ya hau kan ki, lalle idan an yi huta ki ce da gyatumar ki ta sanya ki cikin islamiya, ba a tsufa da neman ilimi bare ke da kuruciyar ki kin ji ko?’’

Bintu ta gyad’a kai. Kana Iya Dije ta kara da
‘’yanzu hukunci babba ya hau kan ki tunda kin balaga, yanda za  a rubuta wa mahaifiyar ki ko ni kai na hukunci haka ke ma za a rubuta mi ki dan kuwa yanzu mu da ke duk d’aya ne har ga Allah, kin tashi daga yarinya. Dan haka ki kula ki kyau ta ta rayuwar ki ta duniya da lahira, ki ruk’e mutunci ki da na iyayen ki. Ba ruwan ki da maza muddin ba da kwakkwaran dalili ba,kin dai san mai wasa da maza karya ce ko?’’
Kai sunkuye Bintu ta jinjina kai alamar ‘’eh’’ Iya Dije ba ta gushe ba ta k’ara da
‘’yauwa, wannan sabon Malamin da ya zo yayi kira akan ki, menene dangantakar ku?’’
Nan fa Bintu ta fara kame kame, ta ce
"iye? na’am? Wai wannan d’in nan? wallahi ni ma ban san shi ba Iya Dije,yau ya fara koyar da mu fa"
Cikin nazari Iya Dije ta kura mata ido kafin daga bisani ta nisa ta ce
‘’kar ki saki jiki da kowane d’a namiji muddin ba muharramin ki ba ne, wato wadda babu auratayya tsakanin ku, kar ki sakarwa kowa fuska ko hannu kar ki yarda wani ya ta6’a ruk'e mi ki idan ba haka ba mutuwa za ki yi,kin ji ko?’’
A tsorace dan ta ji batun mutuwa ta amsa da
‘’Toh, wallahi dama ni ba ruwa na da maza, ko a masarautar mu ma ba na sakar mu su fuska, yaya Ubaliya ma sheda ta ne’’
Kai Iya Dije ta jinjina alamar gamsuwa. Nan ta cigaba da bawa Bintu shawarwari. Ko da ta zo tafiya har ta kai ga k’ofa ta ce
‘’Bintu ya batun turare ina fatan dai ki na da shi, dan yanayin da ki ke ciki sai fa da turaren’’
Bintu na d’an soshe soshe ta ce "Iye?dama dai Inna ta ta bani garin alimun ta ce ina had’awa da leman tsamin sai na ke gogawa a hammata ta’’
‘’eh toh wannan ma ba laifi,amma ki na bukatar turare,dama wannan Malamin ya ce na fad’a masa idan ki na da bukatar wani abu,na fad’a masa. Kuma kar ki manta ki na canza wannan audugar da na baki a kankari, ban da k’azanta dan Allah idan ba haka ba kuwa za ki ji ki kina wari na gaske’’

Cike da jin kunya su ka yi sallama, Bintu ta mata godiya sosai. Bayan fitar ta ne ta ji yunwar da take ji ya dawo ma ta, saboda haka sai ta bu6e akwatin k’arfen ta,ta fito da ajiyar garin kwakin ta da kuli ta sha ta k’oshi. Ta na gamawa da saurin ta ta gyara wajan dan kar Gimbiya Binta ta gani ta zubar mata da ragowar. Ko da ta ga ta sami nutsuwa,ta shifid’a tabarmar ta, ta yi kwanciyar ta kafin lokaci ya cika ta koma aji. Gaba d’aya kunyar Malamin nan ne ke damun ta musammam yanzu da Iya Dije ta fed’e mata daga bindi har wutsiya na game da sabon rayuwar da ta shiga,ga shi shi dai kullum ba ya sa’ar ganin ta cikin hayyacin ta. Da wannan tunanin bacci mai dad’in gaske yayi gaba da ita.

Saukar marin da ta ji ya sa ta yi firgit ta tashi zaune hannun ta bisa kuncin ta ta na mai murzawa. Ba ta bari ta gama wastsakewa ba ta rufe ta da zagi, fad’i ta ke
‘’dan uban ki wannan bawan har ki zo ki kwanta ki na barcin asara kin manta bauta ya kawo ki makarantar nan? k’azama wawuya!’’
Da sauri Bintu ta d’urk’usa jika na b'ari ta ce
‘’Allah ya huci zuciyar gimbiya, tuba na ke, ban san sa’in da baccin ya sace ni ba, ki min aikin gafara’’
A wulak'ance Gimbiya Binta ke duban Bintu,kafin ta furta
‘’ga wanki can na su diras d’ina,bayan kin gama ki min guga. Kuma ki sani yau bazan iya kwana d’aki d’aya da ke ba cikin wannan k’azantar da ki ke. ki d’au k’azamar tabarmar ki ki aje daga can lungun,kuma ki san abun da za ki ce da su Iya Dije su ka gan ki a nan kwance dan idan ki ka kuskura ki ka kira sunana wallahi sai na lahira ya fi ki jin dad’i’’
Cike da ladabi Bintu ta duk’a ta na mai fad’in
‘’Godiya na ke ran ki shi dad’e’’
Gimbiya Binta ta k’ara da
"wallahi na tsane ki,duka cikin bayain fada babu wanda na tsana kamar ke,wai amma a rasa wacce za a had’u ni da ita sai ke!’’
Ta shure Bintu ta wuce ciki,kan gado ta nufa ta zauna d’ai-d’ai abun ta. Kai sun kuye Bintu ta tashi, ta nad’e tabarmar ta sannan ta kwashe wankin Gimbiya. Gaba d’aya a takure ta ke yin komai musammam yanda tafiya ma mai kyau da kyar ta ke gudun kar ta sake b’aci.

Sai da la’asar sakaliya ta gama wankin,bayan ta yi shanya ta na shirin fara guga su Zahira su ka shigo d’akin. Nan fa su ka zauna in ban da maganar Aisar babu abun da su ke.
‘’Aisar Gaddafi Nur ai ba k’aramin had’uwa yayi ba’’ fad’in Gimbiya,ta k’ara da
‘’ni abun da ke ban mamaki ganin shi a matsayin malami’’

"ko ni ma na yi mamaki gaskiya’’
Zahira ta taya ta.Ajiyar zuciya Gimbiya Binta ta saki kana ta ce

"ni fa k’awaye na wallahi na kamu, gaba d’aya ya shiga rai na’’

Maryam da Zahira su ka sa shewa, Maryam ce ta amsa mata da

"ai dama ni tuni na d’ago jirgin ki,kar ki damu ai jinin sarauta ba sa nema su rasa’’
‘’ko ba dan jinina ba ai na isa a soni,ba ku lura da yanda ya ke kallo na ba ne?’’
Fad’in Gimbiya cike da tak’ama, wanda hakan ya sanya k’awayenta yi mata kirari su na dad’a wasa ma ta kai. Bintu da ke jiyo su daga can gefe ta murmusa cikin ranta fad’i ta ke "Malam Aisar ya cika jarumi tinda har ya shiga ran Gimbiya’’ ajiyar zuciya ta saki ta na mai fatan Allah ya tabbatar da alkhairi.

*******
Kamar yanda Gimbiya Binta ta ce,ranar a d’an wani lungu cikin d’akin Bintu ta samu ta ra6’e. Da kyar ta iya samun bacci saboda sauro. Da asubar fari Gimbiya Binta ta tada ita,kuma ba ta bari ta yi amfani da band’akin su ba,sai k’asa ta sauka.
Bayan sun shiga aji sun fito hutun cin abunci da azahar, Gimbiya ta hana ta zama cikin d’akin cin abunci,wai ta na sa ta tashin zuciya. Tsaye ta ke bakin d’akin cin abunci, sai had’iyar yawu ta ke dan yunwar yau tafi ta kullum. Rana ko ta take sosai dan kuwa su na sa ran samuwar ruwan sama kwana kusa. Gashi in da ta ke tsaye sam babu inuwa, bini bini sai ta sa tafin hannun ta ta goge zufar da ke faman ketowa bisa kuncin goshin ta. Da ta ga abun ba na k’arau ba ne,ta sanya hannun ta cikin aljihu ta d’auko k'ulin ta da ta d’an k’unso a yar leda. Wata bishiya ta hango,kai tsaye ta nufe shi ta na k’ok’arin kwance ledar k'ulin. Ta gaban d’akin cin abuncin malamai wuce.

Ta taga ya hango ta,lokacin guda ya bar cin abuncin da ya ke  hannun sa ruk'e da cokali ya bi ta da kallo. Tin da ya ke be tab’a ganin wacce ta iya tafiya tafiya irin na Bintu ba. Tafiya ce a nutse ko wacce k’afa in aka aje sai an tsagaita kafin ta biyu ta biyo ta. Gashi dai babu alamar tak’ama a tattare da tafiyar amma sai ta zama tak’amar ce ma gaba d’aya. Kuma tsayin ta ya sa haka. Be dene kallan ta ba har ta isa ga bishiyar ta zauna. Ganin ta bud’e wata yar leda ta na fitar da wani abu ta na afawa a bakin ta sannan ya tuna fa yanzu lokacin cin abuncin d’alibai ne,me ta ke yi a waje,ya aje cikoli ya tashi kai tsaye ya fito ya nufo in ta ke zaune.

Bintu ta ba ta hango shi ba,ba ta kuma ga tahowar shi ba,ta ciko hannun ta da kuli kenan ta afa a bakin ta , sai kawai ganin shi ta yi tsaye kan ta,bakin ta cike da k'uli ta d'ago kai su ka had’a ido nan da nan gaban ta ya fad’i,cikin zuciyar ta kuwa ihu ta kurma
‘’wayyo ni Bintu aradu wagga Malami ya takura ni!’’

🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

No comments:

Post a Comment